< Markus 6 >
1 Yesu ya tashi daga can ya tafi garinsa, tare da almajiransa.
And he went out thence and came to his own country, and his disciples follow him.
2 Da Asabbaci ya kewayo, sai ya fara koyarwa a cikin majami’a, mutane da yawa da suka saurare shi, suka yi mamaki. Suna tambaya, “Ina mutumin nan ya sami waɗannan abubuwa? Wace hikima ce wannan da aka ba shi, har da yana yin ayyukan banmamaki haka!
And when sabbath was come he began to teach in the synagogue, and many hearing were amazed, saying, Whence [has] this [man] these things? and what [is] the wisdom that is given to him, and such works of power are done by his hands?
3 Ashe, wannan ba shi ne kafinta nan ba? Shin, ba shi ne ɗan Maryamu ba, ba shi ne ɗan’uwan su Yaƙub, Yusuf, Yahuda da kuma Siman ba? Ashe,’yan’uwansa mata kuma ba suna nan tare da mu ba?” Sai suka ji haushinsa.
Is not this the carpenter, the son of Mary, and brother of James, and Joses, and Judas, and Simon? and are not his sisters here with us? And they were offended in him.
4 Yesu ya ce musu, “Sai a garinsa kaɗai, da kuma cikin’yan’uwansa, da cikin gidansa ne, annabi ba shi da daraja.”
But Jesus said to them, A prophet is not despised save in his own country, and among [his] kinsmen, and in his own house.
5 Bai iya yin ayyukan banmamaki a wurin ba, sai dai ɗibiya hannuwansa da ya yi a kan mutane kima da suke da cututtuka, ya kuwa warkar da su.
And he could not do any work of power there, save that laying his hands on a few infirm persons he healed [them].
6 Ya kuwa yi mamaki ƙwarai don rashin bangaskiyarsu. Sai ya Yesu zazzaga ƙauyuka yana koyarwa.
And he wondered because of their unbelief. And he went round the villages in a circuit, teaching.
7 Ya kira Sha Biyun nan wurinsa, ya aike su biyu-biyu, ya kuma ba su iko bisa mugayen ruhohi.
And he calls the twelve to [him]; and he began to send them out two [and] two, and gave to them power over the unclean spirits;
8 Ga dai umarnansa, “Kada ku ɗauki kome don tafiyar, sai dai sanda ba burodi, ba jaka, ba kuɗi a ɗamararku.
and he commanded them that they should take nothing for the way, save a staff only; no scrip, no bread, no money in their belt;
9 Ku sa takalma, amma ban da riga fiye da waɗanda kuka sa.
but be shod with sandals, and put not on two body-coats.
10 Duk sa’ad da kuka shiga wani gida, ku zauna nan sai kun bar garin.
And he said to them, Wheresoever ye shall enter into a house, there remain till ye shall go thence.
11 In kuwa a wani wuri ba a karɓe ku, ba a kuwa saurare ku ba, sai ku karkaɗe ƙurar ƙafafunku sa’ad da kuka fita, a matsayin shaida a kansu.”
And whatsoever place shall not receive you nor hear you, departing thence, shake off the dust which is under your feet for a testimony to them.
12 Suka fita, suna yi wa’azi, suna ce wa mutane su tuba.
And they went forth and preached that they should repent;
13 Suka fitar da aljanu da yawa, suka shafa wa marasa lafiya da yawa mai, suka kuwa warkar da su.
and they cast out many demons, and anointed with oil many infirm, and healed them.
14 Sarki Hiridus ya ji wannan labari, gama sunan Yesu ya bazu a ko’ina. Waɗansu suna cewa, “An tashe Yohanna Mai Baftisma daga matattu ne, shi ya sa yana da ikon yin ayyukan banmamakin nan.”
And Herod the king heard [of him] (for his name had become public), and said, John the baptist is risen from among [the] dead, and on this account works of power are wrought by him.
15 Waɗansu suka ce, “Ai, Iliya ne.” Har wa yau waɗansu suka ce, “Ai, annabi ne, kamar ɗaya daga cikin annabawan dā.”
And others said, It is Elias; and others said, It is a prophet, as one of the prophets.
16 Amma da Hiridus ya ji haka, sai ya ce, “Ai, Yohanna ne, mutumin da na yanke masa kai, shi ne ya tashi daga matattu!”
But Herod when he heard [it] said, John whom I beheaded, he it is; he is risen [from among the dead].
17 Gama Hiridus da kansa ya ba da umarni a kama Yohanna, ya kuma sa aka daure shi, aka sa shi a kurkuku. Ya yi haka saboda Hiridiyas, matar ɗan’uwansa Filibus, wadda ya aura.
For the same Herod had sent and seized John, and had bound him in prison on account of Herodias, the wife of Philip his brother, because he had married her.
18 Gama Yohanna ya yi ta ce wa Hiridus, “Ba daidai ba ne bisa ga doka, ka ɗauki matar ɗan’uwanka.”
For John said to Herod, It is not lawful for thee to have the wife of thy brother.
