< Markus 9 >
1 Ya kuma ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, waɗansu da suke tsattsaye a nan ba za su mutu ba, sai sun ga mulkin Allah ya bayyana da iko.”
And he seide to hem, Treuli Y seie to you, that there ben summen stondynge here, whiche schulen not taste deth, til thei seen the rewme of God comynge in vertu.
2 Bayan kwana shida, sai Yesu ya ɗauki Bitrus, Yaƙub da Yohanna tare da shi, ya kai su kan wani dutse mai tsawo, suka kasance su kaɗai a wurin. A can aka sāke kamanninsa a gabansu.
And aftir sixe daies Jhesus took Petre, and James, and Joon, and ledde hem bi hem silf aloone in to an hiy hille; and he was transfigurid bifor hem.
3 Tufafinsa suka zama fari suna ƙyalli, fiye da yadda wani a duniya zai iya yi su.
And hise clothis weren maad ful schynynge and white as snow, whiche maner white clothis a fuller may not make on erthe.
4 Iliya da Musa suka bayyana a gabansu, suna magana da Yesu.
And Helie with Moises apperide to hem, and thei spaken with Jhesu.
5 Bitrus ya ce wa Yesu, “Rabbi, ya yi kyau da muke nan. Bari mu kafa bukkoki guda uku, ɗaya dominka, ɗaya domin Musa, ɗaya kuma domin Iliya.”
And Petre answeride, and seide to Jhesu, Maister, it is good vs to be here; and make we here thre tabernaclis, oon to thee, oon to Moyses, and oon to Helie.
6 (Bai san abin da zai faɗa ba ne, gama sun tsorata ƙwarai.)
For he wiste not what he schulde seie; for thei weren agaste bi drede.
7 Sai wani girgije ya bayyana, ya rufe su, wata murya kuma ta fito daga girgijen, ta ce, “Wannan Ɗana ne, wanda nake ƙauna, ku saurare shi!”
And ther was maad a cloude overschadewynge hem; and a vois cam of the cloude, and seide, This is my moost derworth sone, here ye hym.
8 Farat ɗaya, da suka waiwaya, ba su ƙara ganin kowa tare da su ba, sai dai Yesu.
And anoon thei bihelden aboute, and sayn no more ony man, but Jhesu oonli with hem.
9 Da suna saukowa daga dutsen, Yesu ya umarce su kada su gaya wa kowa abin da suka gani, sai bayan Ɗan Mutum ya tashi daga matattu.
And whanne thei camen doun fro the hille, he comaundide hem, that thei schulden not telle to ony man tho thingis that thei hadden seen, but whanne mannus sone hath risun ayen fro deeth.
10 Suka riƙe wannan zance a ɓoye tsakaninsu, suna tattaunawa ko mece ce ma’anar “tashi daga matattu.”
And thei helden the word at hem silf, sekynge what this schulde be, whanne he hadde risun ayen fro deth.
11 Suka tambaye shi, suka ce, “Don me malaman dokoki suke cewa, sai Iliya ya fara zuwa?”
And thei axiden hym, and seiden, What thanne seien Farisees and scribis, for it bihoueth `Helie to come first.
12 Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya ne, Iliya zai zo da fari, yă kuma mayar da dukan abubuwa. Don me kuma aka rubuta cewa, dole Ɗan Mutum yă sha wahala sosai, kuma a ƙi shi?
And he answeride, and seide to hem, Whanne Helie cometh, he schal first restore alle thingis; and as it is writun of mannus sone, that he suffre many thingis, and be dispisid.
13 Amma ina faɗa muku, Iliya ya riga ya zo, kuma suka yi duk abin da suka ga dama da shi, kamar yadda aka rubuta game da shi.”
And Y seie to you, that Helie is comun, and thei diden to hym what euer thingis thei wolden, as it is writun of hym.
14 Da suka dawo wurin sauran almajiran, sai suka ga babban taro kewaye da su, malaman dokoki suna gardama da su.
And he comynge to hise disciplis, saiy a greet cumpany aboute hem, and scribis disputynge with hem.
15 Nan take da dukan mutanen suka ga Yesu, sai suka cika da mamaki, suka ruga da gudu don su gai da shi.
And anoon al the puple seynge Jhesu, was astonyed, and thei dredden; and thei rennynge gretten hym.
16 Ya tambaye su ya ce, “Gardamar me kuke yi da su?”
And he axide hem, What disputen ye among you?
