< Markus 3 >

1 Wani lokaci, da ya sāke shiga majami’a, sai ga wani mutum mai shanyayyen hannu.
Et il entra encore dans la synagogue; et il y avait là un homme qui avait la main desséchée.
2 Waɗansu daga cikin mutane suna neman dalilin zargin Yesu, sai suka zuba masa ido, su ga ko zai warkar da shi a ranar Asabbaci.
Et ils l’observaient [pour voir] s’il le guérirait le jour de sabbat, afin de l’accuser.
3 Yesu ya ce wa mutumin mai shanyayyen hannun, “Tashi ka tsaya a gaban kowa.”
Et il dit à l’homme qui avait la main desséchée: Lève-toi là devant tous.
4 Sai Yesu ya tambaye su ya ce, “Me ya kamata a yi bisa ga doka, a ranar Asabbaci, a aikata alheri, ko a aikata mugunta, a ceci rai, ko a yi kisa?” Amma suka yi shiru.
Et il leur dit: Est-il permis de faire du bien le jour de sabbat, ou de faire du mal? de sauver la vie, ou de tuer? Mais ils gardaient le silence.
5 Sai ya kalle su da fushi, don taurin zuciyarsu ya ɓata masa rai sosai. Sai ya ce wa mutumin, “Miƙo hannunka.” Sai ya miƙa, hannunsa kuwa ya koma lafiyayye.
Et les ayant regardés à l’entour avec colère, étant attristé de l’endurcissement de leur cœur, il dit à l’homme: Étends ta main. Et il l’étendit, et sa main fut rétablie.
6 Sai Farisiyawa suka fita, suka fara ƙulla shawara da mutanen Hiridus yadda za su kashe Yesu.
Et les pharisiens, sortant aussitôt avec les hérodiens, tinrent conseil contre lui pour le faire périr.
7 Yesu da almajiransa suka janye zuwa tafkin, taro mai yawa kuwa daga Galili ya bi shi.
Et Jésus se retira avec ses disciples vers la mer; et une grande multitude le suivit de la Galilée, et de la Judée,
8 Mutane da yawa daga Yahudiya, da Urushalima, da Edom, da kuma yankunan da suke ƙetaren Urdun, da kewayen Taya, da Sidon suka zo wurinsa, don sun ji dukan abubuwan da yake yi.
et de Jérusalem, et de l’Idumée, et de par-delà le Jourdain. Et ceux des environs de Tyr et de Sidon, une grande multitude, ayant entendu les choses qu’il faisait, vinrent vers lui.
9 Saboda taron, sai ya ce wa almajiransa su shirya masa ƙaramin jirgin ruwa, don kada mutane su matse shi.
Et il dit à ses disciples qu’un petit bateau soit là à sa disposition, à cause de la foule, afin qu’elle ne le presse pas;
10 Gama ya warkar da mutane da yawa, masu cututtuka suka yi ta ƙoƙarin zuwa gaba, don su taɓa shi.
car il en guérit beaucoup, de sorte que tous ceux qui étaient affligés de quelque fléau se jetaient sur lui afin de le toucher.
11 Duk sa’ad da mugayen ruhohi suka gan shi, sai fāɗi a gabansa, su ɗaga murya, su ce, “Kai Ɗan Allah ne.”
Et les esprits immondes, quand ils le voyaient, se jetaient devant lui et s’écriaient, disant: Tu es le Fils de Dieu.
12 Amma yakan tsawata musu, kada su shaida ko wane ne shi.
Et il leur défendait très expressément de le faire connaître.
13 Yesu ya hau gefen wani dutse, ya kira waɗanda yake so, suka kuma zo wurinsa.
Et il monte sur une montagne, et il appelle ceux qu’il voulait; et ils vinrent à lui;
14 Ya naɗa sha biyu, ya kira su manzanni don su kasance tare da shi, domin kuma yă aike su yin wa’azi,
et il en établit douze pour être avec lui, et pour les envoyer prêcher,
15 don kuma su sami ikon fitar da aljanu.
et pour avoir autorité [de guérir les maladies et] de chasser les démons;
16 Ga sha biyun da ya naɗa. Siman (wanda ya ba shi suna Bitrus);
et il surnomma Simon, Pierre;
17 Yaƙub ɗan Zebedi da kuma ɗan’uwansa Yohanna (ga waɗannan kuwa ya sa musu suna Buwarnajis, wato, “’ya’yan tsawa”);
et Jacques le [fils] de Zébédée et Jean le frère de Jacques, et il les surnomma Boanergès, ce qui est: fils de tonnerre;
18 Andarawus, Filibus, Bartolomeyu, Mattiyu, Toma, Yaƙub ɗan Alfayus, Taddayus, Siman wanda ake kira Zilot,
et André, et Philippe, et Barthélemy, et Matthieu, et Thomas, et Jacques le [fils] d’Alphée, et Thaddée, et Simon le Cananéen,
19 da kuma Yahuda Iskariyot, wanda ya bashe Yesu.
et Judas Iscariote, qui aussi le livra.