19 Saboda haka, Hiridiyas ta ƙulla munafunci game da Yohanna, ta kuma so ta kashe shi. Amma ba tă iya ba,
But Herodias kept it [in her mind] against him, and wished to kill him, and could not:
20 domin Hiridus yana jin tsoron Yohanna, ya kuma kāre shi sosai, da sanin cewa shi mutum ne mai adalci da kuma mai tsarki. Duk sa’ad da Hiridus ya saurari Yohanna, yakan damu ƙwarai, duk da haka, yakan so yă ji shi.
for Herod feared John knowing that he was a just and holy man, and kept him safe; and having heard him, did many things, and heard him gladly.
21 A ƙarshe, ta sami zarafi. A ranar murnar haihuwar Hiridus, ya yi biki domin hakimansa, da shugabannin sojojinsa, da kuma manyan mutanen Galili.
And a holiday being come, when Herod, on his birthday, made a supper to his grandees, and to the chiliarchs, and the chief [men] of Galilee;
22 Sa’ad da diyar Hiridiyas ta shigo, ta kuma yi rawa, sai ta gamshi Hiridus tare da baƙinsa. Sai Sarkin ya ce wa yarinyar, “Ki tambaye ni kome da kike so, ni kuwa zan ba ki.”
and the daughter of the same Herodias having come in, and danced, pleased Herod and those that were with [him] at table; and the king said to the damsel, Ask of me whatsoever thou wilt and I will give it thee.
23 Ya yi mata alkawari da rantsuwa cewa, “Duk abin da kika roƙa, zan ba ki, ko da rabin mulkina ne.”
And he swore to her, Whatsoever thou shalt ask me I will give thee, to half of my kingdom.
24 Sai ta fita ta ce wa mahaifiyarta, “Me zan roƙa?” Ta ce, “Kan Yohanna Mai Baftisma.”
And she went out, and said to her mother, What should I ask? And she said, The head of John the baptist.
25 Nan da nan, sai yarinyar ta yi hanzari zuwa wajen sarki da roƙon, “Ina so ka ba ni kan Yohanna Mai Baftisma a cikin tasa, yanzu-yanzu nan.”
And immediately going in with haste to the king, she asked saying, I desire that thou give me directly upon a dish the head of John the baptist.
26 Sai sarki ya yi baƙin ciki ƙwarai, amma saboda rantsuwar da kuma baƙinsa, bai so yă hana ta ba.
And the king, [while] made very sorry, on account of the oaths and those lying at table with [him] would not break his word with her.
27 Nan take, sai ya aiki mai aiwatar da kisa da umarni ya kawo kan Yohanna. Mutumin ya je ya yanke kan Yohanna a kurkuku.
And immediately the king, having sent one of the guard, ordered his head to be brought. And he went out and beheaded him in the prison,
28 Ya kuma kawo kan a tasa ya ba yarinyar. Ita kuma ta ba wa mahaifiyarta.
and brought his head upon a dish, and gave it to the damsel, and the damsel gave it to her mother.
29 Da almajiran Yohanna suka sami labari, sai suka zo suka ɗauki jikinsa suka binne a kabari.
And his disciples having heard [it], came and took up his body, and laid it in a tomb.
30 Manzannin suka taru kewaye da Yesu, suka ba shi rahoton duk abin da suka yi, da kuma suka koyar.
And the apostles are gathered together to Jesus. And they related to him all things, [both] what they had done and what they had taught.
31 To, saboda mutane da yawa suna kai da kawowa, har ma ba su sami damar cin abinci ba, sai ya ce musu, “Ku zo mu kaɗaita inda ba kowa don ku ɗan huta.”
And he said to them, Come ye yourselves apart into a desert place and rest a little. For those coming and those going were many, and they had not leisure even to eat.
32 Sai suka tafi a jirgin ruwa su kaɗai, inda ba kowa.
And they went away apart into a desert place by ship.
33 Amma mutane da yawa waɗanda suka ga tashinsu, sun gane su, sai suka ruga da gudu a ƙafa daga dukan birane, suka riga su kaiwa can.
And many saw them going, and recognised them, and ran together there on foot, out of all the cities, and got [there] before them.
34 Da Yesu ya sauka, ya ga taro mai yawa, sai ya ji tausayinsu, gama kamar tumaki suke waɗanda ba su da makiyayi. Sai ya fara koya musu abubuwa da yawa.
And on leaving [the ship] [Jesus] saw a great crowd, and he was moved with compassion for them, because they were as sheep not having a shepherd. And he began to teach them many things.
35 A lokacin nan yamma ta yi, sai almajiransa suka zo wurinsa suka ce masa, “Wurin nan ƙauye ne, ga shi kuma lokaci ya ƙure.
