< Markus 5 >

1 Suka ƙetare tafkin suka je yankin Gerasenawa.
And they went across the strait of the sea into the region of the Gerasenes.
2 Da Yesu ya sauka daga jirgin ruwa, sai wani mutum mai mugun ruhu ya fito daga kaburbura, ya tarye shi.
And as he was departing from the boat, he was immediately met, from among the tombs, by a man with an unclean spirit,
3 Wannan mutumin ya mai da kaburbura gidansa. Kuma ba wanda ya iya daure shi, ko da sarƙa ma.
who had his dwelling place with the tombs; neither had anyone been able to bind him, even with chains.
4 Gama an sha daure shi hannu da ƙafa da sarƙa, amma yakan tsintsinke sarƙar, yă kuma karye ƙarafan da suke ƙafafunsa. Ba wanda yake da ƙarfin da zai iya yă riƙe shi.
For having been bound often with shackles and chains, he had broken the chains and smashed the shackles; and no one had been able to tame him.
5 Dare da rana, sai yă dinga kuka yana ƙuƙƙuje jikinsa da duwatsu a cikin kaburbura da kan tuddai.
And he was always, day and night, among the tombs, or in the mountains, crying out and cutting himself with stones.
6 Da ya hangi Yesu daga nesa, sai ya ruga da gudu, ya zo ya durƙusa a gabansa.
And seeing Jesus from afar, he ran and adored him.
7 Ya yi ihu da babbar murya ya ce, “Ina ruwanka da ni Yesu, Ɗan Allah Mafi Ɗaukaka? Ka rantse da Allah cewa ba za ka ba ni azaba ba!”
And crying out with a loud voice, he said: “What am I to you, Jesus, the Son of the Most High God? I beseech you by God, that you not torment me.”
8 Gama Yesu ya riga ya ce masa, “Ka fita daga jikin mutumin nan, kai mugun ruhu!”
For he said to him, “Depart from the man, you unclean spirit.”
9 Sai Yesu ya tambaye shi ya ce, “Mene ne sunanka?” Sai ya amsa ya ce, “Sunana Lejiyon, wato, ‘Tuli,’ domin muna da yawa.”
And he questioned him: “What is your name?” And he said to him, “My name is Legion, for we are many.”
10 Sai ya yi ta roƙon Yesu, kada yă kore su daga wurin.
And he entreated him greatly, so that he would not expel him from the region.
11 A kan tudun da yake nan kusa kuwa, akwai wani babban garken aladu, suna kiwo.
And in that place, near the mountain, there was a great herd of swine, feeding.
12 Sai aljanun suka roƙi Yesu, suka ce, “Tura mu cikin aladun nan, ka bari mu shiga cikinsu.”
And the spirits entreated him, saying: “Send us into the swine, so that we may enter into them.”
13 Ya kuwa yarda musu, sai mugayen ruhohin suka fita suka shiga cikin aladun. Garken kuwa, yana da kusan aladu dubu biyu, suka gangara daga kan tudun zuwa cikin tafkin, suka nutse.
And Jesus promptly gave them permission. And the unclean spirits, departing, entered into the swine. And the herd of about two thousand rushed down with great force into the sea, and they were drowned in the sea.
14 Masu kiwon aladun kuwa suka ruga da gudu zuwa cikin gari da ƙauyuka, suka ba da wannan labari. Sai mutanen suka fito, domin su ga abin da ya faru.
Then those who pastured them fled, and they reported it in the city and in the countryside. And they all went out to see what was happening.
15 Da suka kai wajen Yesu, sai suka ga mutumin da dā yake da tulin aljanun yana zaune a wurin, sanye da tufafi kuma cikin hankalinsa, sai suka ji tsoro.
And they came to Jesus. And they saw the man who had been troubled by the demon, sitting, clothed and with a sane mind, and they were afraid.
16 Waɗanda suka ga abin da ya faru, suka ba da labarin abin da ya faru da mai aljanun, da kuma aladun.
And those who had seen it explained to them how he had dealt with the man who had the demon, and about the swine.
17 Sai mutane suka fara roƙon Yesu yă bar yankinsu.
And they began to petition him, so that he would withdraw from their borders.
18 Yesu yana kan shiga cikin jirgin ruwa ke nan, sai mutumin da dā yake da aljanun ya roƙa yă bi shi.
And as he was climbing into the boat, the man who had been troubled by the demons began to beg him, so that he might be with him.
19 Yesu bai yardar masa ba, amma ya ce, “Ka tafi gida wurin iyalinka, ka gaya musu babban alherin da Ubangiji ya yi maka, da yadda ya yi maka jinƙai.”
And he did not permit him, but he said to him, “Go to your own people, in your own house, and announce to them how great are the things that the Lord has done for you, and how he has taken pity on you.”
20 Sai mutumin ya tafi, ya yi ta ba da labari a cikin Dekafolis a kan babban alherin da Yesu ya yi masa. Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
And he went away and began to preach in the Ten Cities, how great were the things that Jesus had done for him. And everyone wondered.
21 Da Yesu ya sāke ƙetarewa cikin jirgin ruwa zuwa ɗaya hayen tafkin, sai taro mai yawa ya taru kewaye da shi yayinda yake a bakin tafkin.
And when Jesus had crossed in the boat, over the strait again, a great crowd came together before him. And he was near the sea.
22 Sai ɗaya a cikin masu mulkin majami’a, wanda ake kira Yayirus ya zo wurin. Da ganin Yesu, sai ya durƙusa a gabansa,
And one of the rulers of the synagogue, named Jairus, approached. And seeing him, he fell prostrate at his feet.
