< Markus 3 >

1 Wani lokaci, da ya sāke shiga majami’a, sai ga wani mutum mai shanyayyen hannu.
And He entered again into the synagogue, and there was there a man having the hand withered,
2 Waɗansu daga cikin mutane suna neman dalilin zargin Yesu, sai suka zuba masa ido, su ga ko zai warkar da shi a ranar Asabbaci.
and they were watching Him, whether on the Sabbaths He will heal him, that they might accuse Him.
3 Yesu ya ce wa mutumin mai shanyayyen hannun, “Tashi ka tsaya a gaban kowa.”
And He says to the man having the hand withered, “Rise up in the midst.”
4 Sai Yesu ya tambaye su ya ce, “Me ya kamata a yi bisa ga doka, a ranar Asabbaci, a aikata alheri, ko a aikata mugunta, a ceci rai, ko a yi kisa?” Amma suka yi shiru.
And He says to them, “Is it lawful on the Sabbaths to do good, or to do evil? To save life, or to kill?” But they were silent.
5 Sai ya kalle su da fushi, don taurin zuciyarsu ya ɓata masa rai sosai. Sai ya ce wa mutumin, “Miƙo hannunka.” Sai ya miƙa, hannunsa kuwa ya koma lafiyayye.
And having looked around on them with anger, being grieved for the hardness of their heart, He says to the man, “Stretch forth your hand”; and he stretched forth, and his hand was restored whole as the other;
6 Sai Farisiyawa suka fita, suka fara ƙulla shawara da mutanen Hiridus yadda za su kashe Yesu.
and the Pharisees having gone forth, immediately, with the Herodians, were taking counsel against Him how they might destroy Him.
7 Yesu da almajiransa suka janye zuwa tafkin, taro mai yawa kuwa daga Galili ya bi shi.
And Jesus withdrew with His disciples to the sea, and a great multitude from Galilee followed Him, and from Judea,
8 Mutane da yawa daga Yahudiya, da Urushalima, da Edom, da kuma yankunan da suke ƙetaren Urdun, da kewayen Taya, da Sidon suka zo wurinsa, don sun ji dukan abubuwan da yake yi.
and from Jerusalem, and from Idumea and beyond the Jordan; and they around Tyre and Sidon—a great multitude—having heard how He was doing great things, came to Him.
9 Saboda taron, sai ya ce wa almajiransa su shirya masa ƙaramin jirgin ruwa, don kada mutane su matse shi.
And He said to His disciples that a little boat may wait on Him, because of the multitude, that they may not press on Him,
10 Gama ya warkar da mutane da yawa, masu cututtuka suka yi ta ƙoƙarin zuwa gaba, don su taɓa shi.
for He healed many, so that they threw themselves on Him, in order to touch Him—as many as had plagues;
11 Duk sa’ad da mugayen ruhohi suka gan shi, sai fāɗi a gabansa, su ɗaga murya, su ce, “Kai Ɗan Allah ne.”
and the unclean spirits, when they were seeing Him, were falling down before Him, and were crying, saying, “You are the Son of God”;
12 Amma yakan tsawata musu, kada su shaida ko wane ne shi.
and many times He was charging them that they might not make Him apparent.
13 Yesu ya hau gefen wani dutse, ya kira waɗanda yake so, suka kuma zo wurinsa.
And He goes up to the mountain, and calls near whom He willed, and they went away to Him;
14 Ya naɗa sha biyu, ya kira su manzanni don su kasance tare da shi, domin kuma yă aike su yin wa’azi,
and He appointed twelve, that they may be with Him, and that He may send them forth to preach,
15 don kuma su sami ikon fitar da aljanu.
and to have power to heal the sicknesses, and to cast out the demons.
