< Markus 5 >
1 Suka ƙetare tafkin suka je yankin Gerasenawa.
Na protějším břehu jezera přistáli v gerasenském kraji.
2 Da Yesu ya sauka daga jirgin ruwa, sai wani mutum mai mugun ruhu ya fito daga kaburbura, ya tarye shi.
Jakmile Ježíš vystoupil ze člunu, přiběhl k němu nějaký člověk. Byl to muž posedlý démony,
3 Wannan mutumin ya mai da kaburbura gidansa. Kuma ba wanda ya iya daure shi, ko da sarƙa ma.
který žil ve starých hrobech vytesaných do skály
4 Gama an sha daure shi hannu da ƙafa da sarƙa, amma yakan tsintsinke sarƙar, yă kuma karye ƙarafan da suke ƙafafunsa. Ba wanda yake da ƙarfin da zai iya yă riƙe shi.
a měl takovou sílu, že když ho spoutali okovy na nohou a řetězy na rukou, pouta vždycky rozlámal a řetězy roztrhal. Nenašel se nikdo tak silný, aby ho mohl zkrotit.
5 Dare da rana, sai yă dinga kuka yana ƙuƙƙuje jikinsa da duwatsu a cikin kaburbura da kan tuddai.
Ve dne i v noci se skrýval v hrobech a toulal se po okolních pahorcích, skučel a tloukl se kamením.
6 Da ya hangi Yesu daga nesa, sai ya ruga da gudu, ya zo ya durƙusa a gabansa.
Když teď uviděl Ježíše, přiběhl a vrhl se před ním na zem. Ve chvíli, kdy Ježíš přikazoval démonovi, aby posedlého muže opustil, začal onen ubožák křičet: „Co si mne všímáš, Ježíši, Synu Boha nejvyššího? Zapřísahám tě při Bohu, nech mne na pokoji!“
7 Ya yi ihu da babbar murya ya ce, “Ina ruwanka da ni Yesu, Ɗan Allah Mafi Ɗaukaka? Ka rantse da Allah cewa ba za ka ba ni azaba ba!”
8 Gama Yesu ya riga ya ce masa, “Ka fita daga jikin mutumin nan, kai mugun ruhu!”
9 Sai Yesu ya tambaye shi ya ce, “Mene ne sunanka?” Sai ya amsa ya ce, “Sunana Lejiyon, wato, ‘Tuli,’ domin muna da yawa.”
„Jak se jmenuješ?“zeptal se Ježíš. „Zástup, protože je nás v tomto těle mnoho, “zněla odpověď.
10 Sai ya yi ta roƙon Yesu, kada yă kore su daga wurin.
A potom démoni žadonili, aby je neposílal nikam daleko.
11 A kan tudun da yake nan kusa kuwa, akwai wani babban garken aladu, suna kiwo.
Na stráni nad pobřežím se právě páslo stádo vepřů.
12 Sai aljanun suka roƙi Yesu, suka ce, “Tura mu cikin aladun nan, ka bari mu shiga cikinsu.”
„Pošli nás do těch prasat, “volali démoni.
13 Ya kuwa yarda musu, sai mugayen ruhohin suka fita suka shiga cikin aladun. Garken kuwa, yana da kusan aladu dubu biyu, suka gangara daga kan tudun zuwa cikin tafkin, suka nutse.
Ježíš svolil a nečistí duchové vjeli do zvířat. Vzápětí se to velké, asi dvoutisícové stádo splašilo a hnalo se po stráni dolů k jezeru, vběhlo do vody a utopilo se.
14 Masu kiwon aladun kuwa suka ruga da gudu zuwa cikin gari da ƙauyuka, suka ba da wannan labari. Sai mutanen suka fito, domin su ga abin da ya faru.
Pasáci těch vepřů utekli do města a cestou všude rozhlašovali, co se stalo. Každý, kdo je uslyšel, spěchal se o tom přesvědčit na vlastní oči.
15 Da suka kai wajen Yesu, sai suka ga mutumin da dā yake da tulin aljanun yana zaune a wurin, sanye da tufafi kuma cikin hankalinsa, sai suka ji tsoro.
