< Markus 16 >
1 Da Asabbaci ya wuce, sai Maryamu Magdalin, Maryamu mahaifiyar Yaƙub, da kuma Salome suka sayi kayan ƙanshi domin su je su shafa wa jikin Yesu.
Quand le sabbat fut passé, Marie-Madeleine, Marie, mère de Jacques, et Salomé, achetèrent des aromates pour aller embaumer le corps de Jésus.
2 A ranar farko ta mako, da sassafe, bayan fitowar rana, suna kan hanyarsu zuwa kabarin ke nan,
Le premier jour de la semaine, de grand matin, elles se rendirent au tombeau, comme le soleil venait de se lever.
3 sai suka tambaye juna suka ce, “Wane ne zai gungura mana dutsen daga bakin kabarin?”
Elles se disaient entre elles: Qui nous roulera la pierre qui ferme l'entrée du tombeau?
4 Amma da suka ɗaga kai, sai suka ga cewa, an riga an gungura dutsen. Dutsen kuwa babba ne.
Ayant regardé, elles virent que la pierre avait été roulée; or, elle était très grande.
5 Da suna shiga cikin kabarin, sai suka ga wani saurayi sanye da farar riga, yana zaune a hannun dama, sai suka firgita.
Puis, étant entrées dans le tombeau, elles virent un jeune homme assis du côté droit, vêtu d'une robe blanche; et elles en furent épouvantées.
6 Ya ce, “Kada ku firgita. Kuna neman Yesu Banazare wanda aka gicciye ne. Ya tashi! Ba ya nan. Ku dubi inda aka kwantar da shi.
Mais il leur dit: Ne vous effrayez point! Vous cherchez Jésus de Nazareth qui a été crucifié: il est ressuscité. Il n'est pas ici; voici le lieu où on l'avait mis.
7 Amma ku tafi ku gaya wa almajiransa da kuma Bitrus cewa, ‘Ya sha gabanku zuwa Galili. Can za ku gan shi, kamar yadda ya faɗa muku.’”
Mais allez dire à ses disciples et à Pierre que Jésus vous précède en Galilée; c'est là que vous le verrez, comme il vous l'a dit.
8 Da rawan jiki da kuma ruɗewa, matan suka fita a guje daga kabarin. Ba su kuwa gaya wa kowa ba, don suna tsoro.
Elles sortirent du tombeau et s'enfuirent; car elles étaient saisies de crainte et d'étonnement. Et elles ne dirent rien à personne, tant elles étaient effrayées.
9 (note: The most reliable and earliest manuscripts do not include Mark 16:9-20.) Da Yesu ya tashi daga matattu da safe, a ranar farko ta mako, ya fara bayyana ga Maryamu Magdalin, wadda ya fitar da aljanu bakwai daga cikinta.
(note: The most reliable and earliest manuscripts do not include Mark 16:9-20.) [Or, Jésus, étant ressuscité le matin du premier jour de la semaine, apparut premièrement à Marie-Madeleine, de laquelle il avait chassé sept démons.
10 Ta je ta gaya wa waɗanda dā suke tare da shi, waɗanda kuma suke makoki da kuka.
Elle alla porter la nouvelle à ceux qui avaient vécu avec lui, et qui étaient dans le deuil et dans les larmes.
11 Da suka ji cewa Yesu yana da rai, har ma ta gan shi, ba su gaskata ba.
Mais eux, lorsqu'ils apprirent d'elle qu'il était vivant et qu'elle l'avait vu, ne la crurent point.
12 Daga baya Yesu ya bayyana a wani kamanni dabam ga biyunsu, yayinda suke tafiya ƙauye.
Après cela, Jésus se montra sous une autre forme à deux d'entre eux qui étaient en chemin pour aller à la campagne.
13 Waɗannan kuwa suka koma suka shaida wa sauran, amma su ma ba su gaskata ba.
Ceux-ci vinrent l'annoncer aux autres disciples; mais ils ne les crurent pas non plus.
14 Bayan haka, Yesu ya bayyana ga Sha Ɗayan, yayinda suke cin abinci. Ya tsawata musu a kan rashin bangaskiyarsu, da yadda suka ƙi gaskata waɗanda suka gan shi bayan ya tashi.
Plus tard, il se montra aux Onze, pendant qu'ils étaient à table, et il leur reprocha leur incrédulité et la dureté de leur coeur, parce qu'ils n'avaient pas cru ceux qui l'avaient vu ressuscité.
15 Ya ce, musu, “Ku tafi cikin dukan duniya, ku yi wa’azin bishara ga dukan halitta.
Puis il leur dit: Allez par tout le monde et prêchez l'Evangile à toute créature.
16 Duk wanda ya gaskata, aka kuma yi masa baftisma, zai sami ceto. Amma duk wanda bai gaskata ba kuwa, zai hallaka.
Celui qui croira et sera baptisé, sera sauvé; mais celui qui ne croira point sera condamné.
17 Waɗannan alamu za su kasance tare da waɗanda suka gaskata. A cikin sunana za su fitar da aljanu, za su yi magana da sababbin harsuna.
Voici les miracles qui accompagneront ceux qui auront cru: ils chasseront des démons en mon nom; ils parleront des langues nouvelles;
18 Za su ɗauki macizai da hannuwansu. In kuwa suka sha mugun dafi, ba zai cuce su ba ko kaɗan. Za su ɗibiya hannuwansu a kan marasa lafiya, su kuwa warke.”
ils prendront des serpents dans leurs mains; quand ils auront bu quelque breuvage mortel, il ne leur fera point de mal; ils imposeront les mains aux malades, et ceux-ci seront guéris.
19 Bayan Ubangiji Yesu ya yi musu magana, sai aka ɗauke shi zuwa sama, ya kuma zauna a hannun dama na Allah.
Le Seigneur Jésus, après leur avoir ainsi parlé, fut enlevé au ciel, et il s'assit à la droite de Dieu.
20 Sai almajiran suka fita, suka yi wa’azi ko’ina. Ubangiji kuwa ya yi aiki tare da su, ya tabbatar da maganarsa ta wurin alamu da suke biye da maganar.
Pour eux, étant partis, ils prêchèrent en tous lieux. Le Seigneur agissait avec eux, et il confirmait la parole par les miracles qui l'accompagnaient.]