16 Ga sha biyun da ya naɗa. Siman (wanda ya ba shi suna Bitrus);
And He put on Simon the name Peter;
17 Yaƙub ɗan Zebedi da kuma ɗan’uwansa Yohanna (ga waɗannan kuwa ya sa musu suna Buwarnajis, wato, “’ya’yan tsawa”);
and James of Zebedee, and John the brother of James, and He put on them names—Boanerges, that is, “Sons of thunder”;
18 Andarawus, Filibus, Bartolomeyu, Mattiyu, Toma, Yaƙub ɗan Alfayus, Taddayus, Siman wanda ake kira Zilot,
and Andrew, and Philip, and Bartholomew, and Matthew, and Thomas, and James of Alpheus, and Thaddeus, and Simon the Zealot,
19 da kuma Yahuda Iskariyot, wanda ya bashe Yesu.
and Judas Iscariot, who also delivered Him up; and they come into a house.
20 Sai Yesu ya shiga wani gida, taro kuma ya sāke haɗuwa, har shi da almajiransa ma ba su sami damar cin abinci ba.
And a multitude comes together again, so that they are not even able to eat bread;
21 Da’yan’uwansa suka sami wannan labari, sai suka tafi don su dawo da shi, suna cewa, “Ai, ya haukace.”
and those alongside Him having heard, went forth to lay hold on Him, for they said that He was beside Himself,
22 Malaman dokokin da suka zo daga Urushalima suka ce, “Ai, yana da Be’elzebub! Da ikon sarkin aljanu yake fitar da aljanu.”
and the scribes who [are] from Jerusalem having come down, said, “He has Beelzebul,” and, “By the ruler of the demons He casts out the demons.”
23 Sai Yesu ya kira su, ya yi musu magana da misalai ya ce, “Yaya Shaiɗan zai fitar da Shaiɗan?
And having called them near, He said to them in allegories, “How is Satan able to cast out Satan?
24 In mulki yana gāba da kansa, wannan mulki ba zai tsaya ba.
And if a kingdom is divided against itself, that kingdom cannot be made to stand;
25 In gida yana gāba da kansa, wannan gida ba zai tsaya ba.
and if a house is divided against itself, that house cannot be made to stand;
26 In kuwa Shaiɗan yana gāba da kansa, ya kuma rabu biyu, ba zai tsaya ba, ƙarshensa ya zo ke nan.
and if Satan rose against himself, and has been divided, he cannot be made to stand, but has an end.
27 Tabbatacce, ba mai shiga gidan mai ƙarfi yă kwashe dukiyarsa, sai bayan ya daure mai ƙarfin, sa’an nan zai iya yin fashin gidansa.
No one is able to spoil the vessels of the strong man, having entered into his house, if first he may not bind the strong man, and then he will spoil his house.
28 Gaskiya nake gaya muku, za a gafarta duk zunubai da kuma saɓon mutane suka yi.
Truly I say to you that all sins will be forgiven to the sons of men, and slanders with which they might have slandered,
29 Amma duk wanda ya saɓi Ruhu Mai Tsarki, ba za a taɓa gafara masa ba. Ya aikata madawwamin zunubi ke nan.” (aiōn g165, aiōnios g166)
but whoever may slander in regard to the Holy Spirit has no forgiveness—throughout the age, but is in danger of continuous judgment; (aiōn g165, aiōnios g166)
30 Ya faɗi haka domin suna cewa, “Yana da mugun ruhu.”
because they said, He has an unclean spirit.”
31 Sai mahaifiyar Yesu tare da’yan’uwansa suka iso. Suna tsaye a waje, sai suka aiki wani ciki yă kira shi.
Then His brothers and mother come, and standing outside, they sent to Him, calling Him,
32 Taron yana zaune kewaye da shi, sai suka ce masa, “Mahaifiyarka da’yan’uwanka suna waje, suna nemanka.”
and a multitude was sitting around Him, and they said to Him, “Behold, Your mother and Your brothers seek You outside.”
33 Ya yi tambaya ya ce, “Su wane ne mahaifiyata, da’yan’uwana?”
And He answered them, saying, “Who is My mother, or My brothers?”
34 Sai ya dubi waɗanda suke zaune kewaye da shi ya ce, “Ga mahaifiyata da’yan’uwana!
And having looked around in a circle to those sitting around Him, He says, “Behold, My mother and My brothers!
35 Duk wanda yake aikata nufin Allah, shi ne ɗan’uwana, da’yar’uwata, da kuma mahaifiyata.”
For whoever may do the will of God, he is My brother, and My sister, and mother.”

< Markus 3 >