< Markus 6 >
1 Yesu ya tashi daga can ya tafi garinsa, tare da almajiransa.
And he went forth from thence, and cometh into his own city, —and his disciples follow him.
2 Da Asabbaci ya kewayo, sai ya fara koyarwa a cikin majami’a, mutane da yawa da suka saurare shi, suka yi mamaki. Suna tambaya, “Ina mutumin nan ya sami waɗannan abubuwa? Wace hikima ce wannan da aka ba shi, har da yana yin ayyukan banmamaki haka!
And, when it was Sabbath, he began to be teaching in the synagogue, and, the greater part, as they heard, were being struck with astonishment, saying—Whence hath this man these things?—and—What the wisdom which hath been given to this man?—and—Such mighty works as these, through his hands, are coming to pass!
3 Ashe, wannan ba shi ne kafinta nan ba? Shin, ba shi ne ɗan Maryamu ba, ba shi ne ɗan’uwan su Yaƙub, Yusuf, Yahuda da kuma Siman ba? Ashe,’yan’uwansa mata kuma ba suna nan tare da mu ba?” Sai suka ji haushinsa.
Is not, this, the carpenter? the son of Mary, the brother of James and Joses and Judas and Simon? And are not his sisters here with us?—and they were finding cause of stumbling in him.
4 Yesu ya ce musu, “Sai a garinsa kaɗai, da kuma cikin’yan’uwansa, da cikin gidansa ne, annabi ba shi da daraja.”
And Jesus was saying unto them—A prophet is not without honour, save in his own city and among his kinsfolk, and in his house;
5 Bai iya yin ayyukan banmamaki a wurin ba, sai dai ɗibiya hannuwansa da ya yi a kan mutane kima da suke da cututtuka, ya kuwa warkar da su.
and he could not, there, do so much as a single mighty work, —save, on a few sick, he laid his hands and cured them.
6 Ya kuwa yi mamaki ƙwarai don rashin bangaskiyarsu. Sai ya Yesu zazzaga ƙauyuka yana koyarwa.
And he marvelled because of their unbelief. And he was going round the villages in a circuit, teaching.
7 Ya kira Sha Biyun nan wurinsa, ya aike su biyu-biyu, ya kuma ba su iko bisa mugayen ruhohi.
And he calleth near the twelve, and began to be sending them forth two and two, —and was giving them authority over the impure spirits:
8 Ga dai umarnansa, “Kada ku ɗauki kome don tafiyar, sai dai sanda ba burodi, ba jaka, ba kuɗi a ɗamararku.
and charged them that they should take, nothing, for a journey, save a staff only, —no bread, no satchel, no copper, for the belt;
9 Ku sa takalma, amma ban da riga fiye da waɗanda kuka sa.
but having bound on light sandals, and not to put on, two tunics;
10 Duk sa’ad da kuka shiga wani gida, ku zauna nan sai kun bar garin.
and he was saying unto them—Wheresoever ye shall enter into a house, there, abide, until ye go forth from thence;
11 In kuwa a wani wuri ba a karɓe ku, ba a kuwa saurare ku ba, sai ku karkaɗe ƙurar ƙafafunku sa’ad da kuka fita, a matsayin shaida a kansu.”
And, whatsoever place shall not welcome you nor hearken unto you, when ye are going forth from thence, shake off the dust that is under you feet, for a witness against them.
12 Suka fita, suna yi wa’azi, suna ce wa mutane su tuba.
And they went forth and made proclamation, in order that men should repent;
13 Suka fitar da aljanu da yawa, suka shafa wa marasa lafiya da yawa mai, suka kuwa warkar da su.
and, many demons, were they casting out, —and were anointing with oil, many sick, and were curing them.
14 Sarki Hiridus ya ji wannan labari, gama sunan Yesu ya bazu a ko’ina. Waɗansu suna cewa, “An tashe Yohanna Mai Baftisma daga matattu ne, shi ya sa yana da ikon yin ayyukan banmamakin nan.”
