< Markus 15 >

1 Da sassafe, sai manyan firistoci da dattawa, da malaman dokoki, da dukan Majalisa, suka yanke shawara. Suka daure Yesu, suka kai shi, suka miƙa shi ga Bilatus.
And as soon as ever it was light the chief priests holding a consultation with the elders and scribes, they and the whole sanhedrim, bound Jesus, and carried Him away, and delivered Him to Pilate.
2 Bilatus ya yi tambaya ya ce, “Kai ne Sarkin Yahudawa?” Yesu ya amsa ya ce, “I, haka yake, kamar yadda ka faɗa.”
And Pilate asked Him, Art thou the king of the Jews? and He answered It is as thou sayst.
3 Manyan firistoci suka zarge shi a kan abubuwa da yawa.
And the chief priests accused Him of many things: but he answered nothing.
4 Don haka Bilatus ya sāke tambayarsa ya ce, “Ba za ka amsa ba? Dubi abubuwa da yawa da suke zarginka da su.”
So Pilate asked Him again, saying, Dost thou answer nothing? See how many things they witness against thee:
5 Amma har yanzu, Yesu bai ba da amsa ba, Bilatus ya yi mamaki.
but Jesus still answered nothing, so that Pilate was amazed.
6 Yanzu fa, al’ada ce a lokacin Bikin, a saki ɗan kurkuku guda wanda mutane suka roƙa.
Now at the feast he used to release to them one prisoner, whomsoever they desired:
7 Wani mutumin da ake kira Barabbas, yana a kurkuku, tare da waɗansu’yan tawaye da suka yi kisankai a lokacin wani hargitsi.
and there was one Barabbas under confinement with some of his accomplices in sedition, who had committed murder in the insurrection.
8 Taron suka matso, suka ce roƙi Bilatus yă yi musu abin da ya saba yi.
And the people clamoured and desired him to do as he always used to do for them.
9 Bilatus ya yi tambaya ya ce, “Kuna so in sakar muku Sarkin Yahudawa?”
But Pilate answered them, saying, Would ye have me release to you the king of the Jews?
10 Don ya san saboda sonkai ne manyan firistoci suka ba da Yesu a gare shi.
(for he knew that the chief priests had delivered Him up to him out of envy: )
11 Amma manyan firistoci suka zuga taron su sa a saki Barabbas, a maimakon Yesu.
but the chief priests incited the people to desire that he would rather release Barabbas to them.
12 Bilatus ya tambaye su ya ce, “To, me zan yi da wanda kuke ce da shi, sarkin Yahudawa?”
And Pilate answered, and said to them again, What then would you have me do with Him, whom ye call king of the Jews?
13 Suka yi ihu, suka ce, “A gicciye shi!”
And they cried out again, Crucify Him.
14 Bilatus ya yi tambaya ya ce, “Don me? Wane laifi ya yi?” Amma suka ƙara yin ihu suna cewa, “A gicciye shi!”
But Pilate said unto them, Why, what ill has He done? And they cried out the more vehemently, Crucify Him.
15 Don son yă faranta wa taron rai, sai Bilatus ya sakar musu Barabbas. Ya sa aka yi wa Yesu bulala, sa’an nan ya ba da shi a gicciye.
So Pilate being willing to ingratiate with the multitude, released Barabbas to them, and having scourged Jesus, delivered Him up to be crucified.
16 Sojojin suka tafi da Yesu cikin fadar gwamna (wato, Firetoriyum), suka kira dukan kamfanin sojoji wuri ɗaya.
And the soldiers led Him away into the hall, which is called the Pretorium; and gathered their whole company together:
17 Suka sa masa wata riga mai ruwan shunayya, suka kuma tuƙa rawanin ƙaya suka sa masa.
and they clad Him in purple, and platted a crown of thorns and put it on his head,
18 Sai suka fara ce masa, “Ranka yă daɗe sarkin Yahudawa!”
and saluted Him, saying, Hail king of the Jews;
19 Suka dinga bugunsa a kā da sanda, suka tattofa masa miyau. Suka durƙusa suka yi masa bangirma na ba’a.
and struck Him on the head with a reed, and spit upon Him, and bowed their knees, and did Him homage.
20 Bayan da suka gama yin masa ba’a, suka tuɓe rigar mai ruwan shunayyar, suka sa masa nasa tufafi. Sai suka tafi da shi don a gicciye shi.
And when they had thus abused Him, they took off the purple from Him, and put his own clothes on Him, and brought Him out to crucify Him.
21 Sai ga wani mutum daga Sairin da ake kira Siman, mahaifin Alekzanda da Rufus, yana wucewa kan hanyarsa daga ƙauye. Sai suka tilasta shi yă ɗauki gicciyen.
And they compel one Simon a Cyrenian, the father of Alexander and Rufus, as he was passing by, coming out of the country, to carry his cross:
22 Suka kawo Yesu a wurin da ake kira Golgota (wanda yake nufin Wurin Ƙoƙon Kai).
and they brought Him to a place called Golgotha, which is, being interpreted, the place of a scull.
23 Sai suka miƙa masa ruwan inabi gauraye da mur, don yă rage zafi, amma bai sha ba.
And they offered Him wine mingled with myrrh to drink, but He would not take it.
24 Sai suka gicciye shi. Suka rarraba tufafinsa, suka jefa ƙuri’a a kansu don su ga abin da kowa zai samu.
And when they had fastened Him to the cross, they parted his garments, casting lots upon them, what each of them should take.
25 Sa’a ta uku na safe ce kuwa aka gicciye shi.
And it was the third hour, when they fixed Him on the cross:
26 Akwai rubutu na zarginsa, da ya ce, Sarkin Yahudawa.
and the title of his charge was written over Him, THE KING OF THE JEWS.
