< Markus 4 >

1 Har wa yau, Yesu ya fara koyarwa a bakin tafki. Domin taron da yake kewaye da shi mai girma ne sosai, sai ya shiga cikin jirgin ruwa, ya zauna a ciki a tafkin, dukan mutanen kuwa suna a gaɓar ruwan.
And He began to teach again by the sea-side, and there was gathered unto Him a great multitude; so that He went into a ship, and sat on board, and all the people were by the sea, upon the shore.
2 Ya koya musu abubuwa da yawa da misalai. A koyarwarsa kuwa ya ce,
And He taught them many things by similitudes, and said to them in his instruction,
3 “Ku saurara! Wani manomi ya fita don yă shuka irinsa.
hearken, Behold a sower went out to sow:
4 Da yana yafa irin, sai waɗansu suka fāɗi a kan hanya, tsuntsaye suka zo suka cinye su.
and in sowing, some fell by the way-side, and the birds came and ate it up:
5 Waɗansu suka fāɗi a wuri mai duwatsu inda babu ƙasa sosai. Nan da nan, suka tsira domin ƙasar ba zurfi.
and some fell on stony ground, where it had not much earth, and it sprang up immediately, because it had not depth of earth;
6 Amma da rana ta taso, sai tsire-tsiren suka ƙone, suka yanƙwane, domin ba su da saiwa.
but when the sun rose, it was burnt up, and withered because it had no root:
7 Waɗansu irin suka fāɗi a cikin ƙaya. Da suka yi girma sai ƙaya suka shaƙe su, har ya sa ba su yi ƙwaya ba.
and some fell among thorns, and the thorns grew up and choked it, and it yielded no fruit:
8 Har yanzu, waɗansu irin suka fāɗi a ƙasa mai kyau. Suka tsira, suka yi girma, suka ba da amfani, suka yi riɓi talatin-talatin, waɗansu sittin-sittin, waɗansu kuma ɗari-ɗari.”
and other fell on good ground, and yielded fruit springing up and increasing; and produced some thirty, and some sixty, and some an hundred-fold.
9 Sai Yesu ya ce, “Duk mai kunnen ji, yă ji.”
And He said unto them, He that hath ears to hear, let him hear.
10 Lokacin da yake shi kaɗai, Sha Biyun, da kuma waɗanda suke kewaye da shi, suka tambaye shi game da misalan.
And when He was apart from the multitude, those that were about Him with the twelve asked Him concerning the parable.
11 Sai ya ce musu, “An ba ku sanin asirin mulkin Allah. Amma ga waɗanda suke waje kuwa, kome sai da misalai.
And he said unto them, To you it is granted to know the mystery of the kingdom of God; but unto them that are without all things are delivered in parables:
12 Saboda, “‘ko sun dinga duba, ba za su taɓa gane ba, kuma ko su dinga ji, ba za su taɓa fahimta ba, in ba haka ba, mai yiwuwa, su tuba, a gafarta musu!’”
that in seeing they may see and not perceive, and in hearing they may hear and not understand, least they should be converted, and their sins be forgiven them.
13 Sai Yesu ya ce musu, “Ba ku fahimci wannan misali ba? Yaya za ku fahimci wani misali ke nan?
Then saith He unto them, Do ye not understand this parable? how then will ye understand all my other parables.
14 Manomi yakan shuka maganar Allah.
The sower is he that soweth the word. And these are they by the way-side:
15 Waɗansu mutane suna kama da irin da ya fāɗi a kan hanya, inda akan shuka maganar Allah. Da jin maganar, nan da nan sai Shaiɗan yă zo yă ɗauke maganar da aka shuka a zuciyarsu.
where the word is sown; but when they have heard it, Satan cometh immediately, and taketh away the word that was sown in their hearts.
16 Waɗansu suna kama da irin da aka shuka a wurare masu duwatsu, sukan ji maganar Allah, sukan kuma karɓe ta nan da nan da farin ciki.
And in like manner, they that are sown as on stony grounds are such, as when they hear the word,
17 Amma da yake ba su da saiwa, ba sa daɗewa. Da wahala ko tsanani ya tashi saboda maganar, nan da nan, sai su ja da baya.
immediately receive it with joy, but have no root in themselves, and so continue but for a short season: and then, when affliction cometh, or persecution on account of the word, they are as soon offended.
18 Har yanzu, waɗansu kamar irin da aka shuka cikin ƙaya, sukan ji maganar,
And those that are sown as among thorns, are these: such as hear the word indeed,
19 amma damuwar wannan duniya, da son dukiya, da kuma kwaɗayin waɗansu abubuwa, sukan shiga, su shaƙe maganar, har su mai da ita marar amfani. (aiōn g165)
but the cares of this world, and the deceitfulness of riches, and inordinate desires after other things entering in choke the word, and so it becometh unfruitful. (aiōn g165)
20 Waɗansu mutane kuwa suna kama da irin da aka shuka a ƙasa mai kyau, sukan ji maganar Allah, su kuma karɓa, sa’an nan kuma su fid da amfani riɓi talatin-talatin, ko sittin-sittin, ko ɗari-ɗari.”
