< Markus 9 >
1 Ya kuma ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, waɗansu da suke tsattsaye a nan ba za su mutu ba, sai sun ga mulkin Allah ya bayyana da iko.”
And he said to them, “Amen I say to you, that there are some among those standing here who shall not taste death until they see the kingdom of God arriving in power.”
2 Bayan kwana shida, sai Yesu ya ɗauki Bitrus, Yaƙub da Yohanna tare da shi, ya kai su kan wani dutse mai tsawo, suka kasance su kaɗai a wurin. A can aka sāke kamanninsa a gabansu.
And after six days, Jesus took with him Peter, and James, and John; and he led them separately to a lofty mountain alone; and he was transfigured before them.
3 Tufafinsa suka zama fari suna ƙyalli, fiye da yadda wani a duniya zai iya yi su.
And his vestments became radiant and exceedingly white like snow, with such a brilliance as no fuller on earth is able to achieve.
4 Iliya da Musa suka bayyana a gabansu, suna magana da Yesu.
And there appeared to them Elijah with Moses; and they were speaking with Jesus.
5 Bitrus ya ce wa Yesu, “Rabbi, ya yi kyau da muke nan. Bari mu kafa bukkoki guda uku, ɗaya dominka, ɗaya domin Musa, ɗaya kuma domin Iliya.”
And in response, Peter said to Jesus: “Master, it is good for us to be here. And so let us make three tabernacles, one for you, and one for Moses, and one for Elijah.”
6 (Bai san abin da zai faɗa ba ne, gama sun tsorata ƙwarai.)
For he did not know what he was saying. For they were overwhelmed by fear.
7 Sai wani girgije ya bayyana, ya rufe su, wata murya kuma ta fito daga girgijen, ta ce, “Wannan Ɗana ne, wanda nake ƙauna, ku saurare shi!”
And there was a cloud overshadowing them. And a voice came from the cloud, saying: “This is my most beloved Son. Listen to him.”
8 Farat ɗaya, da suka waiwaya, ba su ƙara ganin kowa tare da su ba, sai dai Yesu.
And immediately, looking around, they no longer saw anyone, except Jesus alone with them.
9 Da suna saukowa daga dutsen, Yesu ya umarce su kada su gaya wa kowa abin da suka gani, sai bayan Ɗan Mutum ya tashi daga matattu.
And as they were descending from the mountain, he instructed them not to relate to anyone what they had seen, until after the Son of man will have risen again from the dead.
10 Suka riƙe wannan zance a ɓoye tsakaninsu, suna tattaunawa ko mece ce ma’anar “tashi daga matattu.”
And they kept the word to themselves, arguing about what “after he will have risen from the dead” might mean.
11 Suka tambaye shi, suka ce, “Don me malaman dokoki suke cewa, sai Iliya ya fara zuwa?”
And they questioned him, saying: “Then why do the Pharisees and the scribes say that Elijah must arrive first?”
12 Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya ne, Iliya zai zo da fari, yă kuma mayar da dukan abubuwa. Don me kuma aka rubuta cewa, dole Ɗan Mutum yă sha wahala sosai, kuma a ƙi shi?
And in response, he said to them: “Elijah, when he will arrive first, shall restore all things. And in the manner that it has been written about the Son of man, so must he suffer many things and be condemned.
13 Amma ina faɗa muku, Iliya ya riga ya zo, kuma suka yi duk abin da suka ga dama da shi, kamar yadda aka rubuta game da shi.”
But I say to you, that Elijah also has arrived, (and they have done to him whatever they wanted) just as it has been written about him.”
14 Da suka dawo wurin sauran almajiran, sai suka ga babban taro kewaye da su, malaman dokoki suna gardama da su.
And approaching his disciples, he saw a great crowd surrounding them, and the scribes were arguing with them.
15 Nan take da dukan mutanen suka ga Yesu, sai suka cika da mamaki, suka ruga da gudu don su gai da shi.
And soon all the people, seeing Jesus, were astonished and struck with fear, and hurrying to him, they greeted him.
16 Ya tambaye su ya ce, “Gardamar me kuke yi da su?”
And he questioned them, “What are you arguing about among yourselves?”
17 Wani mutum a cikin taron ya amsa ya ce, “Malam, na kawo maka ɗana mai wani ruhun da yake hana shi magana.
And one from the crowd responded by saying: “Teacher, I have brought to you my son, who has a mute spirit.