27 Suka gicciye’yan fashi biyu tare da shi, ɗaya a damansa, ɗayan kuma a hagunsa.
And they crucified two thieves with Him, one on his right hand and one on his left:
so that the scripture was fulfilled, which saith, "And He was numbered with the transgressors."
29 Masu wucewa suka zazzage shi. Suka kaɗa kai suna cewa, “To, kai da za ka rushe haikali ka kuma gina shi a kwana uku,
And they that passed by reviled Him, shaking their heads and saying, Ah, thou that destroyest, the temple,
30 sai ka sauko daga gicciyen, ka ceci kanka!”
and buildest it in three days, save thyself and come down from the cross.
31 Haka kuma, manyan firistoci da malaman dokoki suka yi masa ba’a a junansu, suna cewa, “Ya ceci waɗansu, amma ya kāsa ceton kansa!
And the chief priests likewise scoffing at Him among themselves, with the scribes, said, He saved others, Himself He cannot save: let Christ,
32 Bari wannan Kiristi, wannan Sarkin Isra’ila, yă sauko yanzu daga gicciye, don mu ga mu kuma gaskata.” Waɗanda aka gicciye tare da shi ma suka zazzage shi.
the king of Israel, come down now from the cross, that we may see and believe in Him. And even they that were crucified with Him, reviled Him.
33 Daga sa’a ta shida har zuwa sa’a ta tara na rana, duhu ya rufe dukan ƙasar.
Now at the sixth hour there was darkness over the whole land, until the ninth hour.
34 A daidai sa’a ta tara na rana, sai Yesu ya ɗaga murya da ƙarfi ya ce, “Eloi, Eloi, lama sabaktani?” (Wato, “Ya Allahna, ya Allahna, don me ka yashe ni?”).
And at the ninth hour Jesus cried out with a loud voice, saying, "Eloi, Eloi, lama sabachthani," which is being interpreted, My God, my God, why hast thou forsaken me?
35 Da waɗansu cikin waɗanda suke tsattsaye kusa da wurin suka ji haka, suka ce, “Ku saurara, yana kiran Iliya.”
And some of them that stood by hearing it, said, Behold He calleth upon Elias.
36 Wani mutum ya ruga ya je ya jiƙo soso da ruwan tsami, ya soka a sanda ya miƙa wa Yesu yă sha. Ya ce, “Ku ƙyale shi. Bari mu ga ko Iliya zai zo yă saukar da shi.”
And there ran one, and filled a spunge with vinegar, and putting it on a reed offered it Him to drink, saying, Let Him alone, let us see whether Elias will come to take Him down.
37 Da murya mai ƙarfi, Yesu ya ja numfashinsa na ƙarshe.
But Jesus cried with a loud voice and expired.
38 Labulen haikali kuwa ya yage kashi biyu, daga sama har ƙasa.
And the veil of the temple was rent in two from the top to the bottom.
39 Da jarumin da yake tsaye a gaban Yesu ya ji muryarsa, ya kuma ga yadda ya mutu, sai ya ce, “Gaskiya, wannan mutum Ɗan Allah ne!”
And when the centurion, that stood over against Him, saw that He expired with such a cry, he said, Truly this man was the Son of God.
40 Waɗansu mata suna kallo daga nesa. A cikinsu kuwa akwai Maryamu Magdalin, Maryamu mahaifiyar Yaƙub ƙarami da Yusuf, da kuma Salome.
There were also women at a distance looking on: among whom was Mary Magdalene, and Mary the mother of James the less and of Joses, and Salome;
41 A Galili waɗannan mata ne suka riƙa bin sa suna yin masa hidima. Waɗansu mata da yawa da suka zo tare da shi daga Urushalima, su ma suna nan a can.
who also when He was in Galilee, followed Him and waited on Him: and several others who came up to Jerusalem with Him.
42 Ranar kuwa ita ce ranar Shirye-shirye (wato, ana kashegari Asabbaci). Saboda haka, da yamma ta yi, sai
And the evening being now come, (because it was the preparation,
43 Yusuf daga Arimateya, wani sanannen ɗan Majalisa, wanda dā ma yake jiran zuwan mulkin Allah, ya je wajen Bilatus ba tsoro, ya roƙa a ba shi jikin Yesu.
or the day before the sabbath, ) Joseph of Arimathea, an honorable counsellor, who also was expecting the kingdom of God, came and went in boldly to Pilate, and begged the body of Jesus.
44 Bilatus ya yi mamaki da ya ji cewa Yesu ya riga ya mutu. Sai ya kira jarumin ya tambaye shi ko Yesu ya riga ya mutu.
But Pilate wondered that He was dead already, and therefore calling for the centurion he asked him if He had been dead any time:
45 Da ya ji ta bakin jarumin cewa haka ne, sai ya ba wa Yusuf jikin.
and when he heard it from the centurion, he granted the body to Joseph.
46 Sai Yusuf ya kawo zanen lilin, ya saukar da jikin, ya nannaɗe shi da lilin ɗin, sa’an nan ya sa shi a kabarin da aka fafe a cikin dutse. Sai ya gungura wani dutse ya rufe bakin kabarin.
And he bought fine linen, and took Him down, and wrapped Him in the linen, and laid Him in a sepulchre which was hewn out of a rock; and rolled a stone to the door of the sepulchre.
47 Maryamu Magdalin da Maryamu uwar Yusuf sun ga inda aka kwantar da shi.
And Mary Magdalene, and Mary the mother of Joses observed where He was laid.

< Markus 15 >