A tak se kolem Ježíše shromáždilo mnoho lidí. Když viděli uzdraveného muže, jak sedí oblečený a chová se rozumně, polekali se.
16 Waɗanda suka ga abin da ya faru, suka ba da labarin abin da ya faru da mai aljanun, da kuma aladun.
Ti, kteří byli svědky celé události, jim totiž vyprávěli, co se událo s mužem a kam se poděli vepři.
17 Sai mutane suka fara roƙon Yesu yă bar yankinsu.
A tak začali všichni Ježíše prosit, aby z jejich kraje raději odešel.
18 Yesu yana kan shiga cikin jirgin ruwa ke nan, sai mutumin da dā yake da aljanun ya roƙa yă bi shi.
Nastoupil tedy zase do člunu. Uzdravený muž ho prosil, aby mohl jít s ním.
19 Yesu bai yardar masa ba, amma ya ce, “Ka tafi gida wurin iyalinka, ka gaya musu babban alherin da Ubangiji ya yi maka, da yadda ya yi maka jinƙai.”
Ježíš však odmítl: „Jdi domů ke své rodině a řekni všem známým, jaké dobrodiní ti Bůh prokázal a jak se nad tebou slitoval.“
20 Sai mutumin ya tafi, ya yi ta ba da labari a cikin Dekafolis a kan babban alherin da Yesu ya yi masa. Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
Ten člověk tedy v celém tom kraji zvaném Desítiměstí vyprávěl, jak velké dobrodiní mu prokázal Ježíš. A každý nad tím žasl.
21 Da Yesu ya sāke ƙetarewa cikin jirgin ruwa zuwa ɗaya hayen tafkin, sai taro mai yawa ya taru kewaye da shi yayinda yake a bakin tafkin.
Když se Ježíš znovu vrátil na galilejský břeh, sešel se kolem něho zase obrovský zástup lidí.
22 Sai ɗaya a cikin masu mulkin majami’a, wanda ake kira Yayirus ya zo wurin. Da ganin Yesu, sai ya durƙusa a gabansa,
Přišel i představený místní synagogy Jairos, klekl před ním
23 ya roƙe shi da gaske ya ce, “Ƙaramar diyata tana bakin mutuwa. In ka yarda, ka zo ka ɗibiya hannunka a kanta, domin ta warke, ta kuma rayu.”
a úpěnlivě ho prosil: „Moje dceruška umírá. Pojď a zachraň ji, aby žila.“
24 Sai Yesu ya tafi tare da shi. Babban taron kuma ya bi shi, suna ta matsinsa a kowane gefe.
Ježíš tedy šel s ním. Také zástup se vydal s nimi a tlačil se na Ježíše ze všech stran.
25 A can kuwa akwai wata mace, wadda ta yi shekaru goma sha biyu tana zub da jini.
V davu byla jedna žena, která už dvanáct let trpěla krvácením.
26 Ta kuma sha wahala ƙwarai a hannun likitoci da yawa, har ta kashe duk abin da take da shi, amma maimakon samun sauƙi, sai ciwon ya ƙara muni.
Mnoho lékařů na ní zkoušelo své umění. Stálo ji to celé jmění, ale nebylo to nic platné, nemoc se stále zhoršovala.
27 Da ta ji labarin Yesu, sai ta zo ta bayansa, a cikin taron, ta taɓa rigarsa,
Až jednou se doslechla o Ježíšovi a jeho zázračné moci, a tak ho hledala s myšlenkou: „Když si jen sáhnu na jeho plášť, určitě se uzdravím.“
28 domin ta yi tunani cewa, “Ko da rigunarsa ma na taɓa, zan warke.”
29 Nan da take, zub da jininta ya tsaya, sai ta ji a jikinta ta rabu da shan wahalarta.
A opravdu! Jakmile se ho dotkla, krvácení přestalo a žena cítila, že je nadobro zdravá.
