< Markus 7 >

1 Farisiyawa da waɗansu malaman dokoki waɗanda suka zo daga Urushalima, suka taru kewaye da Yesu.
Og Farisæerne og nogle af de skriftkloge, som vare komne fra Jerusalem, samle sig om ham.
2 Sai suka ga waɗansu daga cikin almajiransa suna cin abinci da hannuwa marasa tsabta, wato, da ba a wanke ba.
Og da de så nogle af hans Disciple holde Måltid med vanhellige, det er utoede, Hænder
3 (Farisiyawa da dukan Yahudawa ba sa cin abinci, sai sun wanke hannuwa sarai tukuna, yadda al’adun dattawa suka ce.
thi Farisæerne og alle Jøderne spise ikke uden at to Hænderne omhyggeligt, idet de fastholde de gamles Overlevering;
4 Sa’ad da suka dawo daga wurin kasuwanci, dole su wanke hannu kafin su ci abinci. Sukan kuma kiyaye waɗansu al’adu da yawa, kamar wanken kwafuna, tuluna da butoci.)
og når de komme fra Torvet, spise de ikke uden først at tvætte sig; og der er mange andre Ting, som de have vedtaget at holde, Tvætninger af Bægere og Krus og Kobberkar og Bænke,
5 Saboda haka, Farisiyawa da malaman dokoki suka tambayi Yesu, suka ce, “Don me almajiranka ba sa bin al’adun dattawa, a maimakon haka suna cin abinci da hannuwa marasa tsabta?”
så spurgte Farisæerne og de skriftkloge ham ad: "Hvorfor vandre dine Disciple ikke efter de gamles Overlevering, men holde Måltid med vanhellige Hænder?"
6 Ya amsa ya ce, “Daidai ne Ishaya ya yi annabci game da ku munafukai; kamar yadda yake a rubuce cewa, “‘Waɗannan mutane da baki suke girmama ni, amma zukatansu sun yi nesa da ni.
Men han sagde til dem: "Rettelig profeterede Esajas om eder, I Hyklere! som der er skrevet: "Dette Folk ærer mig med Læberne, men deres Hjerte er langt borte fra mig.
7 A banza suke mini sujada, koyarwarsu, dokokin mutane ne kawai.’
Men de dyrke mig forgæves, idet de lære Lærdomme, som ere Menneskers Bud."
8 Kun yar da umarnan Allah, kuna bin al’adun mutane.”
I forlade Guds Bud og holde Menneskers Overlevering."
9 Ya kuma ce musu, “Kuna da hanya mai sauƙi na ajiye umarnan Allah a gefe ɗaya, don ku kiyaye al’adunku!
Og han sagde til dem: "Smukt ophæve I Guds Bud, for at I kunne holde eders Overlevering.
10 Gama Musa ya ce, ‘Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka,’kuma, ‘Duk wanda ya zagi mahaifinsa ko mahaifiyarsa, dole a kashe shi.’
Thi Moses har sagt: "Ær din Fader og din Moder"; og:"Den, som hader Fader eller Moder, skal visselig dø".
11 Amma ku, kukan ce, in mutum ya ce wa mahaifinsa, ko mahaifiyarsa, ‘Duk taimakon da ya kamata ku samu daga wurina, Korban ne,’ (wato, abin da aka keɓe wa Allah),
Men I sige: Når en Mand siger til sin Fader eller sin Moder: "Det, hvormed du skulde være hjulpen af mig, skal være Korban (det er: Tempelgave),"
12 sa’an nan haka ba kwa ƙara barinsa yă yi wa mahaifinsa ko mahaifiyarsa wani abu.
da tilstede I ham ikke mere at gøre noget for sin Fader eller Moder,
13 Ta haka kuke rushe maganar Allah ta wurin al’adun da kuke miƙa wa’ya’yanku. Haka kuma kuke yin abubuwa da yawa.”
idet I ophæve Guds Ord ved eders Overlevering, som I have overleveret; og mange lignende Ting gøre I."
14 Sai Yesu ya sāke kiran taron wurinsa ya ce, “Ku saurare ni dukanku, ku kuma fahimci wannan.
Og han kaldte atter Folkeskaren til sig og sagde til dem: "Hører mig alle, og forstår!
15 Ba abin da yake shiga mutum daga waje ba ne yake ƙazantar da shi. Sai dai abin da ya fita daga cikin mutum ne, yake ƙazantar da shi.”
Der er intet uden for Mennesket, som, når det går ind i ham, kan gøre ham uren; men hvad der går ud af Mennesket, det er det, som gør Mennesket urent.
Dersom nogen har Øren at høre med, han høre!"
17 Bayan ya bar taron, ya shiga gida, sai almajiransa suka tambaye shi ma’anar wannan misali.
Og da han var gået ind i Huset og var borte fra Skaren, spurgte hans Disciple ham om Lignelsen.
18 Ya ce, “Ashe, ba ku da saurin ganewa? Ba ku gane cewa ba abin da yake shiga mutum daga waje ba ne yake ƙazantar da shi.
Og han siger til dem: "Ere også I så uforstandige? Forstå I ikke, at intet, som udefra går ind i Mennesket, kan gøre ham uren?
19 Gama ba ya shiga cikin zuciyarsa, sai dai cikin tumbinsa, sa’an nan kuma yă fita daga jikinsa.” (Da faɗin haka, Yesu ya nuna tsabtar kowane irin abinci.)