20 Sai Yesu ya shiga wani gida, taro kuma ya sāke haɗuwa, har shi da almajiransa ma ba su sami damar cin abinci ba.
Et ils viennent à la maison; et la foule s’assemble de nouveau, en sorte qu’ils ne pouvaient pas même manger leur pain.
21 Da’yan’uwansa suka sami wannan labari, sai suka tafi don su dawo da shi, suna cewa, “Ai, ya haukace.”
Et ses proches, ayant entendu cela, sortirent pour se saisir de lui; car ils disaient: Il est hors de sens.
22 Malaman dokokin da suka zo daga Urushalima suka ce, “Ai, yana da Be’elzebub! Da ikon sarkin aljanu yake fitar da aljanu.”
Et les scribes qui étaient descendus de Jérusalem, dirent: Il a Béelzébul; et: Par le chef des démons, il chasse les démons.
23 Sai Yesu ya kira su, ya yi musu magana da misalai ya ce, “Yaya Shaiɗan zai fitar da Shaiɗan?
Et les ayant appelés, il leur dit par des paraboles: Comment Satan peut-il chasser Satan?
24 In mulki yana gāba da kansa, wannan mulki ba zai tsaya ba.
Et si un royaume est divisé contre lui-même, ce royaume-là ne peut pas subsister.
25 In gida yana gāba da kansa, wannan gida ba zai tsaya ba.
Et si une maison est divisée contre elle-même, cette maison-là ne peut pas subsister.
26 In kuwa Shaiɗan yana gāba da kansa, ya kuma rabu biyu, ba zai tsaya ba, ƙarshensa ya zo ke nan.
Et si Satan s’élève contre lui-même et est divisé, il ne peut pas subsister, mais il vient à sa fin.
27 Tabbatacce, ba mai shiga gidan mai ƙarfi yă kwashe dukiyarsa, sai bayan ya daure mai ƙarfin, sa’an nan zai iya yin fashin gidansa.
Nul ne peut entrer dans la maison de l’homme fort, et piller ses biens, si premièrement il n’a lié l’homme fort; et alors il pillera sa maison.
28 Gaskiya nake gaya muku, za a gafarta duk zunubai da kuma saɓon mutane suka yi.
En vérité, je vous dis que tous les péchés seront pardonnés aux fils des hommes, et les paroles injurieuses, quelles qu’elles soient, par lesquelles ils blasphèment;
29 Amma duk wanda ya saɓi Ruhu Mai Tsarki, ba za a taɓa gafara masa ba. Ya aikata madawwamin zunubi ke nan.” (aiōn g165, aiōnios g166)
mais quiconque proférera des paroles injurieuses contre l’Esprit Saint n’aura jamais de pardon; mais il est passible du jugement éternel. (aiōn g165, aiōnios g166)
30 Ya faɗi haka domin suna cewa, “Yana da mugun ruhu.”
C’était parce qu’ils disaient: Il a un esprit immonde.
31 Sai mahaifiyar Yesu tare da’yan’uwansa suka iso. Suna tsaye a waje, sai suka aiki wani ciki yă kira shi.
Ses frères et sa mère donc viennent; et se tenant dehors, ils l’envoyèrent appeler;
32 Taron yana zaune kewaye da shi, sai suka ce masa, “Mahaifiyarka da’yan’uwanka suna waje, suna nemanka.”
et la foule était assise autour de lui. Et on lui dit: Voici, ta mère et tes frères, là dehors, te cherchent.
33 Ya yi tambaya ya ce, “Su wane ne mahaifiyata, da’yan’uwana?”
Et il leur répondit, disant: Qui est ma mère, ou [qui sont] mes frères?
34 Sai ya dubi waɗanda suke zaune kewaye da shi ya ce, “Ga mahaifiyata da’yan’uwana!
Et regardant tout à l’entour ceux qui étaient assis autour de lui, il dit: Voici ma mère et mes frères;
35 Duk wanda yake aikata nufin Allah, shi ne ɗan’uwana, da’yar’uwata, da kuma mahaifiyata.”
car quiconque fera la volonté de Dieu, celui-là est mon frère, et ma sœur, et ma mère.

< Markus 3 >