< Markus 8 >
1 A kwanakin nan wani taro mai girma ya taru. Tun da yake ba su da abin da za su ci, sai Yesu ya kira almajiransa ya ce,
About that time there was again an immense crowd, and they found themselves with nothing to eat. So He called His disciples to Him.
2 “Ina jin tausayin mutanen nan, kwanansu uku ke nan tare da ni, kuma ba su da abin da za su ci.
"My heart yearns over the people," He said; "for this is now the third day they have remained with me, and they have nothing to eat.
3 In na sallame su gida da yunwa, za su kāsa a hanya, don waɗansu daga cikinsu sun zo daga nesa.”
If I were to send them home hungry, they would faint on the way, some of them having come a great distance."
4 Almajiransa suka amsa suka ce, “Amma a ina, a wannan wurin da ba kowa, wani zai iya samun isashen burodi, don a ciyar da su?”
"Where can we possibly get bread here in this remote place to satisfy such a crowd?" answered His disciples.
5 Sai Yesu ya yi tambaya ya ce, “Burodi guda nawa kuke da su?” Suka ce, “Bakwai.”
"How many loaves have you?" He asked. "Seven," they said.
6 Sai ya gaya wa taron su zazzauna a ƙasa. Bayan ya ɗauki burodin nan bakwai, ya yi godiya, sai ya kakkarya, ya ba wa almajiransa su rarraba wa mutanen, suka kuwa yi haka.
So He passed the word to the people to sit down on the ground. Then taking the seven loaves He blessed them, and broke them into portions and proceeded to give them to His disciples for them to distribute, and they distributed them to the people.
7 Suna kuma da ƙananan kifaye kaɗan, ya ba da godiya dominsu, ya kuma ce wa almajiran su rarraba musu.
They had also a few small fish. He blessed them, and He told His disciples to distribute these also.
8 Mutanen suka ci, suka ƙoshi. Daga baya, almajiran suka tattara gutsattsarin da suka rage cike da kwanduna bakwai.
So the people ate an abundant meal; and what remained over they picked up and carried away--seven hampers of broken pieces.
9 Wajen maza dubu huɗu ne suka kasance. Da ya sallame su,
The number fed were about 4,000. Then He sent them away,
10 sai ya shiga jirgin ruwa tare da almajiransa, suka tafi yankin Dalmanuta.
and at once going on board with His disciples He came into the district of Dalmanutha.
11 Farisiyawa suka zo suka fara yin wa Yesu tambayoyi. Don su gwada shi, sai suka nemi yă nuna musu wata alama daga sama.
The Pharisees followed Him and began to dispute with Him, asking Him for a sign in the sky, to make trial of Him.
12 Sai ya ja numfashi mai zurfi ya ce, “Don me wannan zamani yake neman ganin abin banmamaki? Gaskiya nake gaya muku, ba wata alamar da za a ba su.”
Heaving a deep and troubled sigh, He said, "Why do the men of to-day ask for a sign? In solemn truth I tell you that no sign will be given to the men of to-day."
13 Sai ya bar su, ya koma cikin jirgin ruwan, suka ƙetare zuwa ɗaya hayin.
So He left them, went on board again, and came away to the other side.
14 Almajiran suka manta su riƙe burodi, sai dai guda ɗaya da suke da shi a cikin jirgin ruwan.
Now they had forgotten to take bread, nor had they more than a single loaf with them in the boat;
15 Yesu ya gargaɗe su ya ce, “Ku yi hankali, ku kuma lura da yistin Farisiyawa da na Hiridus.”
and when He admonished them, "See to it, be on your guard against the yeast of the Pharisees and the yeast of Herod,"
16 Suka tattauna wannan da juna, suna cewa, “Don ba mu da burodi ne.”
they explained His words to one another by saying, "We have no bread!"
17 Da ya gane abin da suke tattaunawa, sai Yesu ya tambaye su ya ce, “Don me kuke zancen rashin burodi? Har yanzu ba ku gane ko fahimta ba? Zukatanku sun taurare ne?
He perceived what they were saying, and He said to them, "What is this discussion of yours about having no bread? Do you not yet see and understand? Are your minds so dull of comprehension?
18 Kuna da idanu, amma kun kāsa gani, kuna da kunnuwa, amma kun kāsa ji? Ba ku tuna ba?
You have eyes! can you not see? You have ears! can you not hear? and have you no memory?
19 Da na kakkarya burodi guda biyar wa mutane dubu biyar, kwanduna nawa kuka kwashe cike da gutsattsarin?” Suka amsa, “Sha biyu.”
When I broke up the five loaves for the 5,000 men, how many baskets did you carry away full of broken portions?" "Twelve," they said.
20 “Da na kuma kakkarya burodin nan bakwai wa mutum dubu huɗu, kwanduna nawa kuka kwashe cike da gutsattsarin?” Suka ce, “Bakwai.”