18 Duk lokacin da mugun ruhun ya kama shi, yakan jefa shi a ƙasa. Bakinsa yakan yi kumfa, yă cije haƙorarsa, yakan sa jikinsa ya sandare, yă zama da ƙarfi. Na roƙi almajiranka su fitar da ruhun, amma ba su iya ba.”
And whenever it takes hold of him, it throws him down, and he foams and gnashes with his teeth, and he becomes unconscious. And I asked your disciples to cast him out, and they could not.”
19 Yesu ya ce, “Ya ku zamani marar bangaskiya, har yaushe zan kasance tare da ku? Har yaushe zan yi haƙuri da ku? Kawo mini yaron.”
And answering them, he said: “O unbelieving generation, how long must I be with you? How long shall I endure you? Bring him to me.”
20 Sai suka kawo shi. Da ruhun ya ga Yesu, nan da nan sai ya buge yaron da farfaɗiya. Ya fāɗi a ƙasa, yana birgima, bakinsa yana kumfa.
And they brought him. And when he had seen him, immediately the spirit disturbed him. And having been thrown to the ground, he rolled around foaming.
21 Yesu ya tambayi mahaifin yaron ya ce, “Tun yaushe yake haka?” Ya ce, “Tun yana ƙarami.
And he questioned his father, “How long has this been happening to him?” But he said: “From infancy.
22 Ya sha jefa shi cikin wuta, ko ruwa don yă kashe shi. Amma in za ka iya yin wani abu, ka ji tausayinmu ka taimake mu.”
And often it casts him into fire or into water, in order to destroy him. But if you are able to do anything, help us and take pity on us.”
23 Yesu ya ce, “‘In za ka iya’? Ai, kome mai yiwuwa ne ga wanda ya gaskata.”
But Jesus said to him, “If you are able to believe: all things are possible to one who believes.”
24 Nan da nan mahaifin yaron ya faɗa da ƙarfi ya ce, “Na gaskata, ka taimake ni in sha kan rashin bangaskiyata!”
And immediately the father of the boy, crying out with tears, said: “I do believe, Lord. Help my unbelief.”
25 Da Yesu ya ga taron suna zuwa can a guje, sai ya tsawata wa mugun ruhun ya ce, “Kai ruhun kurma, da na bebe, na umarce ka, ka fita daga cikinsa, kada kuma ka ƙara shigarsa.”
And when Jesus saw the crowd rushing together, he admonished the unclean spirit, saying to him, “Deaf and mute spirit, I command you, leave him; and do not enter into him anymore.”
26 Sai ruhun ya yi ihu, ya buge shi da ƙarfi da farfaɗiya, ya fita. Yaron ya kwanta kamar matacce, har mutane da yawa suka ce, “Ai, ya mutu.”
And crying out, and convulsing him greatly, he departed from him. And he became like one who is dead, so much so that many said, “He is dead.”
27 Amma Yesu ya kama shi a hannu ya ɗaga, ya kuwa tashi tsaye.
But Jesus, taking him by the hand, lifted him up. And he arose.
28 Da Yesu ya shiga gida, almajiransa suka tambaye shi a ɓoye, suka ce, “Me ya sa ba mu iya fitar da shi ba?”
And when he had entered into the house, his disciples questioned him privately, “Why were we unable to cast him out?”
29 Ya amsa ya ce, “Sai da addu’akaɗai irin wannan yakan fita.”
And he said to them, “This kind is able to be expelled by nothing other than prayer and fasting.”
30 Suka bar wurin suka bi ta Galili. Yesu bai so wani yă san inda suke ba,
And setting out from there, they passed through Galilee. And he intended that no one know about it.
31 gama yana koya wa almajiransa. Ya ce musu, “Za a ci amanar Ɗan Mutum, a ba da shi ga hannun mutane. Za su kashe shi, bayan kwana uku kuma zai tashi.”
Then he taught his disciples, and he said to them, “For the Son of man shall be delivered into the hands of men, and they will kill him, and having been killed, on the third day he will rise again.”
32 Amma ba su fahimci abin da yake nufi ba, suka kuma ji tsoro su tambaye shi game da wannan.
But they did not understand the word. And they were afraid to question him.
33 Suka iso Kafarnahum. Da yana cikin gida, sai ya tambaye su ya ce, “Gardamar me kuke yi a hanya?”
And they went to Capernaum. And when they were in the house, he questioned them, “What did you discuss on the way?”