17 Wani mutum a cikin taron ya amsa ya ce, “Malam, na kawo maka ɗana mai wani ruhun da yake hana shi magana.
And oon of the cumpany answerde, and seide, Mayster, Y haue brouyt to thee my sone, that hath a doumbe spirit; and where euer he takith hym,
18 Duk lokacin da mugun ruhun ya kama shi, yakan jefa shi a ƙasa. Bakinsa yakan yi kumfa, yă cije haƙorarsa, yakan sa jikinsa ya sandare, yă zama da ƙarfi. Na roƙi almajiranka su fitar da ruhun, amma ba su iya ba.”
he hurtlith hym doun, and he fometh, and betith togidir with teeth, and wexith drye. And Y seide to thi disciplis, that thei schulden caste hym out, and thei myyten not.
19 Yesu ya ce, “Ya ku zamani marar bangaskiya, har yaushe zan kasance tare da ku? Har yaushe zan yi haƙuri da ku? Kawo mini yaron.”
And he answeride to hem, and seide, A! thou generacioun out of bileue, hou longe schal Y be among you, hou longe schal Y suffre you? Brynge ye hym to me.
20 Sai suka kawo shi. Da ruhun ya ga Yesu, nan da nan sai ya buge yaron da farfaɗiya. Ya fāɗi a ƙasa, yana birgima, bakinsa yana kumfa.
And thei brouyten hym. And whanne he had seyn him, anoon the spirit troublide him; and was throw doun to grounde, and walewide, and fomede.
21 Yesu ya tambayi mahaifin yaron ya ce, “Tun yaushe yake haka?” Ya ce, “Tun yana ƙarami.
And he axide his fadir, Hou longe `is it, sith this `hath falle to hym? And he seide, Fro childhode;
22 Ya sha jefa shi cikin wuta, ko ruwa don yă kashe shi. Amma in za ka iya yin wani abu, ka ji tausayinmu ka taimake mu.”
and ofte he hath put hym in to fier, and in to watir, to leese hym; but if thou maiste ony thing, helpe vs, and haue merci on vs.
23 Yesu ya ce, “‘In za ka iya’? Ai, kome mai yiwuwa ne ga wanda ya gaskata.”
And Jhesus seide to hym, If thou maiste bileue, alle thingis ben possible to man that bileueth.
24 Nan da nan mahaifin yaron ya faɗa da ƙarfi ya ce, “Na gaskata, ka taimake ni in sha kan rashin bangaskiyata!”
And anoon the fadir of the child criede with teeris, and seide, Lord, Y bileue; Lord, helpe thou myn vnbileue.
25 Da Yesu ya ga taron suna zuwa can a guje, sai ya tsawata wa mugun ruhun ya ce, “Kai ruhun kurma, da na bebe, na umarce ka, ka fita daga cikinsa, kada kuma ka ƙara shigarsa.”
And whanne Jhesus hadde seyn the puple rennynge togidere, he manasside the vnclene spirit, and seide to hym, Thou deef and doumbe spirit, Y comaunde thee, go out fro hym, and entre no more in to hym.
26 Sai ruhun ya yi ihu, ya buge shi da ƙarfi da farfaɗiya, ya fita. Yaron ya kwanta kamar matacce, har mutane da yawa suka ce, “Ai, ya mutu.”
And he criynge, and myche to breidynge him, wente out fro hym; and he was maad as deed, so that many seiden, that he was deed.
27 Amma Yesu ya kama shi a hannu ya ɗaga, ya kuwa tashi tsaye.
And Jhesus helde his hoond, and lifte hym vp; and he roos.
28 Da Yesu ya shiga gida, almajiransa suka tambaye shi a ɓoye, suka ce, “Me ya sa ba mu iya fitar da shi ba?”
And whanne he hadde entrid in to an hous, hise disciplis axiden hym priueli, Whi myyten not we caste hym out?
29 Ya amsa ya ce, “Sai da addu’akaɗai irin wannan yakan fita.”
And he seide to hem, This kynde in no thing may go out, but in preier and fastyng.
30 Suka bar wurin suka bi ta Galili. Yesu bai so wani yă san inda suke ba,
And thei yeden fro thennus, and wente forth in to Galile; and thei wolden not, that ony man wiste.
31 gama yana koya wa almajiransa. Ya ce musu, “Za a ci amanar Ɗan Mutum, a ba da shi ga hannun mutane. Za su kashe shi, bayan kwana uku kuma zai tashi.”
And he tauyte hise disciplis, and seide to hem, For mannus sone schal be bitrayed in to the hondis of men, and thei schulen sle hym, and he slayn schal ryse ayen on the thridde day.
32 Amma ba su fahimci abin da yake nufi ba, suka kuma ji tsoro su tambaye shi game da wannan.
And thei knewen not the word, and dredden to axe hym.
33 Suka iso Kafarnahum. Da yana cikin gida, sai ya tambaye su ya ce, “Gardamar me kuke yi a hanya?”
And thei camen to Cafarnaum. And whanne thei weren in the hous, he axide hem, What tretiden ye in the weie?
