< Markus 2 >
1 Bayan’yan kwanaki, da Yesu ya sāke shiga Kafarnahum, sai mutane suka ji labarin zuwansa gida.
Quelques jours après, il entra de nouveau à Capernaüm, et l'on apprit qu'il était chez lui.
2 Mutane suka taru da yawa har ma babu wuri, ko a bakin ƙofa ma, sai ya yi musu wa’azin bishara.
Aussitôt, plusieurs se rassemblèrent, au point qu'il n'y avait plus de place, pas même autour de la porte; et il leur adressa la parole.
3 Waɗansu mutum huɗu suka zo wajensa ɗauke da wani shanyayye.
Quatre personnes vinrent, lui portant un paralytique.
4 Da ba su iya kai shi wurin Yesu ba, saboda taron, sai suka buɗe rufin gidan saman, bisa daidai inda Yesu yake. Bayan da suka huda rami, sai suka saukar da shanyayyen, kwance a kan tabarmarsa.
Comme ils ne pouvaient s'approcher de lui à cause de la foule, ils enlevèrent le toit où il se trouvait. Après l'avoir brisé, ils descendirent la natte sur laquelle était couché le paralytique.
5 Da Yesu ya ga bangaskiyarsu, sai ya ce wa shanyayyen, “Saurayi, an gafarta zunubanka.”
Jésus, voyant leur foi, dit au paralytique: « Mon fils, tes péchés te sont pardonnés. »
6 To, waɗansu malaman dokoki da suke zaune a wurin, suka yi tunani a zuciyarsu, suna cewa,
Mais quelques-uns des scribes, assis là, raisonnaient dans leur cœur:
7 “Me ya sa mutumin nan yake magana haka? Yana saɓo! Wane ne zai iya gafarta zunubai, in ba Allah kaɗai ba?”
« Pourquoi cet homme profère-t-il de tels blasphèmes? Qui peut pardonner les péchés, sinon Dieu seul? »
8 Nan da nan, Yesu ya gane a ruhunsa abin da suke tunani a zuciyarsu, sai ya ce musu, “Me ya sa kuke tunanin waɗannan abubuwa?
Aussitôt, Jésus, voyant dans son esprit qu'ils raisonnaient ainsi en eux-mêmes, leur dit: « Pourquoi raisonnez-vous ainsi dans vos cœurs?
9 Wanne ya fi sauƙi, a ce wa shanyayyen, ‘An gafarta zunubanka,’ ko a ce, ‘Tashi, ɗauki tabarmarka ka yi tafiya’?
Lequel est le plus facile, de dire au paralytique: Tes péchés sont pardonnés, ou de lui dire: Lève-toi, prends ton lit et marche?
10 Amma don ku san cewa, Ɗan Mutum yana da iko a duniya yă gafarta zunubai.” Sai ya ce wa shanyayyen,
Mais, afin que vous sachiez que le Fils de l'homme a sur la terre le pouvoir de pardonner les péchés, il dit au paralytique:
11 “Ina ce maka, tashi, ɗauki tabarmarka, ka tafi gida.”
Je te le dis, lève-toi, prends ton lit et va dans ta maison.
12 Sai ya tashi, ya ɗauki tabarmarsa, ya yi tafiyarsa a gabansu duka. Wannan ya ba wa kowa mamaki, suka kuma ɗaukaka Allah suna cewa, “Ba mu taɓa ganin abu haka ba!”
Il se leva, prit aussitôt le tapis et sortit devant eux tous, de sorte qu'ils furent tous stupéfaits et glorifièrent Dieu, en disant: « Nous n'avons jamais rien vu de tel! »
13 Yesu ya sāke tafiya bakin tafkin. Taro mai yawa ya zo wurinsa, sai ya fara koya musu.
Il sortit de nouveau au bord de la mer. Toute la foule venait à lui, et il les enseignait.
14 Yana cikin tafiya, sai ya ga Lawi, ɗan Alfayus zaune a inda ake karɓar haraji. Yesu ya ce masa, “Bi ni.” Sai Lawi ya tashi, ya bi shi.
Comme il passait, il vit Lévi, fils d'Alphée, assis au bureau des impôts. Il lui dit: « Suis-moi. » Et il se leva et le suivit.
15 Yayinda Yesu yake cin abinci a gidan Lawi, sai masu karɓar haraji da “masu zunubi” da yawa, suka zo suka ci tare da shi da almajiransa, gama akwai mutane da yawa da suka bi shi.
Il était à table dans sa maison, et beaucoup de publicains et de pécheurs étaient assis avec Jésus et ses disciples, car ils étaient nombreux, et ils le suivaient.
