< Markus 8 >
1 A kwanakin nan wani taro mai girma ya taru. Tun da yake ba su da abin da za su ci, sai Yesu ya kira almajiransa ya ce,
Gene mobhago, lugwinjili lwa bhandu gulugumbele kabhili. Pabha bhakakwetenjeje shalya, a Yeshu gubhaashemilenje bhaajiganywa bhabho, gubhaalugulilenje,
2 “Ina jin tausayin mutanen nan, kwanansu uku ke nan tare da ni, kuma ba su da abin da za su ci.
“Ngunakwaabhonelanga shiya bhandunjibha pabha bhashitamangana na nne mobha gatatu na bhangalinji shalya.
3 In na sallame su gida da yunwa, za su kāsa a hanya, don waɗansu daga cikinsu sun zo daga nesa.”
Naalugulilangaga bhajabhulangane kunngwabhonji bhalinginji na shibhanga, shibhaondokanje mumpanda, pabha bhananji kubhakopokenje kwatalika.”
4 Almajiransa suka amsa suka ce, “Amma a ina, a wannan wurin da ba kowa, wani zai iya samun isashen burodi, don a ciyar da su?”
Bhaajiganywa bhabho gubhaabhushiyenje a Yeshu, “Putuli pano p akonde, tupate kwei mikate ja jukuta bhandu bhowebha?”
5 Sai Yesu ya yi tambaya ya ce, “Burodi guda nawa kuke da su?” Suka ce, “Bakwai.”
A Yeshu gubhaabhushiyenje, “Nkwetenje mikate jilingwa?” Gubhaajangwilenje, “Shabha.”
6 Sai ya gaya wa taron su zazzauna a ƙasa. Bayan ya ɗauki burodin nan bakwai, ya yi godiya, sai ya kakkarya, ya ba wa almajiransa su rarraba wa mutanen, suka kuwa yi haka.
Bhai, gubhaamulishenje bhandu bhatamangane pai. Gubhatolile mikate shabha jila gubhatendile eja kwa a Nnungu, gubhajigebhenye, gubhaapelenje bhaajiganywa bhabho bhaapanganje bhandu, na bhalabhonji gubhaapelenje.
7 Suna kuma da ƙananan kifaye kaɗan, ya ba da godiya dominsu, ya kuma ce wa almajiran su rarraba musu.
Bhashinkukolanga na yamaki ishokope. A Yeshu gubhatendile eja kwa a Nnungu, gubhaalugulilenje bhaapanganje bhandu.
8 Mutanen suka ci, suka ƙoshi. Daga baya, almajiran suka tattara gutsattsarin da suka rage cike da kwanduna bakwai.
Bhandu gubhalilenje na jukuta. Gubhakundikenyenje malepei gubhagumbeyenje ikapu shabha.
9 Wajen maza dubu huɗu ne suka kasance. Da ya sallame su,
Bhandu bhalilenje bhala pubhalinginji mbuti elupu nsheshe. A Yeshu gubhaalajilenje bhandu, nikwaalekanga bhajendangane kumui.
10 sai ya shiga jirgin ruwa tare da almajiransa, suka tafi yankin Dalmanuta.
Kashokope gubhakwelile mmashua pamo na bhaajiganywa bhabho, gubhapitengene shilambo sha ku Dalumanuta.
11 Farisiyawa suka zo suka fara yin wa Yesu tambayoyi. Don su gwada shi, sai suka nemi yă nuna musu wata alama daga sama.
Mapalishayo gubhaikengenenje, gubhatandwibhenje kutaukangana na a Yeshu. Nkwaalinga, gubhapinjilenje bhatende shilangulo kopoka kunnungu.
12 Sai ya ja numfashi mai zurfi ya ce, “Don me wannan zamani yake neman ganin abin banmamaki? Gaskiya nake gaya muku, ba wata alamar da za a ba su.”
A Yeshu gubhatulwiye mbumu, nigubhashite, “Pakuti alu lubhelekolu lunapinga ilangulo? Kweli ngunakummalanjilanga, alu lubhelekolu lukapegwa shilangulo shoshowe.”
13 Sai ya bar su, ya koma cikin jirgin ruwan, suka ƙetare zuwa ɗaya hayin.
Bhai a Yeshu gubhaaleshilenje, gubhakwelile kabhili mmashua, gubhatandwibhe mwanja gwa jomboka litanda.
