< Markus 7 >
1 Farisiyawa da waɗansu malaman dokoki waɗanda suka zo daga Urushalima, suka taru kewaye da Yesu.
And the Pharisees, and some of the scholars, having come from Jerusalem, gathered in to him.
2 Sai suka ga waɗansu daga cikin almajiransa suna cin abinci da hannuwa marasa tsabta, wato, da ba a wanke ba.
And having seen some of his disciples eating their loaves with profane hands, that is, unwashed, they accused them.
3 (Farisiyawa da dukan Yahudawa ba sa cin abinci, sai sun wanke hannuwa sarai tukuna, yadda al’adun dattawa suka ce.
(For the Pharisees, and all the Jews, unless they wash their hands carefully, do not eat, holding the tradition of the elders.
4 Sa’ad da suka dawo daga wurin kasuwanci, dole su wanke hannu kafin su ci abinci. Sukan kuma kiyaye waɗansu al’adu da yawa, kamar wanken kwafuna, tuluna da butoci.)
And coming from the marketplace, they do not eat unless they bathe. And there are many other things that they have taken in to retain: washings of cups, and pots, and brazen vessels, and beds.)
5 Saboda haka, Farisiyawa da malaman dokoki suka tambayi Yesu, suka ce, “Don me almajiranka ba sa bin al’adun dattawa, a maimakon haka suna cin abinci da hannuwa marasa tsabta?”
Then the Pharisees and the scholars demand of him, Why do thy disciples not walk according to the tradition of the elders, but eat their bread with unwashed hands?
6 Ya amsa ya ce, “Daidai ne Ishaya ya yi annabci game da ku munafukai; kamar yadda yake a rubuce cewa, “‘Waɗannan mutane da baki suke girmama ni, amma zukatansu sun yi nesa da ni.
And having answered, he said to them, Well did Isaiah prophesy about you hypocrites, as it is written, This people honors me with their lips, but their heart is far distant from me.
7 A banza suke mini sujada, koyarwarsu, dokokin mutane ne kawai.’
But in vain they worship me, teaching as doctrines the commandments of men.
8 Kun yar da umarnan Allah, kuna bin al’adun mutane.”
For having set aside the commandment of God, ye hold the tradition of men: washings of pots and cups and many other such like things ye do.
9 Ya kuma ce musu, “Kuna da hanya mai sauƙi na ajiye umarnan Allah a gefe ɗaya, don ku kiyaye al’adunku!
And he said to them, Well do ye reject the commandment of God, so that ye may keep your tradition.
10 Gama Musa ya ce, ‘Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka,’kuma, ‘Duk wanda ya zagi mahaifinsa ko mahaifiyarsa, dole a kashe shi.’
For Moses said, Honor thy father and thy mother, and, He who speaks evil of father or mother, let him perish in death.
11 Amma ku, kukan ce, in mutum ya ce wa mahaifinsa, ko mahaifiyarsa, ‘Duk taimakon da ya kamata ku samu daga wurina, Korban ne,’ (wato, abin da aka keɓe wa Allah),
But ye say, If a man should say to his father or mother, Whatever ye might be benefited from me is Corban, that is, an offering,
12 sa’an nan haka ba kwa ƙara barinsa yă yi wa mahaifinsa ko mahaifiyarsa wani abu.
then ye no longer allow him to do anything for his father or his mother,
13 Ta haka kuke rushe maganar Allah ta wurin al’adun da kuke miƙa wa’ya’yanku. Haka kuma kuke yin abubuwa da yawa.”
annulling the word of God by your tradition that ye have delivered. And many such like things ye do.
14 Sai Yesu ya sāke kiran taron wurinsa ya ce, “Ku saurare ni dukanku, ku kuma fahimci wannan.
And having summoned all the people, he said to them, Hear me all of you, and understand.
15 Ba abin da yake shiga mutum daga waje ba ne yake ƙazantar da shi. Sai dai abin da ya fita daga cikin mutum ne, yake ƙazantar da shi.”
There is nothing outside the man, entering into him that can defile him, but the things coming out of him those are the things that defile the man.
If any man has ears to hear, let him hear.
17 Bayan ya bar taron, ya shiga gida, sai almajiransa suka tambaye shi ma’anar wannan misali.
And when he entered into a house from the crowd, his disciples questioned him about the parable.
18 Ya ce, “Ashe, ba ku da saurin ganewa? Ba ku gane cewa ba abin da yake shiga mutum daga waje ba ne yake ƙazantar da shi.
And he says to them, Are also ye so without understanding? Do ye not perceive that everything outside that enters into the man cannot defile him,
19 Gama ba ya shiga cikin zuciyarsa, sai dai cikin tumbinsa, sa’an nan kuma yă fita daga jikinsa.” (Da faɗin haka, Yesu ya nuna tsabtar kowane irin abinci.)
because it does not enter into his heart, but into the belly, and goes out into the toilet (making all foods clean)?