16 Da malaman dokoki, waɗanda su ma Farisiyawa ne, suka ga yana ci tare da masu “zunubi” da masu karɓar haraji, sai suka tambayi almajiransa, suka ce, “Me ya sa yake ci tare da masu karɓar haraji da masu zunubi?”
Les scribes et les pharisiens, voyant qu'il mangeait avec les pécheurs et les publicains, dirent à ses disciples: « Pourquoi mange-t-il et boit-il avec les publicains et les pécheurs? »
17 Da jin wannan, Yesu ya ce musu, “Ai, masu lafiya ba sa bukatar likita, sai dai marasa lafiya. Ban zo domin in kira masu adalci ba, sai dai masu zunubi.”
Ayant entendu cela, Jésus leur dit: « Ceux qui sont en bonne santé n'ont pas besoin de médecin, mais ceux qui sont malades. Je suis venu non pas pour appeler les justes, mais les pécheurs à la repentance. »
18 To, almajiran Yohanna da na Farisiyawa suna azumi, sai waɗansu mutane suka zo suka tambayi Yesu, suka ce, “Yaya almajiran Yohanna da na Farisiyawa suna azumi, amma almajiranka ba sa yi?”
Les disciples de Jean et les pharisiens étaient en train de jeûner, et ils vinrent lui demander: « Pourquoi les disciples de Jean et les disciples des pharisiens jeûnent-ils, mais tes disciples ne jeûnent pas? »
19 Yesu ya amsa ya ce, “Yaya abokan ango za su yi azumi, sa’ad da yana tare da su? Ai, ba za su yi ba, muddin yana tare da su.
Jésus leur dit: « Les mariés peuvent-ils jeûner tant que l'époux est avec eux? Tant qu'ils ont l'époux avec eux, ils ne peuvent pas jeûner.
20 Ai, lokaci yana zuwa da za a ɗauke musu angon. A sa’an nan ne fa za su yi azumi.
Mais les jours viendront où l'époux leur sera enlevé, et alors ils jeûneront en ce jour-là.
21 “Ba mai facin sabon ƙyalle a tsohuwar riga. In ya yi haka, sabon ƙyallen zai yage daga tsohuwar, yagewar kuwa za tă zama da muni.
Personne ne coud une pièce de tissu non trempé sur un vieux vêtement, sinon la pièce se rétracte et le nouveau se détache du vieux, et le trou est pire.
22 Ba wanda yakan zuba sabon ruwan inabi a tsofaffin salkuna. In ya yi haka, ruwan inabin zai farfashe salkunan, yă yi hasarar ruwan inabin, salkunan kuma su lalace. A’a, yakan zuba sabon ruwan inabin a sababbin salkuna.”
Personne ne met du vin nouveau dans de vieilles outres, sinon le vin nouveau fait éclater les outres, et le vin se répand, et les outres sont détruites; mais on met du vin nouveau dans des outres neuves. »
23 Wata ranar Asabbaci, Yesu yana ratsa gonakin hatsi, sai almajiransa da suke tafiya tare da shi, suka fara kakkarya waɗansu kan hatsi.
Il traversait les champs de blé, le jour du sabbat, et ses disciples se mirent à arracher les épis.
24 Farisiyawa suka ce masa, “Duba, me ya sa suke yin abin da doka ta hana a yi, a ranar Asabbaci?”
Les pharisiens lui dirent: « Voici, pourquoi font-ils ce qui n'est pas permis le jour du sabbat? »
25 Ya amsa ya ce, “Ashe, ba ku taɓa karanta abin da Dawuda ya yi ba, sa’ad da shi da abokan tafiyarsa suka ji yunwa, suna kuma cikin bukata?
Il leur dit: « N'avez-vous jamais lu ce que fit David, quand il était dans le besoin et qu'il avait faim, et ceux qui étaient avec lui?
26 Ya shiga gidan Allah a zamanin Abiyatar babban firist, ya ci keɓaɓɓen burodin nan, ya kuma ba wa abokan tafiyarsa abin da firistoci kaɗai sukan ci bisa ga doka?”
Comment il entra dans la maison de Dieu au moment où Abiathar, le grand prêtre, mangea le pain de proposition, qu'il n'est pas permis de manger, sauf pour les prêtres, et en donna aussi à ceux qui étaient avec lui? »
27 Sai ya ce musu, “An yi Asabbaci saboda mutum ne, ba mutum saboda Asabbaci ba.
Il leur dit: « Le sabbat a été fait pour l'homme, et non l'homme pour le sabbat.
28 Don haka, Ɗan Mutum Ubangiji ne, har ma da na Asabbaci.”
C'est pourquoi le Fils de l'homme est maître même du sabbat. »