30 Nan da nan Yesu ya gane cewa, iko ya fita daga gare shi. Sai ya juya a cikin taron ya yi tambaya, “Wa ya taɓa rigata?”
Ježíš ovšem ihned poznal, že z něho vyšla uzdravující síla, otočil se a otázal se: „Kdo se to dotkl mého pláště?“
31 Sai almajiransa suka ce, “Kana ganin mutane suna matsinka, duk da haka kana tambaya, ‘Wa ya taɓa ni?’”
Jeho učedníci se divili: „Všichni se na tebe tlačí a ty se ptáš, kdo se tě dotkl?“
32 Amma Yesu ya ci gaba da dubawa don yă ga wa ya taɓa shi.
Ale Ježíš se rozhlížel, aby zjistil, kdo to byl.
33 Matar, da yake ta san abin da ya faru da ita, sai ta zo ta durƙusa a gabansa, da tsoro da rawan jiki, ta kuma gaya masa dukan abin da ya faru.
Žena, celá rozechvělá tím, co se s ní událo, padla mu k nohám a všechno mu pravdivě pověděla.
34 Sai ya ce mata, “Diyata, bangaskiyarki ta warkar da ke. Ki sauka lafiya, kin kuma rabu da dukan wahalarki.”
On ji ujistil: „Dcero, tvá víra tě uzdravila. Můžeš klidně jít, protože nemoc tě už nebude trápit.“
35 Yayinda Yesu yana cikin magana, sai waɗansu mutane daga gidan Yayirus, mai mulkin majami’a, suka zo suka ce, “Diyarka ta rasu. Kada ma ka wahal da Malam.”
Když s ní ještě mluvil, dorazili poslové z Jairova domu se zprávou, že již je pozdě shánět pomoc. „Tvá dcera právě umřela, už Mistra neobtěžuj, “oznamovali Jairovi.
36 Yesu bai kula da abin da suka faɗa ba, sai ya ce wa mai mulkin majami’ar, “Kada ka ji tsoro, ka gaskata kawai.”
Jako by nic neslyšel, obrátil se Ježíš k Jairovi a řekl mu: „Jen se neboj a důvěřuj mi!“Do Jairova domu s sebou vzal pouze Petra, Jakuba a jeho bratra Jana. Ostatní požádal, aby zůstali venku.
37 Bai bar kowa ya bi shi ba, sai Bitrus, Yaƙub da Yohanna ɗan’uwan Yaƙub.
38 Da suka iso gidan mai mulkin majami’ar, sai Yesu ya ga ana hayaniya, mutane suna kuka da kururuwa.
Dům byl plný hlasitého pláče a nářku. „K čemu ten pláč a rozruch? Vždyť to děvče není mrtvé, jenom spí!“
39 Sai ya shiga ciki, ya ce musu, “Mene ne dalilin wannan hayaniya da kuka? Yarinyar ba mutuwa ne ta yi ba, barci take yi.”
40 Sai suka yi masa dariya. Bayan ya fitar da su duk waje, sai ya ɗauki mahaifin da mahaifiyar yarinyar tare da almajiran da suke tare da shi, suka shiga inda yarinyar take.
Vysmáli se mu. Vykázal všechny kromě rodičů a svých tří učedníků. Vešli do místnosti, kde dívka ležela.
41 Sai ya kama hannunta ya ce mata, “Talita kum!” (Wato, “Ƙaramar yarinya, na ce miki, tashi!”).
Vzal ji za ruku a řekl: „Děvčátko, přikazuji ti, vstaň!“
42 Nan da nan, sai yarinyar ta tashi ta yi tafiya (shekarunta goma sha biyu ne). Saboda wannan, suka yi mamaki ƙwarai.
Dvanáctiletá dívka vstala a chodila. Přítomní oněměli úžasem.
43 Sai ya ba da umarni mai tsanani, kada kowa yă san kome game da wannan. Sai ya ce musu, su ba ta wani abu tă ci.
Ježíš jim důrazně nařídil, aby nikomu nevypravovali, co se stalo. „Dejte jí najíst, “připomněl rodičům.