And King Herod heard, —for, famous, had become his name; and he was saying—John the Immerser hath arisen from among the dead, and, for this cause, are the powers working mightily in him;
15 Waɗansu suka ce, “Ai, Iliya ne.” Har wa yau waɗansu suka ce, “Ai, annabi ne, kamar ɗaya daga cikin annabawan dā.”
But, others, were saying—It is Elijah, and, others were saying—A prophet, like one of the prophets!
16 Amma da Hiridus ya ji haka, sai ya ce, “Ai, Yohanna ne, mutumin da na yanke masa kai, shi ne ya tashi daga matattu!”
But, when Herod heard, he was saying—He whom I beheaded—John, the same, hath been raised.
17 Gama Hiridus da kansa ya ba da umarni a kama Yohanna, ya kuma sa aka daure shi, aka sa shi a kurkuku. Ya yi haka saboda Hiridiyas, matar ɗan’uwansa Filibus, wadda ya aura.
For, Herod himself, had sent and secured John and bound him in prison, for the sake of Herodias the wife of Philip his brother, —for, her, had he married,
18 Gama Yohanna ya yi ta ce wa Hiridus, “Ba daidai ba ne bisa ga doka, ka ɗauki matar ɗan’uwanka.”
For John had been saying to Herod—It is not allowed thee, to have, the wife of thy brother.
19 Saboda haka, Hiridiyas ta ƙulla munafunci game da Yohanna, ta kuma so ta kashe shi. Amma ba tă iya ba,
And, Herodias, was cherishing [a grudge] against him, and wishing, to slay him, —and could not;
20 domin Hiridus yana jin tsoron Yohanna, ya kuma kāre shi sosai, da sanin cewa shi mutum ne mai adalci da kuma mai tsarki. Duk sa’ad da Hiridus ya saurari Yohanna, yakan damu ƙwarai, duk da haka, yakan so yă ji shi.
for, Herod, stood in fear of John, knowing him to be a man righteous and holy, —and was keeping him safe; and, when he heard him, he paid earnest heed, and, with pleasure, used to listen to him.
21 A ƙarshe, ta sami zarafi. A ranar murnar haihuwar Hiridus, ya yi biki domin hakimansa, da shugabannin sojojinsa, da kuma manyan mutanen Galili.
And, an opportune day arriving, when Herod on his birthday made a feast for his nobles, and for the rulers of thousands and for the first men of Galilee,
22 Sa’ad da diyar Hiridiyas ta shigo, ta kuma yi rawa, sai ta gamshi Hiridus tare da baƙinsa. Sai Sarkin ya ce wa yarinyar, “Ki tambaye ni kome da kike so, ni kuwa zan ba ki.”
when the daughter of this very Herodias came in and danced, she pleased Herod and those reclining together, and, the king, said unto the damsel—Ask me what thou wilt, and I will give it thee;
23 Ya yi mata alkawari da rantsuwa cewa, “Duk abin da kika roƙa, zan ba ki, ko da rabin mulkina ne.”
and he took an oath to her—Whatsoever thou shalt ask me, I will give thee, unto half my kingdom.
24 Sai ta fita ta ce wa mahaifiyarta, “Me zan roƙa?” Ta ce, “Kan Yohanna Mai Baftisma.”
And, going out, she said unto her mother—What shall I ask? and she said—The head of John the Immerser;
25 Nan da nan, sai yarinyar ta yi hanzari zuwa wajen sarki da roƙon, “Ina so ka ba ni kan Yohanna Mai Baftisma a cikin tasa, yanzu-yanzu nan.”
And, coming in straightway, with hast, unto the king, she asked, saying—I desire, that, forthwith, thou give me, upon a charger, the head of John the Immerser.
