< Markus 4 >
1 Har wa yau, Yesu ya fara koyarwa a bakin tafki. Domin taron da yake kewaye da shi mai girma ne sosai, sai ya shiga cikin jirgin ruwa, ya zauna a ciki a tafkin, dukan mutanen kuwa suna a gaɓar ruwan.
Again he began to teach beside the sea, and a large crowd gathered around him. He stepped into a boat that was on the sea, and he sat down in it. The whole crowd was on the shore beside the sea.
2 Ya koya musu abubuwa da yawa da misalai. A koyarwarsa kuwa ya ce,
He taught them many things in parables, and in his teaching, this is what he said to them.
3 “Ku saurara! Wani manomi ya fita don yă shuka irinsa.
“Listen, the farmer went out to sow his seed.
4 Da yana yafa irin, sai waɗansu suka fāɗi a kan hanya, tsuntsaye suka zo suka cinye su.
As he sowed, some seed fell on the road, and the birds came and devoured it.
5 Waɗansu suka fāɗi a wuri mai duwatsu inda babu ƙasa sosai. Nan da nan, suka tsira domin ƙasar ba zurfi.
Other seed fell on the rocky ground, where it did not have much soil. Immediately it sprang up, because it did not have deep soil.
6 Amma da rana ta taso, sai tsire-tsiren suka ƙone, suka yanƙwane, domin ba su da saiwa.
But when the sun rose, the plants were scorched, and because they had no root, they dried up.
7 Waɗansu irin suka fāɗi a cikin ƙaya. Da suka yi girma sai ƙaya suka shaƙe su, har ya sa ba su yi ƙwaya ba.
Other seed fell among the thorn plants. The thorn plants grew up and choked it, and it did not produce a crop.
8 Har yanzu, waɗansu irin suka fāɗi a ƙasa mai kyau. Suka tsira, suka yi girma, suka ba da amfani, suka yi riɓi talatin-talatin, waɗansu sittin-sittin, waɗansu kuma ɗari-ɗari.”
Other seed fell into good soil and it produced a crop growing up and increasing thirty, sixty, and even a hundred times.”
9 Sai Yesu ya ce, “Duk mai kunnen ji, yă ji.”
Then he said, “Whoever has ears to hear, let him hear!”
10 Lokacin da yake shi kaɗai, Sha Biyun, da kuma waɗanda suke kewaye da shi, suka tambaye shi game da misalan.
When Jesus was alone, those who were close to him and with the twelve asked him about the parables.
11 Sai ya ce musu, “An ba ku sanin asirin mulkin Allah. Amma ga waɗanda suke waje kuwa, kome sai da misalai.
He said to them, “To you is given the mystery of the kingdom of God. But to those outside everything is in parables,
12 Saboda, “‘ko sun dinga duba, ba za su taɓa gane ba, kuma ko su dinga ji, ba za su taɓa fahimta ba, in ba haka ba, mai yiwuwa, su tuba, a gafarta musu!’”
so that when they look, yes they look, but do not see, and so that when they hear, yes they hear, but do not understand, or else they would turn and God would forgive them.”
13 Sai Yesu ya ce musu, “Ba ku fahimci wannan misali ba? Yaya za ku fahimci wani misali ke nan?
Then he said to them, “Do you not understand this parable? How then will you understand all the other parables?
14 Manomi yakan shuka maganar Allah.
The farmer who sows his seed is the one who sows the word.
15 Waɗansu mutane suna kama da irin da ya fāɗi a kan hanya, inda akan shuka maganar Allah. Da jin maganar, nan da nan sai Shaiɗan yă zo yă ɗauke maganar da aka shuka a zuciyarsu.
These are the ones that fall beside the road, where the word was sown, but when they hear it, Satan immediately comes and takes away the word that was sown in them.
16 Waɗansu suna kama da irin da aka shuka a wurare masu duwatsu, sukan ji maganar Allah, sukan kuma karɓe ta nan da nan da farin ciki.
These are the ones that are sown on rocky ground, who, when they hear the word, immediately receive it with joy.
17 Amma da yake ba su da saiwa, ba sa daɗewa. Da wahala ko tsanani ya tashi saboda maganar, nan da nan, sai su ja da baya.
They have no root in themselves, but endure for a short time. Then tribulation or persecution comes because of the word, and immediately they stumble.
18 Har yanzu, waɗansu kamar irin da aka shuka cikin ƙaya, sukan ji maganar,
The others are the ones that were sown among the thorns. They hear the word,
19 amma damuwar wannan duniya, da son dukiya, da kuma kwaɗayin waɗansu abubuwa, sukan shiga, su shaƙe maganar, har su mai da ita marar amfani. (aiōn )
but the cares of the world, the deceitfulness of riches, and the desires of other things enter in and choke the word, and it does not produce a crop. (aiōn )
20 Waɗansu mutane kuwa suna kama da irin da aka shuka a ƙasa mai kyau, sukan ji maganar Allah, su kuma karɓa, sa’an nan kuma su fid da amfani riɓi talatin-talatin, ko sittin-sittin, ko ɗari-ɗari.”