20 Ya ci gaba, “Abin da yake fitowa daga mutum ne yake ƙazantar da shi.
And he said, That which comes out of the man, that defiles the man.
21 Gama daga ciki, daga zuciyar mutane, mugayen tunani suke fitowa, fasikanci, sata, kisankai, zina,
For from inside the heart of men proceed evil thoughts, adulteries, fornications, murders, thefts,
22 kwaɗayi, ƙeta, ruɗu, ƙazantaccen sha’awa, kishi, ɓata suna, girman kai da kuma wauta.
covetings, wickednesses, deceit, licentiousness, an evil eye, reviling, pride, foolishness.
23 Duk waɗannan mugayen abubuwa daga cikin suke fitowa, suna kuma ƙazantar da mutum.”
All these evil things come from inside, and defile the man.
24 Sai Yesu ya bar wurin, ya kuma tafi wajajen Taya. Ya shiga wani gida, bai kuwa so kowa yă sani ba. Duk da haka, bai iya ɓoye kasancewarsa ba.
And having risen from there, he went away into the borders of Tyre and Sidon. And having entered into a house, he wanted no man to know it, and yet he could not be hid.
25 Da jin labarinsa, sai wata mace wadda ƙaramar diyarta tana da mugun ruhu, ta zo ta durƙusa a gabansa.
For a woman whose little daughter had an unclean spirit, after hearing about him, having come, she fell down at his feet.
26 Macen kuwa mutuniyar Hellenawa ce, an haife ta a Funisiya a Suriya. Ta roƙi Yesu yă fitar da aljani da yake jikin diyarta.
Now the woman was a Greek, a Syrophoenician by race. And she besought him that he would cast out the demon from her daughter.
27 Yesu ya ce mata, “Da farko, bari’ya’ya su ci su ƙoshi tukuna, gama ba daidai ba ne, a ɗauki burodin yara a jefa wa karnukansu.”
And Jesus said to her, Allow the children first be filled, for it is not right to take the children's bread and cast it to the house dogs.
28 Ta amsa, ta ce, “I, Ubangiji, ko karnuka ma da suke ƙarƙashin tebur, sukan ci burbuɗin da suke fāɗuwa daga abincin yara.”
But she answered and says to him, Yes, Lord, for even the house dogs under the table eat of the children's crumbs.
29 Sai ya ce mata, “Saboda irin wannan amsa, ki tafi, aljanin ya rabu da diyarki.”
And he said to her, Because of this saying, go thou. The demon has gone out of thy daughter.
30 Ta tafi gida, ta tarar da diyarta kwance a gado, aljanin kuwa ya fita.
And having departed to her house, she found the demon having gone out, and her daughter laid upon the bed.
31 Sai Yesu ya bar wajajen Taya, ya bi ta Sidon har zuwa Tekun Galili da kuma cikin yankin Dekafolis.
And again having departed from the borders of Tyre and Sidon, he came to the sea of Galilee in the midst of the regions of Decapolis.
32 A can ne waɗansu mutane suka kawo masa wani kurma, wanda da ƙyar yake magana. Sai suka roƙe shi yă ɗibiya hannunsa a kan mutumin.
And they bring a deaf, tongue-tied man to him, and they beseech him to lay his hand upon him.
33 Bayan da ya jawo shi gefe, sai Yesu ya sa yatsotsinsa a kunnuwan mutumin, ya tofa miyau ya kuma taɓa harshen mutumin.
And having taken him from the multitude in private, he put his fingers into his ears, and having spat, he touched his tongue.
34 Ya ɗaga kai sama, ya ja numfashi mai zurfi, sa’an nan ya ce masa, “Effata!” (Wato, “Buɗe!”).
And having looked up to heaven, he sighed, and says to him, Ephphatha, that is, Be opened.
35 Bayan ya faɗa haka, sai kunnuwan mutumin suka buɗe, harshensa kuma ya kunce, sai ya fara magana sarai.
And straightaway his ears were opened, and the bond of his tongue was loosened, and he spoke plainly.
36 Yesu ya umarce su, kada su gaya wa kowa. Amma ƙara yawan kwaɓarsu ƙara yawan yaɗa labarin suke ta yi.
And he commanded them that they should tell no man, but as much as he commanded them, so much the more abundantly they proclaimed it.
37 Mutane suka cika da mamaki, suka ce, “Kai, ya yi kome daidai. Har ma yana sa kurame su ji, bebaye kuma su yi magana.”
And they were exceedingly astonished, saying, He has done all things well. He even makes the deaf to hear, and the mute to speak.