< Markus 15 >
1 Da sassafe, sai manyan firistoci da dattawa, da malaman dokoki, da dukan Majalisa, suka yanke shawara. Suka daure Yesu, suka kai shi, suka miƙa shi ga Bilatus.
And anone in ye dawnynge the hye prestes helde counsell wt ye elders and ye scribes and ye whoole cogregacion and bounde Iesus and ledde him awaye and delivered him to Pilate.
2 Bilatus ya yi tambaya ya ce, “Kai ne Sarkin Yahudawa?” Yesu ya amsa ya ce, “I, haka yake, kamar yadda ka faɗa.”
And Pilate axed him: arte thou the kynge of the Iewes? And he answered and sayde vnto him: thou sayest it.
3 Manyan firistoci suka zarge shi a kan abubuwa da yawa.
And the hye prestes accused him of many thinges.
4 Don haka Bilatus ya sāke tambayarsa ya ce, “Ba za ka amsa ba? Dubi abubuwa da yawa da suke zarginka da su.”
Wherfore Pilate axed him agayne sayinge: Answerest thou nothinge? Beholde how many thinges they lay vnto thy charge.
5 Amma har yanzu, Yesu bai ba da amsa ba, Bilatus ya yi mamaki.
Iesus yet answered never aworde so that Pilate merveled.
6 Yanzu fa, al’ada ce a lokacin Bikin, a saki ɗan kurkuku guda wanda mutane suka roƙa.
At that feast Pilate was wont to delivre at their pleasure a presoner: whomsoever they wolde desyre.
7 Wani mutumin da ake kira Barabbas, yana a kurkuku, tare da waɗansu’yan tawaye da suka yi kisankai a lokacin wani hargitsi.
And ther was one named Barrabas which laye bounde with the that made insurreccion and in the insurreccion comitted murther.
8 Taron suka matso, suka ce roƙi Bilatus yă yi musu abin da ya saba yi.
And ye people called vnto him and began to desyre accordinge as he had ever done vnto them.
9 Bilatus ya yi tambaya ya ce, “Kuna so in sakar muku Sarkin Yahudawa?”
Pylate answered them and sayd: Will ye that I lowse vnto you the kynge of the Iewes?
10 Don ya san saboda sonkai ne manyan firistoci suka ba da Yesu a gare shi.
For he knewe that the hye Prestes had delyvered him of envy.
11 Amma manyan firistoci suka zuga taron su sa a saki Barabbas, a maimakon Yesu.
But the hye prestes had moved the people that he shuld rather delyvre Barrabas vnto them.
12 Bilatus ya tambaye su ya ce, “To, me zan yi da wanda kuke ce da shi, sarkin Yahudawa?”
And Pylate answered agayne and sayd vnto the: What will ye then that I do wt him whom ye call ye kynge of ye Iewes?
13 Suka yi ihu, suka ce, “A gicciye shi!”
And they cryed agayne: crucifie him.
14 Bilatus ya yi tambaya ya ce, “Don me? Wane laifi ya yi?” Amma suka ƙara yin ihu suna cewa, “A gicciye shi!”
Pylate sayde vnto them: What evell hath he done? And they cryed ye moore fervently: crucifie him.
15 Don son yă faranta wa taron rai, sai Bilatus ya sakar musu Barabbas. Ya sa aka yi wa Yesu bulala, sa’an nan ya ba da shi a gicciye.
And so Pylate willinge to content the people lowsed them Barrabas and delyvered Iesus when he had scourged him for to be crucified.
16 Sojojin suka tafi da Yesu cikin fadar gwamna (wato, Firetoriyum), suka kira dukan kamfanin sojoji wuri ɗaya.
And the souddeers ledde him awaye into ye commen hall and called togedder the whoole multitude
17 Suka sa masa wata riga mai ruwan shunayya, suka kuma tuƙa rawanin ƙaya suka sa masa.
and they clothed him with purple and they platted a croune of thornes and crouned him with all
18 Sai suka fara ce masa, “Ranka yă daɗe sarkin Yahudawa!”
and beganne to salute him. Hayle kynge of the Iewes.
19 Suka dinga bugunsa a kā da sanda, suka tattofa masa miyau. Suka durƙusa suka yi masa bangirma na ba’a.
And they smoote him on the heed wt a rede and spat apon him and kneled doune and worsheped him.
20 Bayan da suka gama yin masa ba’a, suka tuɓe rigar mai ruwan shunayyar, suka sa masa nasa tufafi. Sai suka tafi da shi don a gicciye shi.
And when they had moocked him they toke the purple of him and put his awne cloothes on him and ledde him oute to crucifie him.
21 Sai ga wani mutum daga Sairin da ake kira Siman, mahaifin Alekzanda da Rufus, yana wucewa kan hanyarsa daga ƙauye. Sai suka tilasta shi yă ɗauki gicciyen.
And they compelled one that passed by called Symon of Cyrene (which cam oute of the felde and was father of Alexander and Rufus) to beare his crosse.
