< Markus 4 >
1 Har wa yau, Yesu ya fara koyarwa a bakin tafki. Domin taron da yake kewaye da shi mai girma ne sosai, sai ya shiga cikin jirgin ruwa, ya zauna a ciki a tafkin, dukan mutanen kuwa suna a gaɓar ruwan.
Another time Jesus began to teach [people] alongside Lake [Galilee. As he was doing that, a very large crowd gathered around him. Because people were jostling him], he got into a boat in the lake [so that he could speak to the crowd better. Then he sat in it and began to teach the crowd from the boat]. At the same time, the crowd was on the shore close to the lake.
2 Ya koya musu abubuwa da yawa da misalai. A koyarwarsa kuwa ya ce,
Then he taught them many parables. While he was teaching them, he told them [this]:
3 “Ku saurara! Wani manomi ya fita don yă shuka irinsa.
“Consider [well the meaning of this illustration]: A man/farmer went out [to his field] to sow [some seeds].
4 Da yana yafa irin, sai waɗansu suka fāɗi a kan hanya, tsuntsaye suka zo suka cinye su.
As he was scattering them [over the soil], some [of the] seeds fell on the path. Then some birds came and ate those seeds.
5 Waɗansu suka fāɗi a wuri mai duwatsu inda babu ƙasa sosai. Nan da nan, suka tsira domin ƙasar ba zurfi.
Other [seeds] fell on ground where there was not much soil [on top of] rock. Very soon the [seeds] sprouted because [the sun warmed] the moist soil quickly where it was not deep.
6 Amma da rana ta taso, sai tsire-tsiren suka ƙone, suka yanƙwane, domin ba su da saiwa.
But after the sun shone [on those young plants], they became scorched. Then they withered because they did not have [deep] roots.
7 Waɗansu irin suka fāɗi a cikin ƙaya. Da suka yi girma sai ƙaya suka shaƙe su, har ya sa ba su yi ƙwaya ba.
As the farmer sowed, other [seeds] fell on [ground that contained roots of] thorny plants. [The] seeds [grew, but] the thorny plants also grew up and crowded out [the] good [plants. So the plants] produced no grain.
8 Har yanzu, waɗansu irin suka fāɗi a ƙasa mai kyau. Suka tsira, suka yi girma, suka ba da amfani, suka yi riɓi talatin-talatin, waɗansu sittin-sittin, waɗansu kuma ɗari-ɗari.”
But as the farmer sowed, other [seeds] fell on good soil. As a result, they sprouted, they grew well, and then they produced [plenty of] grain. [Some] plants bore 30 [grains]. [Some] bore 60 [grains]. [Some] bore 100 [grains].”
9 Sai Yesu ya ce, “Duk mai kunnen ji, yă ji.”
Then Jesus said, “If you want to understand this [MTY], you should consider [carefully what I have just said].”
10 Lokacin da yake shi kaɗai, Sha Biyun, da kuma waɗanda suke kewaye da shi, suka tambaye shi game da misalan.
[Later], when only the twelve [disciples] and a few [other] people were with him, they asked him about the parables.
11 Sai ya ce musu, “An ba ku sanin asirin mulkin Allah. Amma ga waɗanda suke waje kuwa, kome sai da misalai.
He said to them, “People have not understood before [the new message] about how God wants to rule people’s lives. It is to you that this is being made known {that I am making this known}. But I tell about this [only] (in parables/figuratively) to those who have not [yet invited God to rule their lives].
12 Saboda, “‘ko sun dinga duba, ba za su taɓa gane ba, kuma ko su dinga ji, ba za su taɓa fahimta ba, in ba haka ba, mai yiwuwa, su tuba, a gafarta musu!’”
As a result [it is true what a prophet has written], Although they see [what I do], they do not perceive [what it means] [DOU]. Although they hear [what I say], they do not understand [what it means] [DOU]. So they do not (repent/turn away from their sinful behavior) in order that they would be forgiven {[God] would forgive them}.”
13 Sai Yesu ya ce musu, “Ba ku fahimci wannan misali ba? Yaya za ku fahimci wani misali ke nan?
He also said to them, “([I am disappointed that] you do not understand this illustration!/Can you not understand this illustration?) [RHQ] [If you do not understand] this, (you will certainly not understand any of the [other] illustrations!/how will you understand any of the [other] illustrations?) [RHQ] [Nevertheless, I will explain it to you].
