< Markus 4 >
1 Har wa yau, Yesu ya fara koyarwa a bakin tafki. Domin taron da yake kewaye da shi mai girma ne sosai, sai ya shiga cikin jirgin ruwa, ya zauna a ciki a tafkin, dukan mutanen kuwa suna a gaɓar ruwan.
UJesu waphinda njalo wafundisa okhunjini lwesiziba. Ixuku labantu elaqoqana labuthana kuye laba likhulu kakhulu waze wangena esikepeni wahlala kuso siphakathi kwamanzi, kodwa abantu bonke bona bethe gwaqa okhunjini ekucineni kwamanzi.
2 Ya koya musu abubuwa da yawa da misalai. A koyarwarsa kuwa ya ce,
Wabafundisa izinto ezinengi ngemizekeliso, ekufundiseni kwakhe wathi:
3 “Ku saurara! Wani manomi ya fita don yă shuka irinsa.
“Lalelani! Umlimi waphuma wayahlanyela inhlanyelo yakhe.
4 Da yana yafa irin, sai waɗansu suka fāɗi a kan hanya, tsuntsaye suka zo suka cinye su.
Kwathi eyihaza inhlanyelo, enye yawela endleleni, kwafika izinyoni zayidobha.
5 Waɗansu suka fāɗi a wuri mai duwatsu inda babu ƙasa sosai. Nan da nan, suka tsira domin ƙasar ba zurfi.
Eyinye yawela okhetheni lapho okwakungela mhlabathi owaneleyo. Yamila masinyane ngoba umhlabathi wawungatshoni.
6 Amma da rana ta taso, sai tsire-tsiren suka ƙone, suka yanƙwane, domin ba su da saiwa.
Kodwa kwathi ilanga seliphumile, yahanguka yabuna ngoba yayingelampande.
7 Waɗansu irin suka fāɗi a cikin ƙaya. Da suka yi girma sai ƙaya suka shaƙe su, har ya sa ba su yi ƙwaya ba.
Enye inhlanyelo yawela emeveni asuka akhula aminya leyonhlanyelo yaze yehluleka ukuthela izikhwebu.
8 Har yanzu, waɗansu irin suka fāɗi a ƙasa mai kyau. Suka tsira, suka yi girma, suka ba da amfani, suka yi riɓi talatin-talatin, waɗansu sittin-sittin, waɗansu kuma ɗari-ɗari.”
Eyinye inhlanyelo yawela emhlabathini omuhle. Yamila, yakhula, yathela amabele yanda ngamatshumi amathathu, ayisithupha ngitsho langekhulu.”
9 Sai Yesu ya ce, “Duk mai kunnen ji, yă ji.”
UJesu wasesithi, “Lowo olendlebe zokuzwa kezwe.”
10 Lokacin da yake shi kaɗai, Sha Biyun, da kuma waɗanda suke kewaye da shi, suka tambaye shi game da misalan.
Kwathi eseyedwa, abalitshumi lambili labanye ababeseduze laye bambuza mayelana lemizekeliso leyo.
11 Sai ya ce musu, “An ba ku sanin asirin mulkin Allah. Amma ga waɗanda suke waje kuwa, kome sai da misalai.
Wabatshela wathi, “Imfihlakalo yombuso kaNkulunkulu seliyambulelwe. Kodwa kulabo abangaphandle konke kukhulunywa ngemizekeliso
12 Saboda, “‘ko sun dinga duba, ba za su taɓa gane ba, kuma ko su dinga ji, ba za su taɓa fahimta ba, in ba haka ba, mai yiwuwa, su tuba, a gafarta musu!’”
ukuze, ‘bazahlala bebona kokuphela kodwa bengabonisisi, njalo bahlale besizwa kodwa bengaqedisisi funa baphenduke bathethelelwe!’”
13 Sai Yesu ya ce musu, “Ba ku fahimci wannan misali ba? Yaya za ku fahimci wani misali ke nan?
UJesu wasesithi kubo, “Kaliwuzwisisi na umzekeliso lo? Pho lizawuzwa kanjani loba yiwuphi umzekeliso?
14 Manomi yakan shuka maganar Allah.
Umlimi uhlanyela ilizwi.