26 Sai sarki ya yi baƙin ciki ƙwarai, amma saboda rantsuwar da kuma baƙinsa, bai so yă hana ta ba.
And, though the king was, very grieved, yet, by reason of the oaths, and of them who were reclining, he would not refuse her.
27 Nan take, sai ya aiki mai aiwatar da kisa da umarni ya kawo kan Yohanna. Mutumin ya je ya yanke kan Yohanna a kurkuku.
And the king, straightway, sending off a guard, gave orders to bring his head.
28 Ya kuma kawo kan a tasa ya ba yarinyar. Ita kuma ta ba wa mahaifiyarta.
And, departing, he beheaded him in the prison, and brought his head upon a charger, and gave it unto the damsel—and, the damsel, gave it unto her mother.
29 Da almajiran Yohanna suka sami labari, sai suka zo suka ɗauki jikinsa suka binne a kabari.
And, hearing of it, his disciples went and took away his corpse, and laid it in a tomb.
30 Manzannin suka taru kewaye da Yesu, suka ba shi rahoton duk abin da suka yi, da kuma suka koyar.
And the apostles gather themselves together unto Jesus, and reported unto him all things, as many as they had done, and as many as they had taught.
31 To, saboda mutane da yawa suna kai da kawowa, har ma ba su sami damar cin abinci ba, sai ya ce musu, “Ku zo mu kaɗaita inda ba kowa don ku ɗan huta.”
And he saith unto them—Come, ye yourselves, apart, into a desert place, and rest yourselves a little. For they who were coming and they who were going were many, and, not even to eat, were they finding fitting opportunity.
32 Sai suka tafi a jirgin ruwa su kaɗai, inda ba kowa.
And they departed, in the boat, into a desert place, apart.
33 Amma mutane da yawa waɗanda suka ga tashinsu, sun gane su, sai suka ruga da gudu a ƙafa daga dukan birane, suka riga su kaiwa can.
And many saw them going away, and took note of it, and, afoot, from all the cities, ran they together thither, —and outwent them.
34 Da Yesu ya sauka, ya ga taro mai yawa, sai ya ji tausayinsu, gama kamar tumaki suke waɗanda ba su da makiyayi. Sai ya fara koya musu abubuwa da yawa.
And, coming forth, he saw, a great multitude, and was moved with compassion towards them, because they were like sheep having no shepherd, and he began to be teaching them many things.
35 A lokacin nan yamma ta yi, sai almajiransa suka zo wurinsa suka ce masa, “Wurin nan ƙauye ne, ga shi kuma lokaci ya ƙure.
And, already, a late hour, having arrived, his disciples came unto him and were saying, A desert, is the place, and it is, already, a late hour:
36 Ka sallami mutanen su shiga ƙauyukan da suke kurkusa, su sayi wa kansu wani abu, su ci.”
dismiss them, that, departing into the surrounding hamlets and villages, they may buy themselves something to eat.
37 Sai ya amsa ya ce, “Ku, ku ba su wani abu su ci.” Suka ce masa, “Ai, wannan zai ɗauki albashin wata takwas na mutum! Mu je mu kashe yawan kuɗin nan a burodi mu ba su su ci?”
But, he, answering said to them—Ye, give them, to eat. And they say unto him—Shall we depart and buy two hundred denaries’ worth of loaves, and give them to eat?
38 Sai ya yi tambaya ya ce, “Burodi nawa kuke da su? Je ku duba.” Da suka duba, sai suka ce, “Biyar da kifi biyu.”
And, he, saith unto them—How many loaves, have ye? Go, see! And, getting to know, they say—Five, and, two fishes.
39 Sa’an nan Yesu ya umarce su su sa dukan mutanen su zazzauna ƙungiya-ƙungiya a kan ɗanyar ciyawa.
And he gave them orders, that all should be made recline, in parties, upon, the green grass.
40 Haka suka zazzauna a ƙungiyar ɗari-ɗari, da kuma hamsin-hamsin.
And they fell back, in companies, by hundreds and by fifties.
