< Markus 9 >

1 Ya kuma ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, waɗansu da suke tsattsaye a nan ba za su mutu ba, sai sun ga mulkin Allah ya bayyana da iko.”
Et il leur dit: En vérité, je vous dis, que de ceux qui sont ici présents, il y en a quelques-uns qui ne goûteront point la mort jusqu’à ce qu’ils aient vu le royaume de Dieu venu avec puissance.
2 Bayan kwana shida, sai Yesu ya ɗauki Bitrus, Yaƙub da Yohanna tare da shi, ya kai su kan wani dutse mai tsawo, suka kasance su kaɗai a wurin. A can aka sāke kamanninsa a gabansu.
Et après six jours, Jésus prend avec lui Pierre et Jacques et Jean, et les mène seuls à l’écart, sur une haute montagne. Et il fut transfiguré devant eux;
3 Tufafinsa suka zama fari suna ƙyalli, fiye da yadda wani a duniya zai iya yi su.
et ses vêtements devinrent brillants et d’une extrême blancheur, comme de la neige, tels qu’il n’y a point de foulon sur la terre qui puisse ainsi blanchir.
4 Iliya da Musa suka bayyana a gabansu, suna magana da Yesu.
Et Élie leur apparut avec Moïse, et ils parlaient avec Jésus.
5 Bitrus ya ce wa Yesu, “Rabbi, ya yi kyau da muke nan. Bari mu kafa bukkoki guda uku, ɗaya dominka, ɗaya domin Musa, ɗaya kuma domin Iliya.”
Et Pierre, répondant, dit à Jésus: Rabbi, il est bon que nous soyons ici; et faisons trois tentes: une pour toi, et une pour Moïse, et une pour Élie.
6 (Bai san abin da zai faɗa ba ne, gama sun tsorata ƙwarai.)
Car il ne savait que dire; car ils étaient épouvantés.
7 Sai wani girgije ya bayyana, ya rufe su, wata murya kuma ta fito daga girgijen, ta ce, “Wannan Ɗana ne, wanda nake ƙauna, ku saurare shi!”
Et il vint une nuée qui les couvrit, et il vint de la nuée une voix: Celui-ci est mon Fils bien-aimé, écoutez-le.
8 Farat ɗaya, da suka waiwaya, ba su ƙara ganin kowa tare da su ba, sai dai Yesu.
Et aussitôt, ayant regardé de tous côtés, ils ne virent plus personne, sinon Jésus seul avec eux.
9 Da suna saukowa daga dutsen, Yesu ya umarce su kada su gaya wa kowa abin da suka gani, sai bayan Ɗan Mutum ya tashi daga matattu.
Et comme ils descendaient de la montagne, il leur enjoignit de ne raconter à personne ce qu’ils avaient vu, sinon lorsque le fils de l’homme serait ressuscité d’entre les morts.
10 Suka riƙe wannan zance a ɓoye tsakaninsu, suna tattaunawa ko mece ce ma’anar “tashi daga matattu.”
Et ils gardèrent cette parole, s’entre-demandant ce que c’était que ressusciter d’entre les morts.
11 Suka tambaye shi, suka ce, “Don me malaman dokoki suke cewa, sai Iliya ya fara zuwa?”
Et ils l’interrogèrent, disant: Pourquoi les scribes disent-ils qu’il faut qu’Élie vienne premièrement?
12 Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya ne, Iliya zai zo da fari, yă kuma mayar da dukan abubuwa. Don me kuma aka rubuta cewa, dole Ɗan Mutum yă sha wahala sosai, kuma a ƙi shi?
Et lui, répondant, leur dit: En effet, Élie vient premièrement et rétablit toutes choses; – et comment il est écrit du fils de l’homme, qu’il souffrira beaucoup et qu’il sera chargé de mépris.
13 Amma ina faɗa muku, Iliya ya riga ya zo, kuma suka yi duk abin da suka ga dama da shi, kamar yadda aka rubuta game da shi.”
Mais je vous dis qu’aussi Élie est venu, et ils lui ont fait tout ce qu’ils ont voulu, comme il est écrit de lui.
14 Da suka dawo wurin sauran almajiran, sai suka ga babban taro kewaye da su, malaman dokoki suna gardama da su.
Et venant vers les disciples, il vit autour d’eux une grande foule, et des scribes qui disputaient avec eux.
15 Nan take da dukan mutanen suka ga Yesu, sai suka cika da mamaki, suka ruga da gudu don su gai da shi.
Et aussitôt toute la foule, le voyant, fut saisie d’étonnement; et ils accoururent et le saluèrent.
16 Ya tambaye su ya ce, “Gardamar me kuke yi da su?”
Et il les interrogea, [disant]: De quoi disputez-vous avec eux?
17 Wani mutum a cikin taron ya amsa ya ce, “Malam, na kawo maka ɗana mai wani ruhun da yake hana shi magana.
Et quelqu’un de la foule lui répondit: Maître, je t’ai amené mon fils qui a un esprit muet,
18 Duk lokacin da mugun ruhun ya kama shi, yakan jefa shi a ƙasa. Bakinsa yakan yi kumfa, yă cije haƙorarsa, yakan sa jikinsa ya sandare, yă zama da ƙarfi. Na roƙi almajiranka su fitar da ruhun, amma ba su iya ba.”
et, partout où il le saisit, il l’agite violemment; et il écume, et grince des dents, et il devient sec; et j’ai dit à tes disciples de le chasser, et ils n’ont pas pu.
