< Markus 4 >
1 Har wa yau, Yesu ya fara koyarwa a bakin tafki. Domin taron da yake kewaye da shi mai girma ne sosai, sai ya shiga cikin jirgin ruwa, ya zauna a ciki a tafkin, dukan mutanen kuwa suna a gaɓar ruwan.
Jeesus hakkas taas mere ääres õpetama. Teda tuli kuulama nii palju rahvast, et ta astus paati ja istus vee peal paadis, sel ajal kui rahvas kuulas teda kaldal.
2 Ya koya musu abubuwa da yawa da misalai. A koyarwarsa kuwa ya ce,
Ta näitlikustas oma õpetusi paljude lugudega.
3 “Ku saurara! Wani manomi ya fita don yă shuka irinsa.
„Kuulake, “ütles ta. „Üks külvaja läks välja külvama.
4 Da yana yafa irin, sai waɗansu suka fāɗi a kan hanya, tsuntsaye suka zo suka cinye su.
Kui ta külvates seemneid laiali puistas, kukkus osa teerajale, linnud tulid ja sõid seemned sealt ära.
5 Waɗansu suka fāɗi a wuri mai duwatsu inda babu ƙasa sosai. Nan da nan, suka tsira domin ƙasar ba zurfi.
Osa seemneid pudenes kivisele pinnale, kus ei olnud eriti mulda. Madalas mullakihis hakkasid taimed kiiresti kasvama, aga kuna mullakiht ei olnud sügav,
6 Amma da rana ta taso, sai tsire-tsiren suka ƙone, suka yanƙwane, domin ba su da saiwa.
kõrvetas päike taimi. Kuna neil ei olnud päris juuri, närbusid taimed peagi.
7 Waɗansu irin suka fāɗi a cikin ƙaya. Da suka yi girma sai ƙaya suka shaƙe su, har ya sa ba su yi ƙwaya ba.
Osa seemneid pudenes ohakate sekka. Ohakad kasvasid suureks ja lämmatasid tärkava orase, nii et sellest ei tulnud midagi.
8 Har yanzu, waɗansu irin suka fāɗi a ƙasa mai kyau. Suka tsira, suka yi girma, suka ba da amfani, suka yi riɓi talatin-talatin, waɗansu sittin-sittin, waɗansu kuma ɗari-ɗari.”
Osa seemneid langes heale pinnasele, kus nad idanesid ja kasvasid ning andsid saagiks mõni kolmkümmend, mõni kuuskümmend ja mõni sada korda külvatust rohkem.
9 Sai Yesu ya ce, “Duk mai kunnen ji, yă ji.”
Kui teil on kuulmiseks kõrvad, siis kuulake, mida ma teile räägin.“
10 Lokacin da yake shi kaɗai, Sha Biyun, da kuma waɗanda suke kewaye da shi, suka tambaye shi game da misalan.
Kui Jeesus oli omapead, küsisid kaksteist jüngrit ja teised, kes olid koos temaga, mida need võrdlused tähendasid.
11 Sai ya ce musu, “An ba ku sanin asirin mulkin Allah. Amma ga waɗanda suke waje kuwa, kome sai da misalai.
Ta ütles neile: „Teie saate Jumala riigi mõistatusest aru. Kuid kõrvalseisjatel on ainult lood,
12 Saboda, “‘ko sun dinga duba, ba za su taɓa gane ba, kuma ko su dinga ji, ba za su taɓa fahimta ba, in ba haka ba, mai yiwuwa, su tuba, a gafarta musu!’”
nii et kuigi nad näevad, nad tegelikult ei „näe“, ja kuigi nad kuulevad, nad ei mõista, muidu pöörduksid nad minu poole ja saaksid andeks.“
13 Sai Yesu ya ce musu, “Ba ku fahimci wannan misali ba? Yaya za ku fahimci wani misali ke nan?
„Kas te ei saa sellest loost aru?“küsis Jeesus neilt. „Kui ei saa, kuidas te siis kõigist ülejäänud lugudest aru saate?
14 Manomi yakan shuka maganar Allah.
Külvaja külvab sõna.