Thi det går ikke ind i hans Hjerte men i hans Bug og går ud ad den naturlige Vej, og således renses al Maden."
20 Ya ci gaba, “Abin da yake fitowa daga mutum ne yake ƙazantar da shi.
Men han sagde: "Det, som går ud af Mennesket, dette gør Mennesket urent.
21 Gama daga ciki, daga zuciyar mutane, mugayen tunani suke fitowa, fasikanci, sata, kisankai, zina,
Thi indvortes fra, fra Menneskenes Hjerte, udgå de onde Tanker, Utugt, Tyveri, Mord,
22 kwaɗayi, ƙeta, ruɗu, ƙazantaccen sha’awa, kishi, ɓata suna, girman kai da kuma wauta.
Hor, Havesyge, Ondskab, Svig, Uterlighed, et ondt Øje, Forhånelse, Hovmod, Fremfusenhed;
23 Duk waɗannan mugayen abubuwa daga cikin suke fitowa, suna kuma ƙazantar da mutum.”
alle disse onde Ting udgå indvortes fra og gøre Mennesket urent."
24 Sai Yesu ya bar wurin, ya kuma tafi wajajen Taya. Ya shiga wani gida, bai kuwa so kowa yă sani ba. Duk da haka, bai iya ɓoye kasancewarsa ba.
Og han stod op og gik bort derfra til Tyrus's og Sidons Egne. Og han gik ind i et Hus og vilde ikke, at nogen skulde vide det. Og han kunde dog ikke være skjult;
25 Da jin labarinsa, sai wata mace wadda ƙaramar diyarta tana da mugun ruhu, ta zo ta durƙusa a gabansa.
men en Kvinde, hvis lille Datter havde en uren Ånd, havde hørt om ham og kom straks ind og faldt ned for hans Fødder;
26 Macen kuwa mutuniyar Hellenawa ce, an haife ta a Funisiya a Suriya. Ta roƙi Yesu yă fitar da aljani da yake jikin diyarta.
(men Kvinden var græsk, af Herkomst en Syrofønikerinde), og hun bad ham om, at han vilde uddrive den onde Ånd af hendes Datter.
27 Yesu ya ce mata, “Da farko, bari’ya’ya su ci su ƙoshi tukuna, gama ba daidai ba ne, a ɗauki burodin yara a jefa wa karnukansu.”
Og han sagde til hende: "Lad først Børnene mættes; thi det er ikke smukt at tage Børnenes Brød og kaste det for de små Hunde."
28 Ta amsa, ta ce, “I, Ubangiji, ko karnuka ma da suke ƙarƙashin tebur, sukan ci burbuɗin da suke fāɗuwa daga abincin yara.”
Men hun svarede og siger til ham: "Jo, Herre! også de små Hunde æde under Bordet af Børnenes Smuler."
29 Sai ya ce mata, “Saboda irin wannan amsa, ki tafi, aljanin ya rabu da diyarki.”
Og han sagde til hende: "For dette Ords Skyld gå bort; den onde Ånd er udfaren af din Datter"
30 Ta tafi gida, ta tarar da diyarta kwance a gado, aljanin kuwa ya fita.
Og hun gik bort til sit Hus og fandt Barnet liggende på Sengen og den onde Ånd udfaren.
31 Sai Yesu ya bar wajajen Taya, ya bi ta Sidon har zuwa Tekun Galili da kuma cikin yankin Dekafolis.
Og da han gik bort igen fra Tyrus's Egne, kom han over Sidon midt igennem Dekapolis's Egne til Galilæas Sø.
32 A can ne waɗansu mutane suka kawo masa wani kurma, wanda da ƙyar yake magana. Sai suka roƙe shi yă ɗibiya hannunsa a kan mutumin.
Og de bringe ham en døv, som også vanskeligt kunde tale, og bede ham om, at han vilde lægge Hånden på ham.
33 Bayan da ya jawo shi gefe, sai Yesu ya sa yatsotsinsa a kunnuwan mutumin, ya tofa miyau ya kuma taɓa harshen mutumin.
Og han tog ham afsides fra Skaren og lagde sine Fingre i hans Øren og spyttede og rørte ved hans Tunge
34 Ya ɗaga kai sama, ya ja numfashi mai zurfi, sa’an nan ya ce masa, “Effata!” (Wato, “Buɗe!”).
og så op til Himmelen, sukkede og sagde til ham: "Effata!" det er: lad dig op!
35 Bayan ya faɗa haka, sai kunnuwan mutumin suka buɗe, harshensa kuma ya kunce, sai ya fara magana sarai.
Og hans Øren åbnedes, og straks løstes hans Tunges Bånd, og han talte ret.
36 Yesu ya umarce su, kada su gaya wa kowa. Amma ƙara yawan kwaɓarsu ƙara yawan yaɗa labarin suke ta yi.
Og han bød dem, at de ikke måtte sige det til nogen; men jo mere han bød dem, desto mere kundgjorde de det.
37 Mutane suka cika da mamaki, suka ce, “Kai, ya yi kome daidai. Har ma yana sa kurame su ji, bebaye kuma su yi magana.”
Og de bleve over al Måde slagne af Forundring og sagde: "Han har gjort alle Ting vel; både gør han, at de døve høre, og at målløse tale."

< Markus 7 >