14 Almajiran suka manta su riƙe burodi, sai dai guda ɗaya da suke da shi a cikin jirgin ruwan.
Bhaajiganywa bhashinkulibhalanga jigala mikate, ikabhe nkate gumope gwapali mumashua.
15 Yesu ya gargaɗe su ya ce, “Ku yi hankali, ku kuma lura da yistin Farisiyawa da na Hiridus.”
A Yeshu gubhaaleshiyenje bhalinkuti, “Nnolanje! Mwiteiganje na ngedule ya Mapalishayo na ya a Elode.”
16 Suka tattauna wannan da juna, suna cewa, “Don ba mu da burodi ne.”
Bhaajiganywa gubhatandwibhenje kubheleketa ashaayenenji, “Bhanabheleketa genego pakubha twangali mikate.”
17 Da ya gane abin da suke tattaunawa, sai Yesu ya tambaye su ya ce, “Don me kuke zancen rashin burodi? Har yanzu ba ku gane ko fahimta ba? Zukatanku sun taurare ne?
A Yeshu gubhamumanyi gubhaalugulilenje, Kwa nndi nnaganishiyanga ga ngajigala mikate? Bhuli, nkanabhe kumumanyangape? Bhuli mitima jenunji jishinonopa?
18 Kuna da idanu, amma kun kāsa gani, kuna da kunnuwa, amma kun kāsa ji? Ba ku tuna ba?
Bhuli, nkwetenje meyo na nkalolanga? Nkwetenje makutu na nkapilikananga? Bhuli, nkakumbushilanga.
19 Da na kakkarya burodi guda biyar wa mutane dubu biyar, kwanduna nawa kuka kwashe cike da gutsattsarin?” Suka amsa, “Sha biyu.”
Lyene lyubha linagebhenye mikate ng'ano na kwaliyanga bhandu elupu ng'ano? Imwalokotenje ikapu ilingwa ya malepeyo? Gubhajangwilenje “Ikapu likumi limo na ibhili.”
20 “Da na kuma kakkarya burodin nan bakwai wa mutum dubu huɗu, kwanduna nawa kuka kwashe cike da gutsattsarin?” Suka ce, “Bakwai.”
Na punagebhenye mikate shabha na kwaliyanga bhandu elupu nsheshe, imwalokotenje ikapu ilingwa? Gubhajangwilenje, “Shabha.”
21 Ya ce musu, “Har yanzu ba ku fahimta ba?”
Bhai, gubhaalugulilenje, “Nkanabhe ng'amulangape?”
22 Suka iso Betsaida, sai waɗansu mutane suka kawo wani makaho, suka roƙi Yesu yă taɓa shi.
A Yeshu na bhaajiganywa bhabho gubhaikengenenje ku Bhetishaida, gubhaapeleshelenje mundu jumo nangalole, nikwashondelesheya a Yeshu bhankwaye nkupinga alame.
23 Yesu ya kama hannun makahon ya kai shi bayan ƙauyen. Bayan ya tofa miyau a idanun mutumin, ya kuma ɗibiya masa hannuwansa, sai ya tambaye shi ya ce, “Kana iya ganin wani abu?”
A Yeshu gubhankamwile nkono, gubhapite najo kunyenje shijiji. Gubhanng'unile mata mmeyo, gubhankwashiye na makono, gubhammushiye, “Bhuli, ulikushibhona shindu shoshowe?”
24 Sai ya ɗaga kai ya ce, “Ina ganin mutane, suna kama da itatuwa da suke tafiya.”
Nangalole jula gwalolile, nigwashite, “Ngunakwabhonanga bhandu bhabhagwinji mbuti mikongo jilikwenda.”
25 Yesu ya sāke ɗibiya hannuwansa a idanun mutumin, sai idanunsa suka buɗe, ya sami gani, ya kuma ga kome sarai.
Kungai a Yeshu gubhankwashiye kabhili na makono kumeyo, na jwalakwe gwabhalakwile meyo nigwalamile, gwaibhweni indu yowe ukoto.
26 Yesu ya sallame shi gida ya ce, “Kada ka shiga cikin ƙauyen.”
A Yeshu gubhannugulile ajende kunngwakwe nikung'amulisha, “Unabhuje kushijiji!”
27 Yesu da almajiransa suka tafi ƙauyukan da suke kewaye da Kaisariya Filibbi. A hanya ya tambaye su ya ce, “Wa, mutane suke ce da ni?”