34 Amma suka yi shiru, don a hanya suna gardama ne, a kan ko wane ne a cikinsu ya fi girma?
But they were silent. For indeed, on the way, they had disputed among themselves as to which of them was greater.
35 Da Yesu ya zauna, sai ya kira Sha Biyun ya ce, “In wani yana so yă zama na fari, dole yă zama na ƙarshe duka, da kuma bawan kowa.”
And sitting down, he called the twelve, and he said to them, “If anyone wants to be first, he shall be the last of all and the minister of all.”
36 Ya ɗauki wani ƙaramin yaro ya sa yă tsaya a tsakiyarsu. Ya ɗauke shi a hannunsa, ya ce musu,
And taking a child, he set him in their midst. And when he had embraced him, he said to them:
37 “Duk wanda ya karɓi ɗaya daga cikin waɗannan ƙananan yara a cikin sunana, ni ya karɓa. Duk wanda kuma ya karɓe ni, ba ni ya karɓa ba, amma wanda ya aiko ni ne ya karɓa.”
“Whoever receives one such child in my name, receives me. And whoever receives me, receives not me, but him who sent me.”
38 Yohanna ya ce, “Malam mun ga wani mutum yana fitar da aljanu a cikin sunanka, sai muka ce yă daina, domin shi ba ɗaya daga cikinmu ba ne.”
John responded to him by saying, “Teacher, we saw someone casting out demons in your name; he does not follow us, and so we prohibited him.”
39 Yesu ya ce, “Kada ku hana shi. Ba wanda yake yin ayyukan banmamaki a cikin sunana, nan take yă faɗi wani abu mummuna game da ni.
But Jesus said: “Do not prohibit him. For there is no one who can act with virtue in my name and soon speak evil about me.
40 Gama duk wanda ba ya gāba da mu, namu ne.
For whoever is not against you is for you.
41 Gaskiya nake gaya muku, duk wanda ya ba ku ruwan sha a sunana, saboda ku na Kiristi ne, lalle, ba zai rasa ladarsa ba.
For whoever, in my name, will give you a cup of water to drink, because you belong to Christ: Amen I say to you, he shall not lose his reward.
42 “Idan kuma wani yă sa ɗaya daga cikin waɗannan’yan yara masu gaskatawa da ni yă yi laifi, zai fiye masa a rataya wani babban dutsen niƙa a wuyarsa, a jefa shi cikin teku.
And whoever will have scandalized one of these little ones who believe in me: it would be better for him if a great millstone were placed around his neck and he were thrown into the sea.
43 In hannunka yana sa ka yin zunubi, yanke shi. Ai, gwamma ka shiga rai da hannu ɗaya, da ka shiga jahannama ta wuta, inda ba a iya kashe wutar ba, da hannuwanka biyu. (Geenna )
And if your hand causes you to sin, cut it off: it is better for you to enter into life disabled, than having two hands to go into Hell, into the unquenchable fire, (Geenna )
where their worm does not die, and the fire is not extinguished.
45 In kuma ƙafarka tana sa ka yin zunubi, yanke ta. Ai, gwamma ka shiga rai da ƙafa ɗaya, da a jefa ka cikin jahannama ta wuta, da ƙafafunka biyu. (Geenna )
But if your foot causes you to sin, chop it off: it is better for you to enter into eternal life lame, than having two feet to be cast into the Hell of unquenchable fire, (Geenna )
where their worm does not die, and the fire is not extinguished.
47 In kuma idonka yana sa ka zunubi, ƙwaƙule shi. Ai, gwamma ka shiga mulkin Allah da ido ɗaya, da a jefa ka cikin jahannama ta wuta, da idanu biyu, (Geenna )
But if your eye causes you to sin, pluck it out: it is better for you to enter into the kingdom of God with one eye, than having two eyes to be cast into the Hell of fire, (Geenna )
48 inda “‘tsutsotsinsu ba sa mutuwa, wutar kuma ba a iya kashewa.’
where their worm does not die, and the fire is not extinguished.
49 Za a tsarkake kowa da wuta.
For all shall be salted with fire, and every victim shall be salted with salt.
50 “Gishiri yana da daɗi, amma in ya rabu da ɗanɗanonsa, ta yaya za a sāke mai da ɗanɗanonsa? Ku kasance da gishiri a cikinku, ku kuma yi zauna lafiya da juna.”
Salt is good: but if the salt has become bland, with what will you season it? Have salt in yourselves, and have peace among yourselves.”