19 Yesu ya ce, “Ya ku zamani marar bangaskiya, har yaushe zan kasance tare da ku? Har yaushe zan yi haƙuri da ku? Kawo mini yaron.”
Et lui, leur répondant, dit: Ô génération incrédule, jusques à quand serai-je avec vous? jusques à quand vous supporterai-je? Amenez-le-moi.
20 Sai suka kawo shi. Da ruhun ya ga Yesu, nan da nan sai ya buge yaron da farfaɗiya. Ya fāɗi a ƙasa, yana birgima, bakinsa yana kumfa.
Et ils le lui amenèrent; et quand il l’eut vu, aussitôt l’esprit le déchira; et [l’enfant], tombant à terre, se roulait en écumant.
21 Yesu ya tambayi mahaifin yaron ya ce, “Tun yaushe yake haka?” Ya ce, “Tun yana ƙarami.
Et Jésus demanda au père de l’enfant: Combien y a-t-il de temps que ceci lui est arrivé? Et il dit: Dès son enfance;
22 Ya sha jefa shi cikin wuta, ko ruwa don yă kashe shi. Amma in za ka iya yin wani abu, ka ji tausayinmu ka taimake mu.”
et souvent il l’a jeté dans le feu et dans les eaux pour le faire périr; mais si tu peux quelque chose, assiste-nous, étant ému de compassion envers nous.
23 Yesu ya ce, “‘In za ka iya’? Ai, kome mai yiwuwa ne ga wanda ya gaskata.”
Et Jésus lui dit: Le “Si tu peux”, c’est: Crois! toutes choses sont possibles à celui qui croit.
24 Nan da nan mahaifin yaron ya faɗa da ƙarfi ya ce, “Na gaskata, ka taimake ni in sha kan rashin bangaskiyata!”
Et aussitôt le père de l’enfant, s’écriant, dit avec larmes: Je crois, viens en aide à mon incrédulité.
25 Da Yesu ya ga taron suna zuwa can a guje, sai ya tsawata wa mugun ruhun ya ce, “Kai ruhun kurma, da na bebe, na umarce ka, ka fita daga cikinsa, kada kuma ka ƙara shigarsa.”
Et Jésus, voyant que la foule accourait ensemble, tança l’esprit immonde, lui disant: Esprit muet et sourd, je te commande, moi, sors de lui et n’y rentre plus.
26 Sai ruhun ya yi ihu, ya buge shi da ƙarfi da farfaɗiya, ya fita. Yaron ya kwanta kamar matacce, har mutane da yawa suka ce, “Ai, ya mutu.”
Et ayant crié et l’ayant violemment déchiré, il sortit; et [l’enfant] devint comme mort, de sorte que la plupart disaient: Il est mort.
27 Amma Yesu ya kama shi a hannu ya ɗaga, ya kuwa tashi tsaye.
Et Jésus, l’ayant pris par la main, le redressa; et il se leva.
28 Da Yesu ya shiga gida, almajiransa suka tambaye shi a ɓoye, suka ce, “Me ya sa ba mu iya fitar da shi ba?”
Et lorsqu’il fut entré dans la maison, ses disciples lui demandèrent en particulier: Pourquoi n’avons-nous pu le chasser?
29 Ya amsa ya ce, “Sai da addu’akaɗai irin wannan yakan fita.”
Et il leur dit: Cette sorte ne peut sortir en aucune façon, si ce n’est par la prière et par le jeûne.
30 Suka bar wurin suka bi ta Galili. Yesu bai so wani yă san inda suke ba,
Et étant sortis de là, ils traversèrent la Galilée; et il ne voulut pas que personne le sache.
31 gama yana koya wa almajiransa. Ya ce musu, “Za a ci amanar Ɗan Mutum, a ba da shi ga hannun mutane. Za su kashe shi, bayan kwana uku kuma zai tashi.”
Car il enseignait ses disciples et leur disait: Le fils de l’homme est livré entre les mains des hommes, et ils le feront mourir; et ayant été mis à mort, il ressuscitera le troisième jour.
32 Amma ba su fahimci abin da yake nufi ba, suka kuma ji tsoro su tambaye shi game da wannan.
Mais ils ne comprenaient pas ce discours, et ils craignaient de l’interroger.
33 Suka iso Kafarnahum. Da yana cikin gida, sai ya tambaye su ya ce, “Gardamar me kuke yi a hanya?”
Et il vint à Capernaüm; et quand il fut dans la maison, il leur demanda: Sur quoi raisonniez-vous en chemin?
34 Amma suka yi shiru, don a hanya suna gardama ne, a kan ko wane ne a cikinsu ya fi girma?
Et ils gardaient le silence, car ils avaient disputé entre eux, en chemin, qui serait le plus grand.