34 Amma suka yi shiru, don a hanya suna gardama ne, a kan ko wane ne a cikinsu ya fi girma?
And thei weren stille; for thei disputiden among hem in the weie, who of hem schulde be grettest.
35 Da Yesu ya zauna, sai ya kira Sha Biyun ya ce, “In wani yana so yă zama na fari, dole yă zama na ƙarshe duka, da kuma bawan kowa.”
And he sat, and clepide the twelue, and seide to hem, If ony man wole be the firste among you, he schal be the laste of alle, and the mynyster of alle.
36 Ya ɗauki wani ƙaramin yaro ya sa yă tsaya a tsakiyarsu. Ya ɗauke shi a hannunsa, ya ce musu,
And he took a child, and sette hym in the myddil of hem; and whanne he hadde biclippid hym, he seide to hem,
37 “Duk wanda ya karɓi ɗaya daga cikin waɗannan ƙananan yara a cikin sunana, ni ya karɓa. Duk wanda kuma ya karɓe ni, ba ni ya karɓa ba, amma wanda ya aiko ni ne ya karɓa.”
Who euer resseyueth oon of such children in my name, he resseyueth me; and who euer resseyueth me, he resseyueth not me aloone, but hym that sente me.
38 Yohanna ya ce, “Malam mun ga wani mutum yana fitar da aljanu a cikin sunanka, sai muka ce yă daina, domin shi ba ɗaya daga cikinmu ba ne.”
Joon answeride to hym, and seide, Maister, we sayn oon castynge out feendis in thi name, which sueth not vs, and we han forbodun hym.
39 Yesu ya ce, “Kada ku hana shi. Ba wanda yake yin ayyukan banmamaki a cikin sunana, nan take yă faɗi wani abu mummuna game da ni.
And Jhesus seide, Nyle ye forbede him; for ther is no man that doith vertu in my name, and may soone speke yuel of me.
40 Gama duk wanda ba ya gāba da mu, namu ne.
He that is not ayens vs, is for vs.
41 Gaskiya nake gaya muku, duk wanda ya ba ku ruwan sha a sunana, saboda ku na Kiristi ne, lalle, ba zai rasa ladarsa ba.
And who euer yyueth you a cuppe of coold water to drynke in my name, for ye ben of Crist, treuli Y seie to you, he schal not leese his mede.
42 “Idan kuma wani yă sa ɗaya daga cikin waɗannan’yan yara masu gaskatawa da ni yă yi laifi, zai fiye masa a rataya wani babban dutsen niƙa a wuyarsa, a jefa shi cikin teku.
And who euer schal sclaundre oon of these litle that bileuen in me, it were betere to hym that a mylne stoon `of assis were don aboute his necke, and he were cast in to the see.
43 In hannunka yana sa ka yin zunubi, yanke shi. Ai, gwamma ka shiga rai da hannu ɗaya, da ka shiga jahannama ta wuta, inda ba a iya kashe wutar ba, da hannuwanka biyu. (Geenna )
And if thin hoond sclaundre thee, kitte it awey; it is betere to thee to entre feble in to lijf, than haue two hondis, and go in to helle, in to fier that neuer schal be quenchid, (Geenna )
where the worm of hem dieth not, and the fier is not quenchid.
45 In kuma ƙafarka tana sa ka yin zunubi, yanke ta. Ai, gwamma ka shiga rai da ƙafa ɗaya, da a jefa ka cikin jahannama ta wuta, da ƙafafunka biyu. (Geenna )
And if thi foote sclaundre thee, kitte it of; it is betere to thee to entre crokid in to euerlastynge lijf, than haue twei feet, and be sent in to helle of fier, that neuer schal be quenchid, (Geenna )
where the worme of hem dieth not, and the fier is not quenchid.
47 In kuma idonka yana sa ka zunubi, ƙwaƙule shi. Ai, gwamma ka shiga mulkin Allah da ido ɗaya, da a jefa ka cikin jahannama ta wuta, da idanu biyu, (Geenna )
That if thin iye sclaundre thee, cast it out; it is betere to thee to entre gogil iyed in to the reume of God, than haue twey iyen, and be sent in to helle of fier, where the worme of hem dieth not, (Geenna )
48 inda “‘tsutsotsinsu ba sa mutuwa, wutar kuma ba a iya kashewa.’
and the fier is not quenchid.
49 Za a tsarkake kowa da wuta.
And euery man schal be saltid with fier, and euery slayn sacrifice schal be maad sauery with salt.
50 “Gishiri yana da daɗi, amma in ya rabu da ɗanɗanonsa, ta yaya za a sāke mai da ɗanɗanonsa? Ku kasance da gishiri a cikinku, ku kuma yi zauna lafiya da juna.”
Salt is good; if salt be vnsauery, in what thing schulen ye make it sauery? Haue ye salt among you, and haue ye pees among you.