23 ya roƙe shi da gaske ya ce, “Ƙaramar diyata tana bakin mutuwa. In ka yarda, ka zo ka ɗibiya hannunka a kanta, domin ta warke, ta kuma rayu.”
And he beseeched him greatly, saying: “For my daughter is near the end. Come and lay your hand on her, so that she may be healthy and may live.”
24 Sai Yesu ya tafi tare da shi. Babban taron kuma ya bi shi, suna ta matsinsa a kowane gefe.
And he went with him. And a great crowd followed him, and they pressed upon him.
25 A can kuwa akwai wata mace, wadda ta yi shekaru goma sha biyu tana zub da jini.
And there was a woman who had a flow of blood for twelve years.
26 Ta kuma sha wahala ƙwarai a hannun likitoci da yawa, har ta kashe duk abin da take da shi, amma maimakon samun sauƙi, sai ciwon ya ƙara muni.
And she had endured much from several physicians, and she had spent everything she owned with no benefit at all, but instead she became worse.
27 Da ta ji labarin Yesu, sai ta zo ta bayansa, a cikin taron, ta taɓa rigarsa,
Then, when she had heard of Jesus, she approached through the crowd behind him, and she touched his garment.
28 domin ta yi tunani cewa, “Ko da rigunarsa ma na taɓa, zan warke.”
For she said: “Because if I touch even his garment, I will be saved.”
29 Nan da take, zub da jininta ya tsaya, sai ta ji a jikinta ta rabu da shan wahalarta.
And immediately, the source of her bleeding was dried up, and she sensed in her body that she had been healed from the wound.
30 Nan da nan Yesu ya gane cewa, iko ya fita daga gare shi. Sai ya juya a cikin taron ya yi tambaya, “Wa ya taɓa rigata?”
And immediately Jesus, realizing within himself that power that had gone out from him, turning to the crowd, said, “Who touched my garments?”
31 Sai almajiransa suka ce, “Kana ganin mutane suna matsinka, duk da haka kana tambaya, ‘Wa ya taɓa ni?’”
And his disciples said to him, “You see that the crowd presses around you, and yet you say, ‘Who touched me?’”
32 Amma Yesu ya ci gaba da dubawa don yă ga wa ya taɓa shi.
And he looked around to see the woman who had done this.
33 Matar, da yake ta san abin da ya faru da ita, sai ta zo ta durƙusa a gabansa, da tsoro da rawan jiki, ta kuma gaya masa dukan abin da ya faru.
Yet truly, the woman, in fear and trembling, knowing what had happened within her, went and fell prostrate before him, and she told him the whole truth.
34 Sai ya ce mata, “Diyata, bangaskiyarki ta warkar da ke. Ki sauka lafiya, kin kuma rabu da dukan wahalarki.”
And he said to her: “Daughter, your faith has saved you. Go in peace, and be healed from your wound.”
35 Yayinda Yesu yana cikin magana, sai waɗansu mutane daga gidan Yayirus, mai mulkin majami’a, suka zo suka ce, “Diyarka ta rasu. Kada ma ka wahal da Malam.”
While he was still speaking, they arrived from the ruler of the synagogue, saying: “Your daughter is dead. Why trouble the Teacher any further?”
36 Yesu bai kula da abin da suka faɗa ba, sai ya ce wa mai mulkin majami’ar, “Kada ka ji tsoro, ka gaskata kawai.”
But Jesus, having heard the word that was spoken, said to the ruler of the synagogue: “Do not be afraid. You need only believe.”
37 Bai bar kowa ya bi shi ba, sai Bitrus, Yaƙub da Yohanna ɗan’uwan Yaƙub.
And he would not permit anyone to follow him, except Peter, and James, and John the brother of James.
38 Da suka iso gidan mai mulkin majami’ar, sai Yesu ya ga ana hayaniya, mutane suna kuka da kururuwa.
And they went to the house of the ruler of the synagogue. And he saw a tumult, and weeping, and much wailing.
39 Sai ya shiga ciki, ya ce musu, “Mene ne dalilin wannan hayaniya da kuka? Yarinyar ba mutuwa ne ta yi ba, barci take yi.”
And entering, he said to them: “Why are you disturbed and weeping? The girl is not dead, but is asleep.”
40 Sai suka yi masa dariya. Bayan ya fitar da su duk waje, sai ya ɗauki mahaifin da mahaifiyar yarinyar tare da almajiran da suke tare da shi, suka shiga inda yarinyar take.
And they derided him. Yet truly, having put them all out, he took the father and mother of the girl, and those who were with him, and he entered to where the girl was lying.
41 Sai ya kama hannunta ya ce mata, “Talita kum!” (Wato, “Ƙaramar yarinya, na ce miki, tashi!”).
And taking the girl by the hand, he said to her, “Talitha koumi,” which means, “Little girl, (I say to you) arise.”
42 Nan da nan, sai yarinyar ta tashi ta yi tafiya (shekarunta goma sha biyu ne). Saboda wannan, suka yi mamaki ƙwarai.
And immediately the young girl rose up and walked. Now she was twelve years old. And they were suddenly struck with a great astonishment.
43 Sai ya ba da umarni mai tsanani, kada kowa yă san kome game da wannan. Sai ya ce musu, su ba ta wani abu tă ci.
And he instructed them sternly, so that no one would know about it. And he told them to give her something to eat.

< Markus 5 >