14 Manomi yakan shuka maganar Allah.
[In the illustration that I told you], the man who sows [seeds represents someone who] declares God’s message [DOU].
15 Waɗansu mutane suna kama da irin da ya fāɗi a kan hanya, inda akan shuka maganar Allah. Da jin maganar, nan da nan sai Shaiɗan yă zo yă ɗauke maganar da aka shuka a zuciyarsu.
[Some people are like] the path on which [some of] the seeds fell. When they hear [the message], Satan comes at once and causes them to forget what they have heard.
16 Waɗansu suna kama da irin da aka shuka a wurare masu duwatsu, sukan ji maganar Allah, sukan kuma karɓe ta nan da nan da farin ciki.
[Some people are like the ground where the soil was not very deep over] rock. When they hear [God’s] message, they immediately accept it with joy.
17 Amma da yake ba su da saiwa, ba sa daɗewa. Da wahala ko tsanani ya tashi saboda maganar, nan da nan, sai su ja da baya.
But, because [the message does not penetrate deeply] [MET] [into their hearts/inner beings, they] believe it for [only a short time. They are like the plants that] did not have deep roots. When others treat such people badly or cause them to suffer because [they believe], those people [who are suffering] soon stop believing God’s message.
18 Har yanzu, waɗansu kamar irin da aka shuka cikin ƙaya, sukan ji maganar,
[Some people are like] the [soil that had roots of] thorny weeds in it. [Although] those people hear [God’s] message,
19 amma damuwar wannan duniya, da son dukiya, da kuma kwaɗayin waɗansu abubuwa, sukan shiga, su shaƙe maganar, har su mai da ita marar amfani. (aiōn )
they desire to be rich, and they desire to own many other things. So they worry [only] about material things. The result is that they forget [God’s] message and they do not do [the things that God wants them to do]. (aiōn )
20 Waɗansu mutane kuwa suna kama da irin da aka shuka a ƙasa mai kyau, sukan ji maganar Allah, su kuma karɓa, sa’an nan kuma su fid da amfani riɓi talatin-talatin, ko sittin-sittin, ko ɗari-ɗari.”
[But some people] are like the good soil. They hear [God’s] message and they accept it [and they believe] it. [Then they do the things that God wants them to do. They are like the good plants that produced] 30, 60 or 100 [grains].”
21 Sai ya ce musu, “Ko kukan kawo fitila ku rufe ta da murfi ko kuma ku sa ta a ƙarƙashin gado ne? Ba kukan sa ta a kan wurin ajiye fitila ba?
He also told them [another parable], saying, “(People certainly do not [light] an oil lamp and then bring it [in the house] in order that it may be put {someone may put it} under a container or under a bed./Would anyone [light] an oil lamp and then bring it [in the house] in order that it may be put {someone may put it} under a container or under a bed?) [RHQ] (No, [they light it] in order that it may be put {someone may put it} in a place [where it lights the house].[/Wouldn’t they light it] in order that it may be put {someone may put it} in a place [where it lights the house]?) [RHQ]
22 Duk abin da yake a ɓoye, dole za a fallasa shi. Duk abin da kuma yake a rufe, dole za a fitar da shi a fili.
[Similarly], there are some [parts of God’s message] that people do not know. [But he intends that] people will understand all the things that they do not know [now].
23 Duk mai kunnen ji, bari yă ji.”
If you want to understand this, you should consider [carefully] what you [have just heard].”
24 Ya ci gaba da cewa, “Ku lura da abin da kuke ji da kyau. Mudun da ka auna da shi, da shi za a auna maka, har ma a ƙara.
Then he said to them, “Consider carefully what you hear [me say to you], for [God] will let you [understand] to the same degree that you [consider what I say]. [He] will let you [understand] even more than that.
25 Duk wanda yake da shi, za a ƙara masa, duk wanda kuma ba shi da shi, ko abin da yake da shi ma, za a karɓe daga gare shi.”
Those who [consider what I say] and understand it, [God] will enable them to understand more. But those who do not [consider carefully what I say], they will forget even what they already know.”
26 Ya sāke cewa, “Mulkin Allah yana kama da haka. Wani mutum ya yafa iri a gona.
Jesus also said, “God [has the power to change] people who let him rule their lives. I [will illustrate how that can happen] [MET]. A man planted seeds in the ground.