And when it was already late in the day, his disciples coming to him say, The place is desert, and it is already late in the day;
36 Ka sallami mutanen su shiga ƙauyukan da suke kurkusa, su sayi wa kansu wani abu, su ci.”
send them away that they may go into the country and villages around, and buy themselves bread, for they have not anything they can eat.
37 Sai ya amsa ya ce, “Ku, ku ba su wani abu su ci.” Suka ce masa, “Ai, wannan zai ɗauki albashin wata takwas na mutum! Mu je mu kashe yawan kuɗin nan a burodi mu ba su su ci?”
And he answering said to them, Give ye them to eat. And they say to him, Shall we go and buy two hundred denarii worth of bread and give them to eat?
38 Sai ya yi tambaya ya ce, “Burodi nawa kuke da su? Je ku duba.” Da suka duba, sai suka ce, “Biyar da kifi biyu.”
And he says to them, How many loaves have ye? Go [and] see. And when they knew they say, Five, and two fishes.
39 Sa’an nan Yesu ya umarce su su sa dukan mutanen su zazzauna ƙungiya-ƙungiya a kan ɗanyar ciyawa.
And he ordered them to make them all sit down by companies on the green grass.
40 Haka suka zazzauna a ƙungiyar ɗari-ɗari, da kuma hamsin-hamsin.
And they sat down in ranks by hundreds and by fifties.
41 Ya ɗauki burodi guda biyar da kifin nan biyu, ya ɗaga kai sama, ya yi godiya, ya kakkarya burodin. Sai ya ba wa almajiransa su rarraba wa mutane. Ya kuma rarraba kifi biyun a tsakaninsu duka.
And having taken the five loaves and the two fishes, looking up to heaven, he blessed, and broke the loaves, and gave [them] to his disciples that they might set [them] before them. And the two fishes he divided among all.
And they all ate and were satisfied.
43 almajiran suka kwashe gutsattsarin burodin da na kifin cike da kwanduna goma sha biyu.
And they took up of fragments the fillings of twelve hand-baskets, and of the fishes.
44 Yawan mutanen da suka ci kuwa maza dubu biyar ne.
And those that ate of the loaves were five thousand men.
45 Nan da nan Yesu ya sa almajiransa su shiga jirgin ruwa, su sha gabansa zuwa Betsaida, shi kuma yă sallami taron.
And immediately he compelled his disciples to go on board ship, and to go on before to the other side to Bethsaida, while he sends the crowd away.
46 Bayan ya bar su, sai ya hau kan dutse don yă yi addu’a.
And, having dismissed them, he departed into the mountain to pray.
47 Da yamma ta yi, jirgin ruwan yana tsakiyar tafkin, Yesu kuma yana can a ƙasa shi kaɗai.
And when evening was come, the ship was in the midst of the sea, and he alone upon the land.
48 Ya ga almajiran suna fama da tuƙi saboda iska tana gāba da su. Wajen tsara ta huɗu na dare, sai ya tafi wurinsu, yana takawa a kan tafkin. Ya yi kamar zai wuce su,
And seeing them labouring in rowing, for the wind was contrary to them, about the fourth watch of the night he comes to them walking on the sea, and would have passed them by.
49 amma da suka gan shi yana takawa a kan tafkin, sai suka yi tsammani fatalwa ce. Sai suka yi ihu,
But they, seeing him walking on the sea, thought that it was an apparition, and cried out.
50 domin dukansu sun gan shi, suka kuma tsorata. Nan da nan ya yi magana da su ya ce, “Ku yi ƙarfin hali! Ni ne. Kada ku ji tsoro.”
For all saw him and were troubled. And immediately he spoke with them, and says to them, Be of good courage: it is I; be not afraid.
51 Sai ya shiga jirgin ruwan tare da su, iskar kuma ta kwanta. Dukansu suka yi mamaki,
And he went up to them into the ship, and the wind fell. And they were exceedingly beyond measure astonished in themselves and wondered;
52 gama ba su fahimci al’amarin burodin nan ba, don zuciyarsu ta taurare.
for they understood not through the loaves: for their heart was hardened.
53 Da suka haye, sai suka sauka a Gennesaret, suka daure jirgin a ƙugiya.
And having passed over, they came to the land of Gennesaret and made the shore.
54 Da fitowarsu daga jirgin, sai mutane suka gane Yesu.
And on their coming out of the ship, immediately recognising him,
55 Suka gama yankin da gudu, suna ɗaukan marasa lafiya a kan tabarmai zuwa duk inda suka ji yake.
they ran through that whole country around, and began to carry about those that were ill on couches, where they heard that he was.
56 Duk inda ya shiga, cikin ƙauyuka, birane ko karkara, sai su kwantar da marasa lafiya a bakin kasuwa. Suka roƙe shi yă bari su taɓa gefen rigarsa kawai, kuma duk waɗanda suka taɓa shi kuwa, suka warke.
And wherever he entered into villages, or cities, or the country, they laid the sick in the market-places, and besought him that they might touch if it were only the hem of his garment; and as many as touched him were healed.