< Markus 8 >
1 A kwanakin nan wani taro mai girma ya taru. Tun da yake ba su da abin da za su ci, sai Yesu ya kira almajiransa ya ce,
In those dayes whe ther was a very greate companye and had nothinge to eate Iesus called his disciples to him and sayd vnto the:
2 “Ina jin tausayin mutanen nan, kwanansu uku ke nan tare da ni, kuma ba su da abin da za su ci.
I have copassion on this people because they have nowe bene with me. iii. dayes and have nothinge to eate:
3 In na sallame su gida da yunwa, za su kāsa a hanya, don waɗansu daga cikinsu sun zo daga nesa.”
And yf I shuld sende the awaye fastinge to their awne houses they shulde faynt by the waye. For dyvers of the came from farre.
4 Almajiransa suka amsa suka ce, “Amma a ina, a wannan wurin da ba kowa, wani zai iya samun isashen burodi, don a ciyar da su?”
And his disciples answered him: where shuld a man have breade here in the wildernes to satisfie these?
5 Sai Yesu ya yi tambaya ya ce, “Burodi guda nawa kuke da su?” Suka ce, “Bakwai.”
And he axed them: how many loves have ye? They sayde: seven.
6 Sai ya gaya wa taron su zazzauna a ƙasa. Bayan ya ɗauki burodin nan bakwai, ya yi godiya, sai ya kakkarya, ya ba wa almajiransa su rarraba wa mutanen, suka kuwa yi haka.
And he commaunded the people to syt doune on the grounde. And he toke the. vii. loves gave thankes brake and gave to his disciples to set before them. And they dyd set the before the people.
7 Suna kuma da ƙananan kifaye kaɗan, ya ba da godiya dominsu, ya kuma ce wa almajiran su rarraba musu.
And they had a feawe smale fysshes. And he blessed them and comaunded them also to be set before them.
8 Mutanen suka ci, suka ƙoshi. Daga baya, almajiran suka tattara gutsattsarin da suka rage cike da kwanduna bakwai.
And they ate and were suffysed: And they toke vp yf the broken meate that was lefte. vii. baskettes full.
9 Wajen maza dubu huɗu ne suka kasance. Da ya sallame su,
And they yt ate were in nomber aboute fowre thousand. And he sent them awaye.
10 sai ya shiga jirgin ruwa tare da almajiransa, suka tafi yankin Dalmanuta.
And a none he entred into a ship wt his disciples and came into the parties of Dalmanutha.
11 Farisiyawa suka zo suka fara yin wa Yesu tambayoyi. Don su gwada shi, sai suka nemi yă nuna musu wata alama daga sama.
And the pharises cam forth and begane to dispute with him sekinge of him a signe fro heven and temptinge him.
12 Sai ya ja numfashi mai zurfi ya ce, “Don me wannan zamani yake neman ganin abin banmamaki? Gaskiya nake gaya muku, ba wata alamar da za a ba su.”
And he sygthed in his sprete and sayde: why doth this generacion seke a signe? Verely I saye vnto you ther shall no signe be geven vnto this generacion.
13 Sai ya bar su, ya koma cikin jirgin ruwan, suka ƙetare zuwa ɗaya hayin.
And he lefte the and went into the ship agayne and departed over the water.
14 Almajiran suka manta su riƙe burodi, sai dai guda ɗaya da suke da shi a cikin jirgin ruwan.
And they had forgotte to take breed wt the nether had they in the ship with them more then one loofe.
15 Yesu ya gargaɗe su ya ce, “Ku yi hankali, ku kuma lura da yistin Farisiyawa da na Hiridus.”
And he charged the sayinge. Take hede and beware of ye leven of ye pharises and of ye leve of Herode.
16 Suka tattauna wannan da juna, suna cewa, “Don ba mu da burodi ne.”
And they reasoned amonge the selves sayinge: we have no breed
17 Da ya gane abin da suke tattaunawa, sai Yesu ya tambaye su ya ce, “Don me kuke zancen rashin burodi? Har yanzu ba ku gane ko fahimta ba? Zukatanku sun taurare ne?
And whe Iesus knewe yt he sayde vnto the: why take ye thought because ye have no bread? perceave ye not yet nether vnderstonde? Have ye youre hertes yet blynded?
18 Kuna da idanu, amma kun kāsa gani, kuna da kunnuwa, amma kun kāsa ji? Ba ku tuna ba?
Have ye eyes and se not? and have ye eares and heare not? Do ye not remember?
19 Da na kakkarya burodi guda biyar wa mutane dubu biyar, kwanduna nawa kuka kwashe cike da gutsattsarin?” Suka amsa, “Sha biyu.”
When I brake v. loves amonge. v. M. How many baskettes full of broke meate toke ye vp? They sayde vnto him twelve.
20 “Da na kuma kakkarya burodin nan bakwai wa mutum dubu huɗu, kwanduna nawa kuka kwashe cike da gutsattsarin?” Suka ce, “Bakwai.”