27 A kwana a tashi har irin yă tsiro, yă yi girma, bai kuwa santa yadda aka yi ba.
Afterwards he slept each night and rose each day [without worrying about the seeds]. [During that time] the seeds sprouted and grew in a way that he did not understand, because by itself the soil [caused the plants to grow and produce grain].
28 Ƙasar da kanta takan ba da ƙwaya, da farko takan fid da ƙara, sa’an nan ta fid da kai, sa’an nan kan yă fid da ƙwaya.
First the stalks [appeared]. Then the heads [appeared]. Then the full kernels in the heads [appeared].
29 Da ƙwayan ya nuna, sai yă sa lauje yă yanka, domin lokacin girbi ya yi.”
As soon as the grain was ripe he sent [people] [MTY] to harvest it because it was time to harvest [the grain].”
30 Ya kuma ce, “Da me za mu kwatanta mulkin Allah, ko kuwa da wane misali za mu bayyana shi?
[Jesus told them] another [parable. He] said, “I will tell you [RHQ] how the [number of people] whose lives God rules in a new way [will continue to grow] (OR, each continue to have more and more influence in this world). I hope [RHQ] that this illustration will show this [to you].
31 Yana kama da ƙwayar mustad, wadda ita ce ƙwaya mafi ƙanƙanta da akan shuka a gona.
[You know what happens to] mustard seeds when we plant them. Though mustard seeds are among the smallest of seeds, [here in Israel] they become large plants.
32 Duk da haka, in aka shuka ƙwayar, sai tă yi girma, tă zama mafi girma a itatuwan lambu. Har itacen yă kasance da manyan rassa, inda tsuntsayen sararin sama sukan iya huta a inuwarsa.”
After they are planted, they grow up and become larger than the other garden plants. They put out big branches so that birds are able to make nests in their shade.”
33 Da misalai da yawa irin waɗannan, Yesu ya yi magana da su, daidai yadda za su iya fahimta.
Jesus used many such illustrations when he talked to the people about God. If they were able to understand [some, he kept telling them more].
34 Ba abin da ya faɗa musu, da ba da misali ba. Amma lokacin da yake shi kaɗai tare da almajiransa, sai yă bayyana kome.
He always used parables when he spoke to them. But he explained all [the illustrations] to his own disciples when he was alone with them.
35 A wannan rana, da yamma, sai ya ce wa almajiransa, “Mu ƙetare zuwa wancan hayi.”
On that same day, when the sun was setting, Jesus said to [his disciples], “Let’s cross over to the opposite side of [Lake Galilee in the boat].”
36 Da suka bar taron, sai suka tafi tare da shi yadda yake, a cikin jirgin ruwa. Akwai waɗansu jiragen ruwa kuma tare da shi.
So they left the crowd, [got in] the boat where Jesus [already] was, and left. [Other people] went with them in other boats.
37 Sai babban hadari mai iska ya tashi, raƙuman ruwa suna ta bugun jirgin ruwan, har jirgin ruwan ya kusa yă cika da ruwa.
A strong wind came up and the waves started coming into the boat! The boat was soon nearly full [of water]!
38 Yesu kuwa yana can baya, yana barci a kan katifa. Sai almajiran suka tashe shi suka ce masa, “Malam, ba ka kula ba ko mu nutse?”
Jesus was in the back part of the boat. He was sleeping, [with his head] on a cushion. So they woke him up and said to him, “Teacher! (You ought to be concerned that we are about to die!/Are you not concerned that we are about to die?) [RHQ]”
39 Sai ya farka ya tsawata wa iskar, ya ce wa raƙuman ruwan, “Shiru! Ku natsu!” Sai iskar ta kwanta, kome kuma ya yi tsit.
So Jesus got up and rebuked the wind. Then he said to the lake, “Be quiet! Be still! [DOU]” The wind [immediately] blowing and then [the lake] became very calm.
40 Sai ya ce wa almajiransa, “Don me kuke tsoro haka? Har yanzu ba ku da bangaskiya ne?”
He said to the disciples, “([I am disappointed that] you are afraid [like that]!/Why are you afraid [like that]?) [RHQ] Do you not yet believe [that I can protect you]?”
41 Suka tsorata, suka ce wa juna, “Wane ne wannan? Har iska da raƙuman ruwa ma suna masa biyayya!”
They were very awestruck. They said to one another, “[Not only do the demons obey this man, but] even the wind and the waves obey him! “(What kind of man is he?/This man is [not like ordinary] people!) [RHQ]”