15 Waɗansu mutane suna kama da irin da ya fāɗi a kan hanya, inda akan shuka maganar Allah. Da jin maganar, nan da nan sai Shaiɗan yă zo yă ɗauke maganar da aka shuka a zuciyarsu.
Seemned rajal, kuhu sõna külvati, kujutavad neid, kes kuulevad sõnumit, kuid siis tuleb kohe Saatan ja võtab ära sõna, mis neisse on külvatud.
16 Waɗansu suna kama da irin da aka shuka a wurare masu duwatsu, sukan ji maganar Allah, sukan kuma karɓe ta nan da nan da farin ciki.
Samal kombel kujutab kivine pind, kuhu seemned langesid, neid, kes kuulevad sõna ja võtavad selle kohe rõõmuga vastu.
17 Amma da yake ba su da saiwa, ba sa daɗewa. Da wahala ko tsanani ya tashi saboda maganar, nan da nan, sai su ja da baya.
Aga kuna neil ei ole päris juuri, jäävad nad püsima ainult veidikeseks ajaks, kuni tulevad probleemid või tagakiusamine, ja siis langevad nad kiiresti.
18 Har yanzu, waɗansu kamar irin da aka shuka cikin ƙaya, sukan ji maganar,
Ohakate sekka külvatu kujutab neid, kes kuulevad sõna,
19 amma damuwar wannan duniya, da son dukiya, da kuma kwaɗayin waɗansu abubuwa, sukan shiga, su shaƙe maganar, har su mai da ita marar amfani. (aiōn )
kuid selle maailma mured, rikkuse ahvatlus ja muud segavad asjaolud lämmatavad sõna kasvu ja see ei kanna vilja. (aiōn )
20 Waɗansu mutane kuwa suna kama da irin da aka shuka a ƙasa mai kyau, sukan ji maganar Allah, su kuma karɓa, sa’an nan kuma su fid da amfani riɓi talatin-talatin, ko sittin-sittin, ko ɗari-ɗari.”
Ent heale pinnasele külvatud seemned kujutavad neid, kes kuulevad sõna, võtavad selle vastu ja kannavad vilja, andes kolmkümmend, kuuskümmend ja sada korda rohkem kui külvati.
21 Sai ya ce musu, “Ko kukan kawo fitila ku rufe ta da murfi ko kuma ku sa ta a ƙarƙashin gado ne? Ba kukan sa ta a kan wurin ajiye fitila ba?
Kes paneb lambi ämbri või voodi alla?“küsis Jeesus neilt. „Ei, lamp pannakse üles lambijalale.
22 Duk abin da yake a ɓoye, dole za a fallasa shi. Duk abin da kuma yake a rufe, dole za a fitar da shi a fili.
Kõik, mis on varjatud, tuleb ilmsiks ja kõik, mis on salajas, saab avalikuks.
23 Duk mai kunnen ji, bari yă ji.”
Kui teil on kõrvad kuulmiseks, siis kuulake, mida ma räägin!
24 Ya ci gaba da cewa, “Ku lura da abin da kuke ji da kyau. Mudun da ka auna da shi, da shi za a auna maka, har ma a ƙara.
Pange tähele seda, mida te kuulete, “ütles ta neile, „sest teile antakse vastavalt sellele, kui palju tahate vastu võtta, mõõt mõõdu eest.
25 Duk wanda yake da shi, za a ƙara masa, duk wanda kuma ba shi da shi, ko abin da yake da shi ma, za a karɓe daga gare shi.”
Neile, kel juba on arusaamine, antakse rohkem, kuid neilt, kes ei taha teada, võetakse ära seegi vähene arusaamine, mis neil on.
26 Ya sāke cewa, “Mulkin Allah yana kama da haka. Wani mutum ya yafa iri a gona.
Jumala riik on nagu mees, kes külvab põllule seemet, “ütles Jeesus.
27 A kwana a tashi har irin yă tsiro, yă yi girma, bai kuwa santa yadda aka yi ba.
„Ta läheb magama ja tõuseb varakult üles ja nii iga päev, kuid ta ei tea, kuidas seeme idaneb ja tärkab.
