< Markus 8 >
1 A kwanakin nan wani taro mai girma ya taru. Tun da yake ba su da abin da za su ci, sai Yesu ya kira almajiransa ya ce,
In those days, there being again a very great multitude, and they having nothing to eat, Jesus called his disciples to Him,
2 “Ina jin tausayin mutanen nan, kwanansu uku ke nan tare da ni, kuma ba su da abin da za su ci.
and saith unto them, I have compassion on the multitude, for they have now been with me three days, and have nothing to eat:
3 In na sallame su gida da yunwa, za su kāsa a hanya, don waɗansu daga cikinsu sun zo daga nesa.”
and if I send them away fasting to their own home, they will faint by the way; for some of them are come from far.
4 Almajiransa suka amsa suka ce, “Amma a ina, a wannan wurin da ba kowa, wani zai iya samun isashen burodi, don a ciyar da su?”
And his disciples answered Him, From whence can one satisfy these people with bread here in a desert?
5 Sai Yesu ya yi tambaya ya ce, “Burodi guda nawa kuke da su?” Suka ce, “Bakwai.”
And He asked them, How many loaves have ye? and they said, Seven.
6 Sai ya gaya wa taron su zazzauna a ƙasa. Bayan ya ɗauki burodin nan bakwai, ya yi godiya, sai ya kakkarya, ya ba wa almajiransa su rarraba wa mutanen, suka kuwa yi haka.
And He ordered the people to sit down upon the ground: and taking the seven loaves, He gave thanks and brake them, and gave to his disciples to set before them; and they did set them before the multitude.
7 Suna kuma da ƙananan kifaye kaɗan, ya ba da godiya dominsu, ya kuma ce wa almajiran su rarraba musu.
And they had a few small fishes: and He blessed them, and bid them set them also before the people.
8 Mutanen suka ci, suka ƙoshi. Daga baya, almajiran suka tattara gutsattsarin da suka rage cike da kwanduna bakwai.
And they did eat and were satisfied: and they took up what were left, to wit of fragments seven baskets:
9 Wajen maza dubu huɗu ne suka kasance. Da ya sallame su,
and they that had eaten were about four thousand. And then He dismissed them.
10 sai ya shiga jirgin ruwa tare da almajiransa, suka tafi yankin Dalmanuta.
And going directly on board a ship with his disciples, He came into the parts of Dalmanutha:
11 Farisiyawa suka zo suka fara yin wa Yesu tambayoyi. Don su gwada shi, sai suka nemi yă nuna musu wata alama daga sama.
and the pharirisees came forth, and began to dispute with Him, desiring of Him a sign from heaven, tempting Him.
12 Sai ya ja numfashi mai zurfi ya ce, “Don me wannan zamani yake neman ganin abin banmamaki? Gaskiya nake gaya muku, ba wata alamar da za a ba su.”
And He sighing deeply in his spirit, saith, Why doth this generation require a sign? Verily I tell you, There shall no sign be given to this generation.
13 Sai ya bar su, ya koma cikin jirgin ruwan, suka ƙetare zuwa ɗaya hayin.
So He left them, and went on board the ship again, and departed to the other side.
14 Almajiran suka manta su riƙe burodi, sai dai guda ɗaya da suke da shi a cikin jirgin ruwan.
And his disciples had forgot to take bread, neither had they any more than one loaf with them in the ship.
15 Yesu ya gargaɗe su ya ce, “Ku yi hankali, ku kuma lura da yistin Farisiyawa da na Hiridus.”
And therefore as He was giving them a charge, saying, Take heed, beware of the leaven of the pharisees, and of the leaven of Herod,
16 Suka tattauna wannan da juna, suna cewa, “Don ba mu da burodi ne.”
they argued one with another, saying, It is because we have no bread.
17 Da ya gane abin da suke tattaunawa, sai Yesu ya tambaye su ya ce, “Don me kuke zancen rashin burodi? Har yanzu ba ku gane ko fahimta ba? Zukatanku sun taurare ne?
And Jesus knowing it saith unto them, What are ye reasoning about? because ye have no bread? Do ye not yet discern nor understand? have ye your heart still hardened?
18 Kuna da idanu, amma kun kāsa gani, kuna da kunnuwa, amma kun kāsa ji? Ba ku tuna ba?
Have ye eyes, and do not see? and having ears, hear ye not? and do ye not remember?
19 Da na kakkarya burodi guda biyar wa mutane dubu biyar, kwanduna nawa kuka kwashe cike da gutsattsarin?” Suka amsa, “Sha biyu.”
When I brake the five loaves among five thousand, how many baskets full of fragments did ye take up? They answer, Twelve.
20 “Da na kuma kakkarya burodin nan bakwai wa mutum dubu huɗu, kwanduna nawa kuka kwashe cike da gutsattsarin?” Suka ce, “Bakwai.”