When I brake. vii. amonge. iiii. M. How many basketes of the levinges of broken meate toke ye vp? they sayde. vii.
21 Ya ce musu, “Har yanzu ba ku fahimta ba?”
And he sayde vnto the: how is it yt ye vnderstonde not?
22 Suka iso Betsaida, sai waɗansu mutane suka kawo wani makaho, suka roƙi Yesu yă taɓa shi.
And he came to Bethsaida and they brought a blynde man vnto him and desyred him to touche him.
23 Yesu ya kama hannun makahon ya kai shi bayan ƙauyen. Bayan ya tofa miyau a idanun mutumin, ya kuma ɗibiya masa hannuwansa, sai ya tambaye shi ya ce, “Kana iya ganin wani abu?”
And he caught the blynde by the honde and leade him out of the toune and spat in his eyes and put his hondes apon him and axed him whether he saw ought.
24 Sai ya ɗaga kai ya ce, “Ina ganin mutane, suna kama da itatuwa da suke tafiya.”
And he loked vp and sayde: I se ye men: For I se the walke as they were trees.
25 Yesu ya sāke ɗibiya hannuwansa a idanun mutumin, sai idanunsa suka buɗe, ya sami gani, ya kuma ga kome sarai.
After that he put his hondes agayne apon his eyes and made him see. And he was restored to his sight and sawe every ma clerly.
26 Yesu ya sallame shi gida ya ce, “Kada ka shiga cikin ƙauyen.”
And he sent him home to his housse sayinge: nether goo into the toune nor tell it to eny in the toune.
27 Yesu da almajiransa suka tafi ƙauyukan da suke kewaye da Kaisariya Filibbi. A hanya ya tambaye su ya ce, “Wa, mutane suke ce da ni?”
And Iesus went out and his disciples into the tounes that longe to the cite called Cesarea Philippi. Aud by the waye he axed his disciples sayinge: whom do men saye yt I am?
28 Suka amsa, suka ce, “Waɗansu suna cewa, Yohanna Mai Baftisma, waɗansu Iliya, waɗansu kuma har wa yau sun ce, ɗaya daga cikin annabawa.”
And they answered: some saye that thou arte Iohn Baptiste: some saye Helyas: and some one of the Prophetes.
29 Sai ya yi tambaya ya ce, “Amma ku fa, wa kuke ce da ni?” Bitrus ya amsa ya ce, “Kai ne Kiristi.”
And he sayde vnto the: But whom saye ye that I am? Peter answered and sayd vnto him: Thou arte very Christe.
30 Yesu ya gargaɗe su kada su gaya wa kowa kome a kansa.
And he charged them that they shuld tell no man of it.
31 Sai ya fara koya musu cewa, dole Ɗan Mutum yă sha wahaloli da yawa, dattawa, manyan firistoci da malaman dokoki kuma su ƙi shi. Dole kuma a kashe shi, bayan kwana uku kuma, yă tashi.
And he beganne to teache them how that the sonne of man must suffre many thinges and shuld be reproved of the elders and of the hye prestes and scribes and be kylled and after thre dayes aryse agayne.
32 Ya yi wannan zance a sarari. Sai Bitrus ya jawo shi gefe, ya fara tsawata masa.
And he spake that sayinge openly. And Peter toke him asyde and began to chyde him.
33 Amma da Yesu ya juya ya dubi almajiransa, sai ya tsawata wa Bitrus ya ce, “Tashi daga nan Shaiɗan! Ba ka da al’amuran Allah a zuciyarka, sai na mutane.”
Then he tourned aboute and looked on his disciples and rebuked Peter sayinge: Goo after me Satan. For thou saverest not ye thinges of God but the thinges of men.
34 Sai ya kira taron wurinsa tare da almajiransa ya ce, “Duk wanda zai bi ni, dole yă ƙi kansa, yă ɗauki gicciyensa yă bi ni.
And he called the people vnto him with his disciples also and sayd vnto them: Whosoever will folowe me let him forsake him sylfe and take vp his crosse and folowe me.
35 Domin duk mai son ceton ransa zai rasa shi, amma duk wanda ya rasa ransa saboda ni, da kuma bishara, zai same shi.
For whosoever will save his lyfe shall lose it But whosoever shall lose his lyfe for my sake and ye gospels ye same shall save it.
36 Me mutum zai amfana, in ya ribato duniya duka a bakin ransa?
What shall it profet a ma yf he shuld wynne all ye worlde and loose his awne soule?
37 Ko kuma, me mutum zai bayar a musayar ransa?
or els what shall a ma geve to redeme his soule agayne?
38 Duk wanda ya ji kunyata, da na kalmomina a wannan zamani na fasikanci da zunubi, Ɗan Mutum ma zai ji kunyarsa lokacin da ya shiga cikin ɗaukakar Ubansa, tare da tsarkakan mala’iku.”
Whosoever therfore shall be asshamed of me and of my wordes amonge this advoutrous and sinfull generacion: of him shall the sonne of man be ashamed when he cometh in the glory of his father wt the holy angels.