28 Ƙasar da kanta takan ba da ƙwaya, da farko takan fid da ƙara, sa’an nan ta fid da kai, sa’an nan kan yă fid da ƙwaya.
Maa annab saaki iseenesest. Kõigepealt tuleb välja oras, seejärel viljapea ja siis küpse viljaga pea.
29 Da ƙwayan ya nuna, sai yă sa lauje yă yanka, domin lokacin girbi ya yi.”
Kui vili on küps, koristab põllumees selle sirbiga, sest saak on valmis.
30 Ya kuma ce, “Da me za mu kwatanta mulkin Allah, ko kuwa da wane misali za mu bayyana shi?
Millega võrrelda Jumala riiki? Missugust näidet kasutada?“küsis ta.
31 Yana kama da ƙwayar mustad, wadda ita ce ƙwaya mafi ƙanƙanta da akan shuka a gona.
„See on nagu sinepiseeme − kõige pisem seeme.
32 Duk da haka, in aka shuka ƙwayar, sai tă yi girma, tă zama mafi girma a itatuwan lambu. Har itacen yă kasance da manyan rassa, inda tsuntsayen sararin sama sukan iya huta a inuwarsa.”
Aga kui see maha külvata, siis kasvab sellest taim, mis on suurem kui teised taimed. Selle oksad on piisavalt suured, nii et linnud saavad seal varjus olla.“
33 Da misalai da yawa irin waɗannan, Yesu ya yi magana da su, daidai yadda za su iya fahimta.
Jeesus kasutas rahvale kõneledes palju selliseid näitlikke lugusid, et nad mõistaksid võimalikult hästi.
34 Ba abin da ya faɗa musu, da ba da misali ba. Amma lokacin da yake shi kaɗai tare da almajiransa, sai yă bayyana kome.
Õigupoolest kasutas ta avalikult rääkides üksnes jutustusi, kuid omaette olles selgitas ta oma jüngritele kõike.
35 A wannan rana, da yamma, sai ya ce wa almajiransa, “Mu ƙetare zuwa wancan hayi.”
Samal päeval hiljem − õhtul − ütles ta oma jüngritele: „Lähme üle mere teisele poole.“
36 Da suka bar taron, sai suka tafi tare da shi yadda yake, a cikin jirgin ruwa. Akwai waɗansu jiragen ruwa kuma tare da shi.
Jätnud rahvahulga maha, läksid jüngrid koos Jeesusega paati. Nende juures oli veel teisigi paate.
37 Sai babban hadari mai iska ya tashi, raƙuman ruwa suna ta bugun jirgin ruwan, har jirgin ruwan ya kusa yă cika da ruwa.
Peagi hakkas möllama kohutav torm, lained paiskusid vastu paati ja lõid vett sisse.
38 Yesu kuwa yana can baya, yana barci a kan katifa. Sai almajiran suka tashe shi suka ce masa, “Malam, ba ka kula ba ko mu nutse?”
Jeesus magas ahtris, pea padjale toetatud. Jüngrid äratasid ta kisendades: „Õpetaja, kas sa ei hooli sellest, et me oleme uppumas?“
39 Sai ya farka ya tsawata wa iskar, ya ce wa raƙuman ruwan, “Shiru! Ku natsu!” Sai iskar ta kwanta, kome kuma ya yi tsit.
Jeesus ärkas. Ta käskis tuulel vaibuda ja ütles lainetele: „Rahunege! Ärge möllake!“Tuul vaibus ja vesi jäi täiesti tüüneks.
40 Sai ya ce wa almajiransa, “Don me kuke tsoro haka? Har yanzu ba ku da bangaskiya ne?”
„Miks te nii väga kohkusite? Kas te ei ole õppinud mind usaldama?“küsis ta neilt.
41 Suka tsorata, suka ce wa juna, “Wane ne wannan? Har iska da raƙuman ruwa ma suna masa biyayya!”
Nad olid jahmunud ja ehmunud. Nad küsisid üksteiselt: „Kes ta ometi on? Isegi tuul ja lained kuuletuvad talle!“