Kungai a Yeshu na bhaajiganywa bhabho gubhapitengenenje muijiji ya ku Kaishalia Pilipi. Bhalinginji mumpanda a Yeshu gubhabhushiyenje bhaajiganywa bhabho, “Bhandu bhakutinji nne gani?”
28 Suka amsa, suka ce, “Waɗansu suna cewa, Yohanna Mai Baftisma, waɗansu Iliya, waɗansu kuma har wa yau sun ce, ɗaya daga cikin annabawa.”
Gubhaajangwilenje, “Bhananji bhakutinji mmwe a Yowana Bhabhatisha na bhananji bhakutinji a Eliya na bhananji bhakutinji jumo jwa munkumbi gwa ashinkulondola bha a Nnungu.”
29 Sai ya yi tambaya ya ce, “Amma ku fa, wa kuke ce da ni?” Bitrus ya amsa ya ce, “Kai ne Kiristi.”
Nabhalabho a Yeshu gubhaabhushiyenje, “Na mmanganya bhuli, nkutinji nne gani?” A Petili gubhaajangwile, “Mmwe a Kilishitu, nng'agwilwe na a Nnungu”
30 Yesu ya gargaɗe su kada su gaya wa kowa kome a kansa.
A Yeshu gubhaalimbiyenje bhanannugulilanje mundu jojowe jene nganijo.
31 Sai ya fara koya musu cewa, dole Ɗan Mutum yă sha wahaloli da yawa, dattawa, manyan firistoci da malaman dokoki kuma su ƙi shi. Dole kuma a kashe shi, bayan kwana uku kuma, yă tashi.
A Yeshu gubhatandwibhe kwaajiganyanga bhaajiganywa bhabho kuti, inapinjikwa Mwana juka Mundu apotekwe na kanwa na bhanangulungwa na bhakulungwanji bhaabhishila na bhaajiganya bha shalia. Abhulagwe na lyubha lya tatu shaayushe.
32 Ya yi wannan zance a sarari. Sai Bitrus ya jawo shi gefe, ya fara tsawata masa.
A Yeshu bhashinkwaalugulilanga gwangali nng'iyo. Penepo a Petili, gubhaatolile a Yeshu kunyenje na gubhatandwibhe kwaakalipila.
33 Amma da Yesu ya juya ya dubi almajiransa, sai ya tsawata wa Bitrus ya ce, “Tashi daga nan Shaiɗan! Ba ka da al’amuran Allah a zuciyarka, sai na mutane.”
Ikabheje a Yeshu gubhatendebhwishe, gubhaalolilenje bhaajiganywa bhabho, gubhaakalipile a Petili bhalinkuti, “Njoshela apano, Lishetani gwe! Pabha ukaganishiya ga a Nnungu ikabhe ga shigundupe.”
34 Sai ya kira taron wurinsa tare da almajiransa ya ce, “Duk wanda zai bi ni, dole yă ƙi kansa, yă ɗauki gicciyensa yă bi ni.
Kungai a Yeshu gubhaashemilenje bhandu bhagumbelenje bhala na bhaajiganywa bhabho, gubhaalugulilenje, “Mundu jojowe apinga ngagula nne, anapinjikwa aikane nnyene, ajigale nshalabha gwakwe angagule.
35 Domin duk mai son ceton ransa zai rasa shi, amma duk wanda ya rasa ransa saboda ni, da kuma bishara, zai same shi.
Pabha mundu apinga lamya gumi gwakwe shaguobhye, ikabheje akuguobhya gumi gwakwe kwa ligongo lyangu nne na ligongo lya Ngani ja Mmbone, shagutapule.
36 Me mutum zai amfana, in ya ribato duniya duka a bakin ransa?
Bhuli, shiimpwaile indi mundu apegwaga indu yowe ya nshilambolyo showe akuno aliobhya gumi gwakwe?
37 Ko kuma, me mutum zai bayar a musayar ransa?
Eu mundu shashoye shindu shashi pa gumi gwakwe?
38 Duk wanda ya ji kunyata, da na kalmomina a wannan zamani na fasikanci da zunubi, Ɗan Mutum ma zai ji kunyarsa lokacin da ya shiga cikin ɗaukakar Ubansa, tare da tsarkakan mala’iku.”
Mundu jojowe munkumbi gwa lubheleko lwangakulupalika kwa a Nnungu na lwa yambilu, ashangolele oni nne na malobhe gangu, nne mwana juka Mundu shininkolele oni jwene mundujo, malanga pushing'ishe Muukonjelo gwa Atati pamo na ashimalaika bha Ukonjelo bha kunnungu.”