< Markus 16 >
1 Da Asabbaci ya wuce, sai Maryamu Magdalin, Maryamu mahaifiyar Yaƙub, da kuma Salome suka sayi kayan ƙanshi domin su je su shafa wa jikin Yesu.
Vugusilele usikhe gwa khu gatalukha, Maliamu Magdalene nu Maliamu umamaye u Yakobo, nu Salome, vagulile imono inonu, valute vakhabakhe umbili gwa Yesu khujili ya khusiala.
2 A ranar farko ta mako, da sassafe, bayan fitowar rana, suna kan hanyarsu zuwa kabarin ke nan,
Vukilo ee sikhu ya lutanchi ya juma, vakhaluta khuli pumba vu eilinchuva lihuma.
3 sai suka tambaye juna suka ce, “Wane ne zai gungura mana dutsen daga bakin kabarin?”
Vakhanchovana vavo khu vavo, “Veni unchii mulipumba?”
4 Amma da suka ɗaga kai, sai suka ga cewa, an riga an gungura dutsen. Dutsen kuwa babba ne.
Vuvilola, vakha vona umunu akihwusye eelue eeliliale livaha fincho.
5 Da suna shiga cikin kabarin, sai suka ga wani saurayi sanye da farar riga, yana zaune a hannun dama, sai suka firgita.
Vakhiingila mulipumba vakhambona ukheijana afualile eimienda eimivalafu alamile eikhei vakho kyandwuo, vakhasuniiga.
6 Ya ce, “Kada ku firgita. Kuna neman Yesu Banazare wanda aka gicciye ne. Ya tashi! Ba ya nan. Ku dubi inda aka kwantar da shi.
Akhata msite, “Ukhuduada. Mukhundonda u Yesu, vakhu Nazaleti, uviakhabudiwe. Anchukhite! Asipali apa. Lola upu vakhagoninc'he.
7 Amma ku tafi ku gaya wa almajiransa da kuma Bitrus cewa, ‘Ya sha gabanku zuwa Galili. Can za ku gan shi, kamar yadda ya faɗa muku.’”
Lutaga mukha vavule avakongi vamwene nu Peteli ukhuta avalonguule ukhuluka khuu Galilaya. Ukhu munchi khumbona, nduvuakhavavulile.”
8 Da rawan jiki da kuma ruɗewa, matan suka fita a guje daga kabarin. Ba su kuwa gaya wa kowa ba, don suna tsoro.
Vakhahega nu khunyila ukhuhuma mulipumba; vakhatetema nukhuswiiga savakhanchova kheinu khumunu vevoni pakhuva vadwadile sana.
9 (note: The most reliable and earliest manuscripts do not include Mark 16:9-20.) Da Yesu ya tashi daga matattu da safe, a ranar farko ta mako, ya fara bayyana ga Maryamu Magdalin, wadda ya fitar da aljanu bakwai daga cikinta.
(note: The most reliable and earliest manuscripts do not include Mark 16:9-20.) Vukilo eisikhu ya lutanchii mujuma, vuanchukhile akhang'umila Umaliamu Magdalene, uviuyu ukhuhuma khumwene ang'uuminche imipepo saba.
10 Ta je ta gaya wa waɗanda dā suke tare da shi, waɗanda kuma suke makoki da kuka.
Abhahega nukhuvavuli avanine avavale paninie nave vuisikhitikha nu khulila.
11 Da suka ji cewa Yesu yana da rai, har ma ta gan shi, ba su gaskata ba.
Vakhapulikha ukhuta muumi avonikhe lakhuini savakhanumi.
12 Daga baya Yesu ya bayyana a wani kamanni dabam ga biyunsu, yayinda suke tafiya ƙauye.
Vuugahumile ago, akhavone kha hange khuvanu vavili, vuigenda mukhei lung.
13 Waɗannan kuwa suka koma suka shaida wa sauran, amma su ma ba su gaskata ba.
Vakhaluta khukho vavula avakongi avange vavo vakhasigile, pope savakhakela.
14 Bayan haka, Yesu ya bayyana ga Sha Ɗayan, yayinda suke cin abinci. Ya tsawata musu a kan rashin bangaskiyarsu, da yadda suka ƙi gaskata waɗanda suka gan shi bayan ya tashi.
U Yesu pongela akhahumila khuvala kheinchigo na yumo vuvalagine pa tisi akhava dukha pa khu sila ukhueidekha khwa vene, nuvukhe fuewa numbula ncha vene pakhuva savalei khuueidekha vuvikhuvavula vala avalole vu anchukhile ukhuhuma khuu vufye.
15 Ya ce, musu, “Ku tafi cikin dukan duniya, ku yi wa’azin bishara ga dukan halitta.
Akhata, “Mulutage mukhilunga kyooni nu khulumbilila eilimenyu lya Nguluve khukhila munu.
16 Duk wanda ya gaskata, aka kuma yi masa baftisma, zai sami ceto. Amma duk wanda bai gaskata ba kuwa, zai hallaka.
Vevoni uvi uvikhuueidikha nu khuuonciwa ipona nula uvei sikhuleidekha alaheigiwa.
17 Waɗannan alamu za su kasance tare da waɗanda suka gaskata. A cikin sunana za su fitar da aljanu, za su yi magana da sababbin harsuna.
Ifihwani ifi figendaga paninie na voni avikhuleedekha eilitawa lango. Vihenchoga eimipepo. Vinchovaga einchovele eimya.
18 Za su ɗauki macizai da hannuwansu. In kuwa suka sha mugun dafi, ba zai cuce su ba ko kaɗan. Za su ɗibiya hannuwansu a kan marasa lafiya, su kuwa warke.”
Vikhuuibataga injokha namavokho gaveni ndavanyule ifinu fyoni ifya khubuda safigaha kheinu. savifya vive khaga amavokho khuvatanu viponaga.”
19 Bayan Ubangiji Yesu ya yi musu magana, sai aka ɗauke shi zuwa sama, ya kuma zauna a hannun dama na Allah.
Vu anchovile navo akhatoliwa khukianya atamile eikhivokho kyandwo eikya Nguluve.
20 Sai almajiran suka fita, suka yi wa’azi ko’ina. Ubangiji kuwa ya yi aiki tare da su, ya tabbatar da maganarsa ta wurin alamu da suke biye da maganar.
Avakongi vakhahenga nukhulumbilila khila ponu usikhii ugwa u Yesu alekhuvomba eimbombo novo nukhu vonesya elimenyu nukhuponwa nifihwani fikhalongonchana navo.