< Markus 9 >
1 Ya kuma ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, waɗansu da suke tsattsaye a nan ba za su mutu ba, sai sun ga mulkin Allah ya bayyana da iko.”
Il ajouta: « Je vous le dis, en vérité, parmi ceux qui sont ici, quelques-uns ne goûteront pas la mort, qu’ils n’aient vu le royaume de Dieu venir avec puissance. »
2 Bayan kwana shida, sai Yesu ya ɗauki Bitrus, Yaƙub da Yohanna tare da shi, ya kai su kan wani dutse mai tsawo, suka kasance su kaɗai a wurin. A can aka sāke kamanninsa a gabansu.
Six jours après, Jésus prit avec lui Pierre, Jacques et Jean, et les conduisit seuls, à l’écart, sur une haute montagne, et il fut transfiguré devant eux.
3 Tufafinsa suka zama fari suna ƙyalli, fiye da yadda wani a duniya zai iya yi su.
Ses vêtements devinrent étincelants, d’une blancheur aussi éclatante que la neige, et tels qu’aucun foulon sur la terre ne saurait blanchir ainsi.
4 Iliya da Musa suka bayyana a gabansu, suna magana da Yesu.
Puis Élie et Moïse leur apparurent, conversant avec Jésus.
5 Bitrus ya ce wa Yesu, “Rabbi, ya yi kyau da muke nan. Bari mu kafa bukkoki guda uku, ɗaya dominka, ɗaya domin Musa, ɗaya kuma domin Iliya.”
Pierre, prenant la parole, dit à Jésus: « Maître, il nous est bon d’être ici; dressons trois tentes, une pour toi, une pour Moïse, et une pour Élie. »
6 (Bai san abin da zai faɗa ba ne, gama sun tsorata ƙwarai.)
Il ne savait ce qu’il disait, l’effroi les ayant saisis.
7 Sai wani girgije ya bayyana, ya rufe su, wata murya kuma ta fito daga girgijen, ta ce, “Wannan Ɗana ne, wanda nake ƙauna, ku saurare shi!”
Et une nuée les couvrit de son ombre, et de la nuée sortit une voix: « Celui-ci est mon Fils bien-aimé; écoutez-le. »
8 Farat ɗaya, da suka waiwaya, ba su ƙara ganin kowa tare da su ba, sai dai Yesu.
Aussitôt, regardant tout autour, ils ne virent plus personne, si ce n’est Jésus, seul avec eux.
9 Da suna saukowa daga dutsen, Yesu ya umarce su kada su gaya wa kowa abin da suka gani, sai bayan Ɗan Mutum ya tashi daga matattu.
Comme ils descendaient de la montagne, il leur défendit de raconter à personne ce qu’ils avaient vu, jusqu’à ce que le Fils de l’homme fût ressuscité des morts.
10 Suka riƙe wannan zance a ɓoye tsakaninsu, suna tattaunawa ko mece ce ma’anar “tashi daga matattu.”
Et ils gardèrent pour eux la chose, tout en se demandant entre eux ce que signifiait ce mot: « être ressuscité des morts! »
11 Suka tambaye shi, suka ce, “Don me malaman dokoki suke cewa, sai Iliya ya fara zuwa?”
Ils l’interrogèrent et lui dirent: « Pourquoi donc les scribes disent-ils qu’il faut qu’Élie vienne auparavant? »
12 Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya ne, Iliya zai zo da fari, yă kuma mayar da dukan abubuwa. Don me kuma aka rubuta cewa, dole Ɗan Mutum yă sha wahala sosai, kuma a ƙi shi?
Il leur répondit: « Élie doit venir auparavant, et rétablir toutes choses; et comment est-il écrit du Fils de l’homme qu’il doit souffrir beaucoup et être méprisé?
13 Amma ina faɗa muku, Iliya ya riga ya zo, kuma suka yi duk abin da suka ga dama da shi, kamar yadda aka rubuta game da shi.”
Mais, je vous le dis, Élie est déjà venu, et ils l’ont traité comme ils ont voulu, selon qu’il est écrit de lui. »
14 Da suka dawo wurin sauran almajiran, sai suka ga babban taro kewaye da su, malaman dokoki suna gardama da su.
Étant retourné vers ses disciples, il vit une grande foule autour d’eux, et des scribes qui discutaient avec eux.
15 Nan take da dukan mutanen suka ga Yesu, sai suka cika da mamaki, suka ruga da gudu don su gai da shi.
Toute la foule fut surprise de voir Jésus, et elle accourut aussitôt pour le saluer.
16 Ya tambaye su ya ce, “Gardamar me kuke yi da su?”
Il leur demanda: « Sur quoi discutez-vous avec eux? »
17 Wani mutum a cikin taron ya amsa ya ce, “Malam, na kawo maka ɗana mai wani ruhun da yake hana shi magana.
Un homme de la foule lui répondit: « Maître, je t’ai amené mon fils, qui est possédé d’un esprit muet.