Then those that were sown in the good soil are the ones who hear the word and receive it, and they produce crops—thirty, sixty, or a hundred times what was sown.”
21 Sai ya ce musu, “Ko kukan kawo fitila ku rufe ta da murfi ko kuma ku sa ta a ƙarƙashin gado ne? Ba kukan sa ta a kan wurin ajiye fitila ba?
Jesus said to them, “Do you bring a lamp inside the house to put it under a basket, or under the bed? You bring it in and you put it on a lampstand.
22 Duk abin da yake a ɓoye, dole za a fallasa shi. Duk abin da kuma yake a rufe, dole za a fitar da shi a fili.
For nothing is hidden that will not be known, and nothing is secret that will not come out into the open.
23 Duk mai kunnen ji, bari yă ji.”
If anyone has ears to hear, let him hear!”
24 Ya ci gaba da cewa, “Ku lura da abin da kuke ji da kyau. Mudun da ka auna da shi, da shi za a auna maka, har ma a ƙara.
He said to them, “Pay attention to what you hear, for the measure you use will be measured to you, and more will be added to you.
25 Duk wanda yake da shi, za a ƙara masa, duk wanda kuma ba shi da shi, ko abin da yake da shi ma, za a karɓe daga gare shi.”
Because whoever has, to him will be given more, and whoever does not have, even what he has will be taken.”
26 Ya sāke cewa, “Mulkin Allah yana kama da haka. Wani mutum ya yafa iri a gona.
He also said, “The kingdom of God is like a man who sows his seed on the ground.
27 A kwana a tashi har irin yă tsiro, yă yi girma, bai kuwa santa yadda aka yi ba.
He sleeps at night and gets up by day, and the seed sprouts and grows, though he does not know how.
28 Ƙasar da kanta takan ba da ƙwaya, da farko takan fid da ƙara, sa’an nan ta fid da kai, sa’an nan kan yă fid da ƙwaya.
The earth bears grain by itself: First the blade, then the ear, then the mature grain in the ear.
29 Da ƙwayan ya nuna, sai yă sa lauje yă yanka, domin lokacin girbi ya yi.”
When the crop is ripe, he immediately sends in the sickle because the harvest has come.”
30 Ya kuma ce, “Da me za mu kwatanta mulkin Allah, ko kuwa da wane misali za mu bayyana shi?
Again he said, “To what can we compare the kingdom of God, or what parable can we use to explain it?
31 Yana kama da ƙwayar mustad, wadda ita ce ƙwaya mafi ƙanƙanta da akan shuka a gona.
It is like a mustard seed which, when it is sown, is the smallest of all the seeds on earth.
32 Duk da haka, in aka shuka ƙwayar, sai tă yi girma, tă zama mafi girma a itatuwan lambu. Har itacen yă kasance da manyan rassa, inda tsuntsayen sararin sama sukan iya huta a inuwarsa.”
Yet, when it is sown, it grows and becomes greater than all the garden plants, and it forms large branches, so that the birds of heaven can make their nests in its shade.”
33 Da misalai da yawa irin waɗannan, Yesu ya yi magana da su, daidai yadda za su iya fahimta.
With many parables like this he spoke the word to them, as much as they were able to understand,
34 Ba abin da ya faɗa musu, da ba da misali ba. Amma lokacin da yake shi kaɗai tare da almajiransa, sai yă bayyana kome.
and he did not speak to them without a parable. But when he was alone, he explained everything to his own disciples.
35 A wannan rana, da yamma, sai ya ce wa almajiransa, “Mu ƙetare zuwa wancan hayi.”
On that day, when evening had come, he said to them, “Let us go over to the other side.”
36 Da suka bar taron, sai suka tafi tare da shi yadda yake, a cikin jirgin ruwa. Akwai waɗansu jiragen ruwa kuma tare da shi.
So they left the crowd, taking Jesus with them, just as he was, in the boat. There were other boats going along with him.
37 Sai babban hadari mai iska ya tashi, raƙuman ruwa suna ta bugun jirgin ruwan, har jirgin ruwan ya kusa yă cika da ruwa.
Just then a violent windstorm arose and the waves were breaking into the boat so that the boat was almost full of water.
38 Yesu kuwa yana can baya, yana barci a kan katifa. Sai almajiran suka tashe shi suka ce masa, “Malam, ba ka kula ba ko mu nutse?”
But Jesus himself was in the stern, asleep on a cushion. They woke him up, saying, “Teacher, do you not care that we are about to die?”
39 Sai ya farka ya tsawata wa iskar, ya ce wa raƙuman ruwan, “Shiru! Ku natsu!” Sai iskar ta kwanta, kome kuma ya yi tsit.
He got up, rebuked the wind, and said to the sea, “Peace! Be still!” Then the wind ceased, and there was a great calm.
40 Sai ya ce wa almajiransa, “Don me kuke tsoro haka? Har yanzu ba ku da bangaskiya ne?”
Then he said to them, “Why are you afraid? Do you still not have faith?”
41 Suka tsorata, suka ce wa juna, “Wane ne wannan? Har iska da raƙuman ruwa ma suna masa biyayya!”
They were filled with great fear and said to one another, “Who then is this, because even the wind and the sea obey him?”