35 Da Yesu ya zauna, sai ya kira Sha Biyun ya ce, “In wani yana so yă zama na fari, dole yă zama na ƙarshe duka, da kuma bawan kowa.”
Et lorsqu’il se fut assis, il appela les douze et leur dit: Si quelqu’un veut être le premier, il sera le dernier de tous et le serviteur de tous.
36 Ya ɗauki wani ƙaramin yaro ya sa yă tsaya a tsakiyarsu. Ya ɗauke shi a hannunsa, ya ce musu,
Et ayant pris un petit enfant, il le plaça au milieu d’eux; et l’ayant pris entre ses bras, il leur dit:
37 “Duk wanda ya karɓi ɗaya daga cikin waɗannan ƙananan yara a cikin sunana, ni ya karɓa. Duk wanda kuma ya karɓe ni, ba ni ya karɓa ba, amma wanda ya aiko ni ne ya karɓa.”
Quiconque recevra l’un de tels petits enfants en mon nom, me reçoit; et quiconque me recevra, ce n’est pas moi qu’il reçoit, mais c’est celui qui m’a envoyé.
38 Yohanna ya ce, “Malam mun ga wani mutum yana fitar da aljanu a cikin sunanka, sai muka ce yă daina, domin shi ba ɗaya daga cikinmu ba ne.”
Et Jean lui répondit, disant: Maître, nous avons vu quelqu’un qui chassait des démons en ton nom, qui ne nous suit pas; et nous le lui avons défendu, parce qu’il ne nous suit pas.
39 Yesu ya ce, “Kada ku hana shi. Ba wanda yake yin ayyukan banmamaki a cikin sunana, nan take yă faɗi wani abu mummuna game da ni.
Et Jésus leur dit: Ne le lui défendez pas; car il n’y a personne qui fasse un miracle en mon nom, et qui puisse aussitôt mal parler de moi,
40 Gama duk wanda ba ya gāba da mu, namu ne.
car celui qui n’est pas contre nous est pour nous.
41 Gaskiya nake gaya muku, duk wanda ya ba ku ruwan sha a sunana, saboda ku na Kiristi ne, lalle, ba zai rasa ladarsa ba.
Car quiconque vous donnera à boire une coupe d’eau en [mon] nom, parce que vous êtes de Christ, en vérité, je vous dis qu’il ne perdra point sa récompense.
42 “Idan kuma wani yă sa ɗaya daga cikin waɗannan’yan yara masu gaskatawa da ni yă yi laifi, zai fiye masa a rataya wani babban dutsen niƙa a wuyarsa, a jefa shi cikin teku.
Et quiconque sera une occasion de chute pour un des petits qui croient en moi, mieux vaudrait pour lui qu’on lui mette au cou une pierre de meule, et qu’il soit jeté dans la mer.
43 In hannunka yana sa ka yin zunubi, yanke shi. Ai, gwamma ka shiga rai da hannu ɗaya, da ka shiga jahannama ta wuta, inda ba a iya kashe wutar ba, da hannuwanka biyu. (Geenna g1067)
Et si ta main est pour toi une occasion de chute, coupe-la: il vaut mieux pour toi d’entrer estropié dans la vie, que d’avoir les deux mains, et d’aller dans la géhenne, dans le feu inextinguible, (Geenna g1067)
là où leur ver ne meurt pas et où le feu ne s’éteint pas.
45 In kuma ƙafarka tana sa ka yin zunubi, yanke ta. Ai, gwamma ka shiga rai da ƙafa ɗaya, da a jefa ka cikin jahannama ta wuta, da ƙafafunka biyu. (Geenna g1067)
Et si ton pied est pour toi une occasion de chute, coupe-le: il vaut mieux pour toi d’entrer boiteux dans la vie, que d’avoir les deux pieds, et d’être jeté dans la géhenne, dans le feu inextinguible, (Geenna g1067)
là où leur ver ne meurt pas et où le feu ne s’éteint pas.
47 In kuma idonka yana sa ka zunubi, ƙwaƙule shi. Ai, gwamma ka shiga mulkin Allah da ido ɗaya, da a jefa ka cikin jahannama ta wuta, da idanu biyu, (Geenna g1067)
Et si ton œil est pour toi une occasion de chute, arrache-le: il vaut mieux pour toi d’entrer dans le royaume de Dieu, n’ayant qu’un œil, que d’avoir deux yeux et d’être jeté dans la géhenne de feu, (Geenna g1067)
48 inda “‘tsutsotsinsu ba sa mutuwa, wutar kuma ba a iya kashewa.’
là où leur ver ne meurt pas et où le feu ne s’éteint pas.
49 Za a tsarkake kowa da wuta.
Car chacun sera salé de feu; et tout sacrifice sera salé de sel.
50 “Gishiri yana da daɗi, amma in ya rabu da ɗanɗanonsa, ta yaya za a sāke mai da ɗanɗanonsa? Ku kasance da gishiri a cikinku, ku kuma yi zauna lafiya da juna.”
Le sel est bon; mais si le sel devient insipide, avec quoi lui donnerez-vous de la saveur? Ayez du sel en vous-mêmes, et soyez en paix entre vous.

< Markus 9 >