41 Ya ɗauki burodi guda biyar da kifin nan biyu, ya ɗaga kai sama, ya yi godiya, ya kakkarya burodin. Sai ya ba wa almajiransa su rarraba wa mutane. Ya kuma rarraba kifi biyun a tsakaninsu duka.
And, taking the five loaves, and the two fishes, looking up into heaven, he blessed, and brake up the loaves, and began giving unto the disciples, that they might set before them, and, the two fishes, divided he, unto all.
And they did all eat, and were filled.
43 almajiran suka kwashe gutsattsarin burodin da na kifin cike da kwanduna goma sha biyu.
And they took up broken pieces, twelve baskets, full measure, and from the fishes.
44 Yawan mutanen da suka ci kuwa maza dubu biyar ne.
And they who did eat the loaves were, five thousand men.
45 Nan da nan Yesu ya sa almajiransa su shiga jirgin ruwa, su sha gabansa zuwa Betsaida, shi kuma yă sallami taron.
And, straightway, constrained he his disciples to enter into the boat, and be going forward to the other side, unto Bethsaida, —while, he, was dismissing the multitude.
46 Bayan ya bar su, sai ya hau kan dutse don yă yi addu’a.
And, bidding them farewell, he departed into the mountain to pray.
47 Da yamma ta yi, jirgin ruwan yana tsakiyar tafkin, Yesu kuma yana can a ƙasa shi kaɗai.
And, when, evening, came, the boat was in the midst of the sea, and, he alone, on the land.
48 Ya ga almajiran suna fama da tuƙi saboda iska tana gāba da su. Wajen tsara ta huɗu na dare, sai ya tafi wurinsu, yana takawa a kan tafkin. Ya yi kamar zai wuce su,
And, seeing them distressed in the rowing, for the wind was against them, about the fourth watch of the night, he cometh unto them, walking upon the sea, —and was wishing to pass by them.
49 amma da suka gan shi yana takawa a kan tafkin, sai suka yi tsammani fatalwa ce. Sai suka yi ihu,
But, they, seeing him, upon the sea, walking, supposed that it was an apparition, and cried out aloud;
50 domin dukansu sun gan shi, suka kuma tsorata. Nan da nan ya yi magana da su ya ce, “Ku yi ƙarfin hali! Ni ne. Kada ku ji tsoro.”
for, all, saw him, and were troubled. But, he, straightway, talked with them, and saith unto them—Take courage! it is, I—be not afraid!
51 Sai ya shiga jirgin ruwan tare da su, iskar kuma ta kwanta. Dukansu suka yi mamaki,
And he went up unto them, into the boat, —and the wind lulled. And, exceedingly, within themselves, were they astonished;
52 gama ba su fahimci al’amarin burodin nan ba, don zuciyarsu ta taurare.
for they understood not by the loaves, —but their, heart, had been, hardened.
53 Da suka haye, sai suka sauka a Gennesaret, suka daure jirgin a ƙugiya.
And crossing over unto the land, they came unto Gennesaret, and cast anchor near.
54 Da fitowarsu daga jirgin, sai mutane suka gane Yesu.
And, when they had, come forth, out of the boat, straightway, recognizing him,
55 Suka gama yankin da gudu, suna ɗaukan marasa lafiya a kan tabarmai zuwa duk inda suka ji yake.
the people ran round the whole of that country, and began to be carrying round, upon couches, them who were sick, wherever they heard that he was.
56 Duk inda ya shiga, cikin ƙauyuka, birane ko karkara, sai su kwantar da marasa lafiya a bakin kasuwa. Suka roƙe shi yă bari su taɓa gefen rigarsa kawai, kuma duk waɗanda suka taɓa shi kuwa, suka warke.
And, wheresoever he was entering into villages, or into cities, or into hamlets, in the marketplaces, laid they the sick, and were beseeching him, that, only the fringe of his mantle, they might touch, and, as many soever as touched it, were being made well.