< Markus 16 >
1 Da Asabbaci ya wuce, sai Maryamu Magdalin, Maryamu mahaifiyar Yaƙub, da kuma Salome suka sayi kayan ƙanshi domin su je su shafa wa jikin Yesu.
And when the sabbath was past Mary Magdalene, and Mary the mother of James, and Salome, bought spices in order to come and embalm Him:
2 A ranar farko ta mako, da sassafe, bayan fitowar rana, suna kan hanyarsu zuwa kabarin ke nan,
and very early in the morning of the first day of the week they come to the sepulchre at sun-rising.
3 sai suka tambaye juna suka ce, “Wane ne zai gungura mana dutsen daga bakin kabarin?”
And they said to one another, Who will roll away the stone for us from the door of the sepulchre?
4 Amma da suka ɗaga kai, sai suka ga cewa, an riga an gungura dutsen. Dutsen kuwa babba ne.
(but when they looked up, they saw that the stone was rolled away, ) for it was a very great one.
5 Da suna shiga cikin kabarin, sai suka ga wani saurayi sanye da farar riga, yana zaune a hannun dama, sai suka firgita.
And they went into the sepulchre and saw a young man sitting on the right side, clothed in a long white robe; and they were affrighted:
6 Ya ce, “Kada ku firgita. Kuna neman Yesu Banazare wanda aka gicciye ne. Ya tashi! Ba ya nan. Ku dubi inda aka kwantar da shi.
but he said to them, Be not affrighted, ye seek Jesus of Nazareth, who was crucified, He is risen, He is not here, see the place where they laid Him.
7 Amma ku tafi ku gaya wa almajiransa da kuma Bitrus cewa, ‘Ya sha gabanku zuwa Galili. Can za ku gan shi, kamar yadda ya faɗa muku.’”
But go, tell his disciples, and Peter particularly, that He is going before you into Galilee: there ye will see Him, as He told you.
8 Da rawan jiki da kuma ruɗewa, matan suka fita a guje daga kabarin. Ba su kuwa gaya wa kowa ba, don suna tsoro.
And they hasted out and fled from the sepulchre; for they were seized with trembling and amazement: neither said they any thing to any one; for they were afraid.
9 (note: The most reliable and earliest manuscripts do not include Mark 16:9-20.) Da Yesu ya tashi daga matattu da safe, a ranar farko ta mako, ya fara bayyana ga Maryamu Magdalin, wadda ya fitar da aljanu bakwai daga cikinta.
(note: The most reliable and earliest manuscripts do not include Mark 16:9-20.) Now Jesus being risen early on the first day of the week appeared first to Mary Magdalene, from whom He had cast out seven devils:
10 Ta je ta gaya wa waɗanda dā suke tare da shi, waɗanda kuma suke makoki da kuka.
and she went and told those that used to be with Him, who were mourning and weeping;
11 Da suka ji cewa Yesu yana da rai, har ma ta gan shi, ba su gaskata ba.
but they, though they heard that He was indeed alive, and had been seen by her, did not believe it.
12 Daga baya Yesu ya bayyana a wani kamanni dabam ga biyunsu, yayinda suke tafiya ƙauye.
After this He appeared in another form to two of them as they were walking, going into the country:
13 Waɗannan kuwa suka koma suka shaida wa sauran, amma su ma ba su gaskata ba.
and they went and told the rest; but they did not believe them neither.
14 Bayan haka, Yesu ya bayyana ga Sha Ɗayan, yayinda suke cin abinci. Ya tsawata musu a kan rashin bangaskiyarsu, da yadda suka ƙi gaskata waɗanda suka gan shi bayan ya tashi.
At last he appeared to the eleven as they were sitting at table, and upbraided them with their unbelief, and hardness of heart; because they did not believe those who had seen Him after He was risen.
15 Ya ce, musu, “Ku tafi cikin dukan duniya, ku yi wa’azin bishara ga dukan halitta.
And He said unto them, Go to all the world and preach the gospel to every one:
16 Duk wanda ya gaskata, aka kuma yi masa baftisma, zai sami ceto. Amma duk wanda bai gaskata ba kuwa, zai hallaka.
he that believeth and is baptized, shall be saved; but he that believeth not, shall be condemned.
17 Waɗannan alamu za su kasance tare da waɗanda suka gaskata. A cikin sunana za su fitar da aljanu, za su yi magana da sababbin harsuna.
And these signs shall accompany them that believe; in my name shall they cast out demons, they shall speak with new tongues;
18 Za su ɗauki macizai da hannuwansu. In kuwa suka sha mugun dafi, ba zai cuce su ba ko kaɗan. Za su ɗibiya hannuwansu a kan marasa lafiya, su kuwa warke.”
they shall take up serpents, and if they should drink any thing poisonous, it shall not hurt them; they shall lay hands on the sick, and they shall be well.
19 Bayan Ubangiji Yesu ya yi musu magana, sai aka ɗauke shi zuwa sama, ya kuma zauna a hannun dama na Allah.
Now the Lord, after He had spoken to them, was taken up into heaven, and sat on the right hand of God.
20 Sai almajiran suka fita, suka yi wa’azi ko’ina. Ubangiji kuwa ya yi aiki tare da su, ya tabbatar da maganarsa ta wurin alamu da suke biye da maganar.
And they went forth and preached every where, the Lord co-operating with them, and confirming the word by miracles following upon it. Amen.