"And when the seven for the 4,000, how many hampers full of portions did you take away?" "Seven," they answered.
21 Ya ce musu, “Har yanzu ba ku fahimta ba?”
"Do you not yet understand?" He said.
22 Suka iso Betsaida, sai waɗansu mutane suka kawo wani makaho, suka roƙi Yesu yă taɓa shi.
And they came to Bethsaida. And a blind man was brought to Jesus and they entreated Him to touch him.
23 Yesu ya kama hannun makahon ya kai shi bayan ƙauyen. Bayan ya tofa miyau a idanun mutumin, ya kuma ɗibiya masa hannuwansa, sai ya tambaye shi ya ce, “Kana iya ganin wani abu?”
So He took the blind man by the arm and brought him out of the village, and spitting into his eyes He put His hands on him and asked him, "Can you see anything?"
24 Sai ya ɗaga kai ya ce, “Ina ganin mutane, suna kama da itatuwa da suke tafiya.”
He looked up and said, "I can see the people: I see them like trees--only walking."
25 Yesu ya sāke ɗibiya hannuwansa a idanun mutumin, sai idanunsa suka buɗe, ya sami gani, ya kuma ga kome sarai.
Then for the second time He put His hands on the man's eyes, and the man, looking steadily, recovered his sight and saw everything distinctly.
26 Yesu ya sallame shi gida ya ce, “Kada ka shiga cikin ƙauyen.”
So He sent him home, and added, "Do not even go into the village."
27 Yesu da almajiransa suka tafi ƙauyukan da suke kewaye da Kaisariya Filibbi. A hanya ya tambaye su ya ce, “Wa, mutane suke ce da ni?”
From that place Jesus and His disciples went to the villages belonging to Caesarea Philippi. On the way He began to ask His disciples, "Who do people say that I am?"
28 Suka amsa, suka ce, “Waɗansu suna cewa, Yohanna Mai Baftisma, waɗansu Iliya, waɗansu kuma har wa yau sun ce, ɗaya daga cikin annabawa.”
"John the Baptist," they replied, "but others say Elijah, and others, that it is one of the Prophets."
29 Sai ya yi tambaya ya ce, “Amma ku fa, wa kuke ce da ni?” Bitrus ya amsa ya ce, “Kai ne Kiristi.”
Then He asked them pointedly, "But you yourselves, who do you say that I am?" "You are the Christ," answered Peter.
30 Yesu ya gargaɗe su kada su gaya wa kowa kome a kansa.
And He strictly forbad them to tell this about Him to any one.
31 Sai ya fara koya musu cewa, dole Ɗan Mutum yă sha wahaloli da yawa, dattawa, manyan firistoci da malaman dokoki kuma su ƙi shi. Dole kuma a kashe shi, bayan kwana uku kuma, yă tashi.
And now for the first time He told them, "The Son of Man must endure much suffering, and be rejected by the Elders and the High Priests and the Scribes, and be put to death, and after two days rise to life."
32 Ya yi wannan zance a sarari. Sai Bitrus ya jawo shi gefe, ya fara tsawata masa.
This He told them plainly; whereupon Peter took Him and began to remonstrate with Him.
33 Amma da Yesu ya juya ya dubi almajiransa, sai ya tsawata wa Bitrus ya ce, “Tashi daga nan Shaiɗan! Ba ka da al’amuran Allah a zuciyarka, sai na mutane.”
But turning round and seeing His disciples, He rebuked Peter. "Get behind me, Adversary," He said, "for your thoughts are not God's thoughts, but men's."
34 Sai ya kira taron wurinsa tare da almajiransa ya ce, “Duk wanda zai bi ni, dole yă ƙi kansa, yă ɗauki gicciyensa yă bi ni.
Then calling to Him the crowd and also His disciples, He said to them, "If any one is desirous of following me, let him ignore self and take up his cross, and so be my follower.
35 Domin duk mai son ceton ransa zai rasa shi, amma duk wanda ya rasa ransa saboda ni, da kuma bishara, zai same shi.
For whoever is bent on securing his life will lose it, but he who loses his life for my sake, and for the sake of the Good News, will secure it.
36 Me mutum zai amfana, in ya ribato duniya duka a bakin ransa?
Why, what does it benefit a man to gain the whole world and forfeit his life?
37 Ko kuma, me mutum zai bayar a musayar ransa?
For what could a man give to buy back his life?
38 Duk wanda ya ji kunyata, da na kalmomina a wannan zamani na fasikanci da zunubi, Ɗan Mutum ma zai ji kunyarsa lokacin da ya shiga cikin ɗaukakar Ubansa, tare da tsarkakan mala’iku.”
Every one, however, who has been ashamed of me and of my teachings in this faithless and sinful age, of him the Son of Man also will be ashamed when He comes in His Father's glory with the holy angels."