And these are they who are like seed sown on good ground: such as hear the word, and receive it; and bring forth fruit, some thirty-fold, and some sixty, and some an hundred.
21 Sai ya ce musu, “Ko kukan kawo fitila ku rufe ta da murfi ko kuma ku sa ta a ƙarƙashin gado ne? Ba kukan sa ta a kan wurin ajiye fitila ba?
And He said unto them, Is a candle brought to be put under a bushel, or a bed, and not to be set on a candlestick?
22 Duk abin da yake a ɓoye, dole za a fallasa shi. Duk abin da kuma yake a rufe, dole za a fitar da shi a fili.
for there is nothing hidden, which may not be revealed; nor was there any thing concealed, but in order to become manifest.
23 Duk mai kunnen ji, bari yă ji.”
If any one hath ears to hear, let him hear.
24 Ya ci gaba da cewa, “Ku lura da abin da kuke ji da kyau. Mudun da ka auna da shi, da shi za a auna maka, har ma a ƙara.
And mind what ye hear: for with what measure ye mete, it shall be measured to you; and more shall be imparted to you that are observant:
25 Duk wanda yake da shi, za a ƙara masa, duk wanda kuma ba shi da shi, ko abin da yake da shi ma, za a karɓe daga gare shi.”
for whosoever hath, to him more shall be given; and he that hath not, even what he hath, or seemeth to have, shall be taken from him.
26 Ya sāke cewa, “Mulkin Allah yana kama da haka. Wani mutum ya yafa iri a gona.
And He said, The kingdom of God is as if a man should cast seed into the ground,
27 A kwana a tashi har irin yă tsiro, yă yi girma, bai kuwa santa yadda aka yi ba.
and sleep, and rise night and day, and the seed should spring up, and increase; he knows not how.
28 Ƙasar da kanta takan ba da ƙwaya, da farko takan fid da ƙara, sa’an nan ta fid da kai, sa’an nan kan yă fid da ƙwaya.
For the earth produces fruit of itself, first the blade, then the ear, then the full corn in the ear:
29 Da ƙwayan ya nuna, sai yă sa lauje yă yanka, domin lokacin girbi ya yi.”
but when the fruit is ripe, he immediately puts in the sickle, because the harvest is come.
30 Ya kuma ce, “Da me za mu kwatanta mulkin Allah, ko kuwa da wane misali za mu bayyana shi?
And He said, To what shall we compare the kingdom of God, or by what similitude shall we represent it?
31 Yana kama da ƙwayar mustad, wadda ita ce ƙwaya mafi ƙanƙanta da akan shuka a gona.
It is like to a grain of mustard-seed, which when it is sown in the ground, is one of the lest of all the seeds on the earth:
32 Duk da haka, in aka shuka ƙwayar, sai tă yi girma, tă zama mafi girma a itatuwan lambu. Har itacen yă kasance da manyan rassa, inda tsuntsayen sararin sama sukan iya huta a inuwarsa.”
but after it is sown, it grows up, and becomes greater than all herbs, and produces large branches, so that the birds of the air may lodge under it's shadow.
33 Da misalai da yawa irin waɗannan, Yesu ya yi magana da su, daidai yadda za su iya fahimta.
And in many such parables spake He the word to them, as they had ability to hear it: but spake not to them without a parable.
34 Ba abin da ya faɗa musu, da ba da misali ba. Amma lokacin da yake shi kaɗai tare da almajiransa, sai yă bayyana kome.
And He explained all to his disciples in private.
35 A wannan rana, da yamma, sai ya ce wa almajiransa, “Mu ƙetare zuwa wancan hayi.”
And the same day, in the evening, He saith to them, Let us go over to the other side.
36 Da suka bar taron, sai suka tafi tare da shi yadda yake, a cikin jirgin ruwa. Akwai waɗansu jiragen ruwa kuma tare da shi.
So they dismissed the multitude, and took Him as He was in the ship. But there were other small vessels likewise with Him.
37 Sai babban hadari mai iska ya tashi, raƙuman ruwa suna ta bugun jirgin ruwan, har jirgin ruwan ya kusa yă cika da ruwa.
And there arose a great storm of wind, and the waves beat into the ship, so that it was now almost full.
38 Yesu kuwa yana can baya, yana barci a kan katifa. Sai almajiran suka tashe shi suka ce masa, “Malam, ba ka kula ba ko mu nutse?”
And He was in the stern asleep on a pillow: and they awake Him, and say unto Him, Master, art thou under no concern that we are perishing?
39 Sai ya farka ya tsawata wa iskar, ya ce wa raƙuman ruwan, “Shiru! Ku natsu!” Sai iskar ta kwanta, kome kuma ya yi tsit.
And He rose and rebuked the wind, and said unto the sea, Peace, be still; and the wind ceased, and there was a great calm.
40 Sai ya ce wa almajiransa, “Don me kuke tsoro haka? Har yanzu ba ku da bangaskiya ne?”
And He said unto them, Why are ye so fearful? how! have ye no faith?
41 Suka tsorata, suka ce wa juna, “Wane ne wannan? Har iska da raƙuman ruwa ma suna masa biyayya!”
And they were exceedingly afraid, and said to one another, Who is this? that even the wind and the sea obey Him?

< Markus 4 >