18 Duk lokacin da mugun ruhun ya kama shi, yakan jefa shi a ƙasa. Bakinsa yakan yi kumfa, yă cije haƙorarsa, yakan sa jikinsa ya sandare, yă zama da ƙarfi. Na roƙi almajiranka su fitar da ruhun, amma ba su iya ba.”
Partout où l’esprit s’empare de lui, il le jette contre terre, et l’enfant écume, et grince des dents et il se dessèche; j’ai prié tes disciples de le chasser, et ils n’ont pas pu.
19 Yesu ya ce, “Ya ku zamani marar bangaskiya, har yaushe zan kasance tare da ku? Har yaushe zan yi haƙuri da ku? Kawo mini yaron.”
O race incrédule, leur dit Jésus, jusques à quand serai-je avec vous? Jusques à quand vous supporterai-je? Amenez-le-moi. »
20 Sai suka kawo shi. Da ruhun ya ga Yesu, nan da nan sai ya buge yaron da farfaɗiya. Ya fāɗi a ƙasa, yana birgima, bakinsa yana kumfa.
On le lui amena. À sa vue, l’esprit agita soudain l’enfant avec violence; il tomba par terre et se roulait en écumant.
21 Yesu ya tambayi mahaifin yaron ya ce, “Tun yaushe yake haka?” Ya ce, “Tun yana ƙarami.
Jésus demanda au père de l’enfant: « Combien y a-t-il de temps que cela lui arrive? — Depuis son enfance, répondit-il.
22 Ya sha jefa shi cikin wuta, ko ruwa don yă kashe shi. Amma in za ka iya yin wani abu, ka ji tausayinmu ka taimake mu.”
Souvent l’esprit l’a jeté dans le feu et dans l’eau pour le faire périr; si tu peux quelque chose, aie pitié de nous et viens-nous en aide. »
23 Yesu ya ce, “‘In za ka iya’? Ai, kome mai yiwuwa ne ga wanda ya gaskata.”
Jésus lui dit: « Si tu peux (croire), tout est possible à celui qui croit. »
24 Nan da nan mahaifin yaron ya faɗa da ƙarfi ya ce, “Na gaskata, ka taimake ni in sha kan rashin bangaskiyata!”
Aussitôt le père de l’enfant s’écria, disant avec larmes: « Je crois (Seigneur); viens au secours de mon incrédulité »
25 Da Yesu ya ga taron suna zuwa can a guje, sai ya tsawata wa mugun ruhun ya ce, “Kai ruhun kurma, da na bebe, na umarce ka, ka fita daga cikinsa, kada kuma ka ƙara shigarsa.”
Jésus, voyant le peuple accourir en foule, menaça l’esprit impur, en disant: « Esprit sourd et muet, je te le commande, sors de cet enfant, et ne rentre plus en lui. »
26 Sai ruhun ya yi ihu, ya buge shi da ƙarfi da farfaɗiya, ya fita. Yaron ya kwanta kamar matacce, har mutane da yawa suka ce, “Ai, ya mutu.”
Alors, ayant poussé un grand cri, et l’ayant agité avec violence, il sortit, et l’enfant devint comme un cadavre, au point que plusieurs disaient: « Il est mort. »
27 Amma Yesu ya kama shi a hannu ya ɗaga, ya kuwa tashi tsaye.
Mais Jésus, l’ayant pris par la main, le fit lever, et il se tint debout.
28 Da Yesu ya shiga gida, almajiransa suka tambaye shi a ɓoye, suka ce, “Me ya sa ba mu iya fitar da shi ba?”
Lorsqu’il fut entré dans la maison, ses disciples lui demandèrent en particulier: « Pourquoi n’avons-nous pu chasser cet esprit? »
29 Ya amsa ya ce, “Sai da addu’akaɗai irin wannan yakan fita.”
Il leur dit: « Ce genre de démon ne peut être chassé que par la prière et le jeûne. »
30 Suka bar wurin suka bi ta Galili. Yesu bai so wani yă san inda suke ba,
Étant partis de là, ils cheminèrent à travers la Galilée, et Jésus ne voulait pas qu’on le sût,
31 gama yana koya wa almajiransa. Ya ce musu, “Za a ci amanar Ɗan Mutum, a ba da shi ga hannun mutane. Za su kashe shi, bayan kwana uku kuma zai tashi.”
car il enseignait ses disciples et leur disait: « Le fils de l’homme sera livré entre les mains des hommes, et ils le feront mourir, et le troisième jour après sa mort il ressuscitera. »
32 Amma ba su fahimci abin da yake nufi ba, suka kuma ji tsoro su tambaye shi game da wannan.
Mais ils ne comprenaient pas cette parole, et ils craignaient de l’interroger.
33 Suka iso Kafarnahum. Da yana cikin gida, sai ya tambaye su ya ce, “Gardamar me kuke yi a hanya?”
Ils arrivèrent à Capharnaüm. Lorsqu’il fut dans la maison, Jésus leur demanda: « De quoi parliez-vous en chemin? »
34 Amma suka yi shiru, don a hanya suna gardama ne, a kan ko wane ne a cikinsu ya fi girma?
Mais ils gardèrent le silence, car en chemin ils avaient discuté entre eux qui était le plus grand.