And when I divided the seven among four thousand, how many baskets full of fragments took ye up? and they said, Seven.
21 Ya ce musu, “Har yanzu ba ku fahimta ba?”
And He said unto them, How is it then that ye do not understand?
22 Suka iso Betsaida, sai waɗansu mutane suka kawo wani makaho, suka roƙi Yesu yă taɓa shi.
Then He cometh to Bethsaida, where they brought to Him a blind man, and begged of Him that He would touch him.
23 Yesu ya kama hannun makahon ya kai shi bayan ƙauyen. Bayan ya tofa miyau a idanun mutumin, ya kuma ɗibiya masa hannuwansa, sai ya tambaye shi ya ce, “Kana iya ganin wani abu?”
And He took the blind man by the hand, and led him out of the town; and having spit on his eyes, He laid his hands upon him, and asked him, If he saw any thing.
24 Sai ya ɗaga kai ya ce, “Ina ganin mutane, suna kama da itatuwa da suke tafiya.”
And he looked up, and said, I see men (as it were trees) walking.
25 Yesu ya sāke ɗibiya hannuwansa a idanun mutumin, sai idanunsa suka buɗe, ya sami gani, ya kuma ga kome sarai.
Then He put his hands again upon his eyes, and made him look up: and he was restored to sight, and saw them all plainly.
26 Yesu ya sallame shi gida ya ce, “Kada ka shiga cikin ƙauyen.”
And He sent him away to his house, and said, Neither go into the town, nor tell any one in the town.
27 Yesu da almajiransa suka tafi ƙauyukan da suke kewaye da Kaisariya Filibbi. A hanya ya tambaye su ya ce, “Wa, mutane suke ce da ni?”
Then Jesus and his disciples went out into the towns of Cesarea Philippi: and by the way He asked his disciples, saying, Whom do men say that I am?
28 Suka amsa, suka ce, “Waɗansu suna cewa, Yohanna Mai Baftisma, waɗansu Iliya, waɗansu kuma har wa yau sun ce, ɗaya daga cikin annabawa.”
And they answered, Some say, John the baptist; and others, Elias; and others, One of the prophets.
29 Sai ya yi tambaya ya ce, “Amma ku fa, wa kuke ce da ni?” Bitrus ya amsa ya ce, “Kai ne Kiristi.”
And He saith unto them, But whom say ye that I am? Peter answered and saith, Thou art the Christ.
30 Yesu ya gargaɗe su kada su gaya wa kowa kome a kansa.
And He charged them, that they should say this to no one concerning Him:
31 Sai ya fara koya musu cewa, dole Ɗan Mutum yă sha wahaloli da yawa, dattawa, manyan firistoci da malaman dokoki kuma su ƙi shi. Dole kuma a kashe shi, bayan kwana uku kuma, yă tashi.
and began to tell them, that the Son of man must suffer much; and be rejected by the elders, and chief priests, and scribes; and be put to death: and after three days rise again.
32 Ya yi wannan zance a sarari. Sai Bitrus ya jawo shi gefe, ya fara tsawata masa.
And this He spake plainly and openly. Upon which Peter began to rebuke Him.
33 Amma da Yesu ya juya ya dubi almajiransa, sai ya tsawata wa Bitrus ya ce, “Tashi daga nan Shaiɗan! Ba ka da al’amuran Allah a zuciyarka, sai na mutane.”
But He turned about and looking on his disciples reproved Peter, saying, Get thee behind me Satan; for thou savourest not the things of God, but the things that be of men.
34 Sai ya kira taron wurinsa tare da almajiransa ya ce, “Duk wanda zai bi ni, dole yă ƙi kansa, yă ɗauki gicciyensa yă bi ni.
And calling the people and his disciples to Him, He said unto them, Whosoever is willing to come after me, let him deny himself, and take up his cross, and follow me:
35 Domin duk mai son ceton ransa zai rasa shi, amma duk wanda ya rasa ransa saboda ni, da kuma bishara, zai same shi.
for he that would save his life, shall lose it; but he that would lose his life for my sake and the gospel's, shall save it.
36 Me mutum zai amfana, in ya ribato duniya duka a bakin ransa?
For what shall it profit a man, if he gain the whole world, and lose his own soul?
37 Ko kuma, me mutum zai bayar a musayar ransa?
or what shall a man give as a ransom for his soul?
38 Duk wanda ya ji kunyata, da na kalmomina a wannan zamani na fasikanci da zunubi, Ɗan Mutum ma zai ji kunyarsa lokacin da ya shiga cikin ɗaukakar Ubansa, tare da tsarkakan mala’iku.”
for whosoever shall be ashamed of me, and of my words, in this degenerate and sinful age, of him will the Son of man be also ashamed, when He cometh in the glory of his Father, with the holy angels.