15 Waɗansu mutane suna kama da irin da ya fāɗi a kan hanya, inda akan shuka maganar Allah. Da jin maganar, nan da nan sai Shaiɗan yă zo yă ɗauke maganar da aka shuka a zuciyarsu.
Abanye abantu bafana lenhlanyelo esendleleni okuhlanyelwe khona ilizwi. Bonela ukuthi balizwe uSathane uyafika alithathe ilizwi elihlanyelwe kubo.
16 Waɗansu suna kama da irin da aka shuka a wurare masu duwatsu, sukan ji maganar Allah, sukan kuma karɓe ta nan da nan da farin ciki.
Abanye, njengenhlanyelo eyahlanyelwa okhetheni bayalizwa ilizwi bahle balamukele ngentokozo.
17 Amma da yake ba su da saiwa, ba sa daɗewa. Da wahala ko tsanani ya tashi saboda maganar, nan da nan, sai su ja da baya.
Kodwa ngenxa yokuthi kabalampande bema okwesikhatshana kuphela. Kungafika uhlupho loba ukuhlukuluzwa komhlaba baphanga bawe.
18 Har yanzu, waɗansu kamar irin da aka shuka cikin ƙaya, sukan ji maganar,
Kunjalo abanye, njengenhlanyelo ehlanyelwe emeveni, bayalizwa ilizwi;
19 amma damuwar wannan duniya, da son dukiya, da kuma kwaɗayin waɗansu abubuwa, sukan shiga, su shaƙe maganar, har su mai da ita marar amfani. (aiōn )
kodwa ukuphisekela izinto zalumhlaba, inkohliso yenotho kanye lezinkanuko zezinye izinto konke kuyeza kuliminyanise ilizwi, kulenze lingatheli. (aiōn )
20 Waɗansu mutane kuwa suna kama da irin da aka shuka a ƙasa mai kyau, sukan ji maganar Allah, su kuma karɓa, sa’an nan kuma su fid da amfani riɓi talatin-talatin, ko sittin-sittin, ko ɗari-ɗari.”
Abanye, njengenhlanyelo ehlanyelwe emhlabathini omuhle, bayalizwa ilizwi, balamukele, bathele izithelo, bedlule okwakuhlanyelwe ngamatshumi amathathu, ayisithupha loba ngekhulu.”
21 Sai ya ce musu, “Ko kukan kawo fitila ku rufe ta da murfi ko kuma ku sa ta a ƙarƙashin gado ne? Ba kukan sa ta a kan wurin ajiye fitila ba?
Wathi kubo, “Uyalumathisa isibane usifake ngaphansi kwesitsha kumbe ngaphansi kombheda na? Kawusibeki oluthini lwaso yini?
22 Duk abin da yake a ɓoye, dole za a fallasa shi. Duk abin da kuma yake a rufe, dole za a fitar da shi a fili.
Ngoba loba yini efihliweyo kumele yambulwe, lalokho okuthukuziweyo kumele kuvezwe obala.
23 Duk mai kunnen ji, bari yă ji.”
Nxa ekhona olendlebe zokuzwa kezwe.”
24 Ya ci gaba da cewa, “Ku lura da abin da kuke ji da kyau. Mudun da ka auna da shi, da shi za a auna maka, har ma a ƙara.
Waqhubeka wathi, “Kuqapheliseni lokho elikuzwayo. Ngaleso isilinganiso elisisebenzisayo lizalinganiselwa ngaso kumbe kuze kwedlulise.
25 Duk wanda yake da shi, za a ƙara masa, duk wanda kuma ba shi da shi, ko abin da yake da shi ma, za a karɓe daga gare shi.”
Lowo olakho uzakwengezelelwa; lowo ongelakho lalokho alakho uzakwemukwa.”
26 Ya sāke cewa, “Mulkin Allah yana kama da haka. Wani mutum ya yafa iri a gona.
Waphinda wathi, “Umbuso wezulu ufana lalokhu. Indoda ihaza inhlanyelo emhlabathini.
27 A kwana a tashi har irin yă tsiro, yă yi girma, bai kuwa santa yadda aka yi ba.
Ebusuku lemini ingabe ilele loba ikhangele inhlanyelo iyamila ikhule loba yona ingakwazi ukuthi kwenzeka njani.