35 Da Yesu ya zauna, sai ya kira Sha Biyun ya ce, “In wani yana so yă zama na fari, dole yă zama na ƙarshe duka, da kuma bawan kowa.”
Alors ils s’assit, appela les Douze et leur dit: « Si quelqu’un veut être le premier, il sera le dernier de tous, et le serviteur de tous. »
36 Ya ɗauki wani ƙaramin yaro ya sa yă tsaya a tsakiyarsu. Ya ɗauke shi a hannunsa, ya ce musu,
Puis, prenant un petit enfant, il le mit au milieu d’eux; et après l’avoir embrassé, il leur dit:
37 “Duk wanda ya karɓi ɗaya daga cikin waɗannan ƙananan yara a cikin sunana, ni ya karɓa. Duk wanda kuma ya karɓe ni, ba ni ya karɓa ba, amma wanda ya aiko ni ne ya karɓa.”
« Quiconque reçoit en mon nom un de ces petits enfants, me reçoit; et quiconque me reçoit, ce n’est pas moi qu’il reçoit, mais celui qui m’a envoyé. »
38 Yohanna ya ce, “Malam mun ga wani mutum yana fitar da aljanu a cikin sunanka, sai muka ce yă daina, domin shi ba ɗaya daga cikinmu ba ne.”
Jean, prenant la parole, lui dit: « Maître, nous avons vu un homme qui ne va pas avec nous, chasser les démons en ton nom, et nous l’en avons empêché. »
39 Yesu ya ce, “Kada ku hana shi. Ba wanda yake yin ayyukan banmamaki a cikin sunana, nan take yă faɗi wani abu mummuna game da ni.
Mais Jésus dit: « Ne l’en empêchez pas, car personne ne peut faire de miracle en mon nom, et aussitôt après parler mal de moi.
40 Gama duk wanda ba ya gāba da mu, namu ne.
Qui n’est pas contre nous, est pour nous.
41 Gaskiya nake gaya muku, duk wanda ya ba ku ruwan sha a sunana, saboda ku na Kiristi ne, lalle, ba zai rasa ladarsa ba.
Car quiconque vous donnera un verre d’eau en mon nom, parce que vous êtes au Christ, je vous le dis, en vérité, il ne perdra pas sa récompense.
42 “Idan kuma wani yă sa ɗaya daga cikin waɗannan’yan yara masu gaskatawa da ni yă yi laifi, zai fiye masa a rataya wani babban dutsen niƙa a wuyarsa, a jefa shi cikin teku.
Et quiconque sera une occasion de chute pour un de ces petits qui croient en moi, il vaudrait mieux pour lui qu’on lui attachât au cou la meule qu’un âne tourne, et qu’on le jetât dans la mer. »
43 In hannunka yana sa ka yin zunubi, yanke shi. Ai, gwamma ka shiga rai da hannu ɗaya, da ka shiga jahannama ta wuta, inda ba a iya kashe wutar ba, da hannuwanka biyu. (Geenna )
« Si ta main est pour toi une occasion de chute, coupe-la: mieux vaut pour toi entrer mutilé dans la vie, que d’aller, ayant deux mains, dans la géhenne, dans le feu inextinguible, (Geenna )
[là où leur ver ne meurt pas, et où le feu ne s’éteint pas].
45 In kuma ƙafarka tana sa ka yin zunubi, yanke ta. Ai, gwamma ka shiga rai da ƙafa ɗaya, da a jefa ka cikin jahannama ta wuta, da ƙafafunka biyu. (Geenna )
Et si ton pied est pour toi une occasion de chute, coupe-le: mieux vaut pour toi entrer boiteux dans la vie, que d’être jeté, ayant deux pieds, dans la géhenne du feu inextinguible, (Geenna )
[là où leur ver ne meurt pas, et où le feu ne s’éteint pas.]
47 In kuma idonka yana sa ka zunubi, ƙwaƙule shi. Ai, gwamma ka shiga mulkin Allah da ido ɗaya, da a jefa ka cikin jahannama ta wuta, da idanu biyu, (Geenna )
Et si ton œil est pour toi une occasion de chute, arrache-le: mieux vaut pour toi entrer avec un seul œil dans le royaume de Dieu, que d’être jeté, ayant deux yeux, dans la géhenne du feu, (Geenna )
48 inda “‘tsutsotsinsu ba sa mutuwa, wutar kuma ba a iya kashewa.’
là où leur ver ne meurt pas, et où le feu ne s’éteint pas. »
49 Za a tsarkake kowa da wuta.
Car tout homme sera salé par le feu, et toute offrande sera salée avec du sel.
50 “Gishiri yana da daɗi, amma in ya rabu da ɗanɗanonsa, ta yaya za a sāke mai da ɗanɗanonsa? Ku kasance da gishiri a cikinku, ku kuma yi zauna lafiya da juna.”
Le sel est bon; mais si le sel s’affadit, avec quoi lui donnerez-vous de la saveur? Gardez bien le sel en vous, et soyez en paix les uns avec les autres. »