28 Ƙasar da kanta takan ba da ƙwaya, da farko takan fid da ƙara, sa’an nan ta fid da kai, sa’an nan kan yă fid da ƙwaya.
Umhlabathi uyiwo wodwa uthela amabele, kuqala ikhaba kuze isikhwebu besekusiza inhlamvu ezikhwetshini.
29 Da ƙwayan ya nuna, sai yă sa lauje yă yanka, domin lokacin girbi ya yi.”
Kuthi amabele angavuthwa iwavune ngesikela ngoba ukuvuna sekufikile.”
30 Ya kuma ce, “Da me za mu kwatanta mulkin Allah, ko kuwa da wane misali za mu bayyana shi?
Waphinde wathi, “Sizakuthi umbuso kaNkulunkulu unjengani, kumbe sizasebenzisa umzekeliso bani ukuwuchaza?
31 Yana kama da ƙwayar mustad, wadda ita ce ƙwaya mafi ƙanƙanta da akan shuka a gona.
Unjengentanga yemastadi encinyane kulazo zonke intanga ezihlanyelwa emhlabathini.
32 Duk da haka, in aka shuka ƙwayar, sai tă yi girma, tă zama mafi girma a itatuwan lambu. Har itacen yă kasance da manyan rassa, inda tsuntsayen sararin sama sukan iya huta a inuwarsa.”
Kodwa nxa ihlanyeliwe iyakhula ibe yisihlahla esikhulu kulazo zonke esivandeni, sibe lengatsha ezinkulu ezihlalwa emthunzini waso yizinyoni zezulu.”
33 Da misalai da yawa irin waɗannan, Yesu ya yi magana da su, daidai yadda za su iya fahimta.
UJesu walikhuluma ilizwi kubo ngemizekeliso eminengi enjalo ukuze bazwisise.
34 Ba abin da ya faɗa musu, da ba da misali ba. Amma lokacin da yake shi kaɗai tare da almajiransa, sai yă bayyana kome.
Kazange atsho ulutho kubo engasebenzisanga umzekeliso. Kodwa nxa wayeyedwa labafundi bakhe wachaza konke.
35 A wannan rana, da yamma, sai ya ce wa almajiransa, “Mu ƙetare zuwa wancan hayi.”
Ngalelolanga sekuntambama wathi kubafundi bakhe, “Kasihambeni sichaphele ngaphetsheya.”
36 Da suka bar taron, sai suka tafi tare da shi yadda yake, a cikin jirgin ruwa. Akwai waɗansu jiragen ruwa kuma tare da shi.
Batshiya ixuku, bahamba laye esikepeni enjalo. Zazikhona njalo ezinye izikepe zihamba laye.
37 Sai babban hadari mai iska ya tashi, raƙuman ruwa suna ta bugun jirgin ruwan, har jirgin ruwan ya kusa yă cika da ruwa.
Kwaqubuka isiphepho esesabekayo, amagagasi atshaya esikepeni kwaze kwangathi sesitshona.
38 Yesu kuwa yana can baya, yana barci a kan katifa. Sai almajiran suka tashe shi suka ce masa, “Malam, ba ka kula ba ko mu nutse?”
UJesu wayengemuva ezilalele emendlalweni obuthakathaka. Abafundi bamvusa bathi, “Awu, mfundisi kawunanzi yini nxa sigalula?”
39 Sai ya farka ya tsawata wa iskar, ya ce wa raƙuman ruwan, “Shiru! Ku natsu!” Sai iskar ta kwanta, kome kuma ya yi tsit.
Waphakama wawukhuza umoya wathi emagagasini, “Thulani lithi cwaka!” Ngakho umoya wadeda, kwasekuthula cwaka.
40 Sai ya ce wa almajiransa, “Don me kuke tsoro haka? Har yanzu ba ku da bangaskiya ne?”
Wathi kubafundi bakhe, “Kungani lisesaba kangaka? Lilokhu lingakholwa na?”
41 Suka tsorata, suka ce wa juna, “Wane ne wannan? Har iska da raƙuman ruwa ma suna masa biyayya!”
Babethuthumela babuzana bathi, “Ungubani lo na? Kambe aze alalelwe ngumoya lamagagasi!”