22 Suka kawo Yesu a wurin da ake kira Golgota (wanda yake nufin Wurin Ƙoƙon Kai).
And they brought him to a place named Golgotha (which is by interpretacion the place of deed mens scoulles)
23 Sai suka miƙa masa ruwan inabi gauraye da mur, don yă rage zafi, amma bai sha ba.
and they gave him to drinke wyne myngled with myrte but he receaved it not.
24 Sai suka gicciye shi. Suka rarraba tufafinsa, suka jefa ƙuri’a a kansu don su ga abin da kowa zai samu.
And when they had crucified him they parted his garmentes castinge loottes for them what every man shulde have.
25 Sa’a ta uku na safe ce kuwa aka gicciye shi.
And it was aboute ye thyrde houre and they crucified him.
26 Akwai rubutu na zarginsa, da ya ce, Sarkin Yahudawa.
And the tytle of his cause was wrytten: The kynge of the Iewes.
27 Suka gicciye’yan fashi biyu tare da shi, ɗaya a damansa, ɗayan kuma a hagunsa.
And they crucified with him two theves: the one on the ryght honde and the other on his lyfte.
And the scripture was fulfilled which sayeth: he was counted amonge the wicked.
29 Masu wucewa suka zazzage shi. Suka kaɗa kai suna cewa, “To, kai da za ka rushe haikali ka kuma gina shi a kwana uku,
And they that went by rayled on him: waggynge their heedes and sayinge: A wretche that destroyest the temple and byldest it in thre dayes:
30 sai ka sauko daga gicciyen, ka ceci kanka!”
save thy sylfe and come doune from the crosse.
31 Haka kuma, manyan firistoci da malaman dokoki suka yi masa ba’a a junansu, suna cewa, “Ya ceci waɗansu, amma ya kāsa ceton kansa!
Lyke wyse also mocked him ye hye preestes amonge them selves with the scribes and sayde: He saved other men him sylfe he cannot save.
32 Bari wannan Kiristi, wannan Sarkin Isra’ila, yă sauko yanzu daga gicciye, don mu ga mu kuma gaskata.” Waɗanda aka gicciye tare da shi ma suka zazzage shi.
Let Christ the kynge of Israel now descende from the crosse that we maye se and beleve. And they that were crucified with him checked him also.
33 Daga sa’a ta shida har zuwa sa’a ta tara na rana, duhu ya rufe dukan ƙasar.
And when the sixte houre was come darknes aroose over all the erth vntyll ye nynthe houre.
34 A daidai sa’a ta tara na rana, sai Yesu ya ɗaga murya da ƙarfi ya ce, “Eloi, Eloi, lama sabaktani?” (Wato, “Ya Allahna, ya Allahna, don me ka yashe ni?”).
And at the nynthe houre Iesus cryed with a loude voyce sayinge: Eloi Eloi lamaasbathani which is yf it be interpreted: my God my God why hast thou forsaken me?
35 Da waɗansu cikin waɗanda suke tsattsaye kusa da wurin suka ji haka, suka ce, “Ku saurara, yana kiran Iliya.”
And some of them that stode by when they hearde yt sayde: beholde he calleth for Helyas
36 Wani mutum ya ruga ya je ya jiƙo soso da ruwan tsami, ya soka a sanda ya miƙa wa Yesu yă sha. Ya ce, “Ku ƙyale shi. Bari mu ga ko Iliya zai zo yă saukar da shi.”
And one ran and filled a sponge full of veneger and put it on a rede and gave him to drinke sayinge: let him alone let vs se whether Helyas will come and take him doune.
37 Da murya mai ƙarfi, Yesu ya ja numfashinsa na ƙarshe.
But Iesus cryed with aloude voyce and gave vp the gooste.
38 Labulen haikali kuwa ya yage kashi biyu, daga sama har ƙasa.
And the vayle of the temple dyd rent in two peces from the toppe to the boottome.
39 Da jarumin da yake tsaye a gaban Yesu ya ji muryarsa, ya kuma ga yadda ya mutu, sai ya ce, “Gaskiya, wannan mutum Ɗan Allah ne!”
And when the Centurion which stode before him sawe that he so cryed and gave vp the gooste he sayd: truly this man was the sonne of God.
40 Waɗansu mata suna kallo daga nesa. A cikinsu kuwa akwai Maryamu Magdalin, Maryamu mahaifiyar Yaƙub ƙarami da Yusuf, da kuma Salome.
Ther were also wemen a good waye of beholdinge him: amonge whom was Mary Magdalen and Mary the mother of Iames the lytle and of Ioses and Mary Salome
41 A Galili waɗannan mata ne suka riƙa bin sa suna yin masa hidima. Waɗansu mata da yawa da suka zo tare da shi daga Urushalima, su ma suna nan a can.
which also when he was in Galile folowed him and ministred vnto him and many other wemen which came vp with him to Hierusalem.
42 Ranar kuwa ita ce ranar Shirye-shirye (wato, ana kashegari Asabbaci). Saboda haka, da yamma ta yi, sai
And now when nyght was come (because it was ye even that goeth before ye saboth)
43 Yusuf daga Arimateya, wani sanannen ɗan Majalisa, wanda dā ma yake jiran zuwan mulkin Allah, ya je wajen Bilatus ba tsoro, ya roƙa a ba shi jikin Yesu.
Ioseph of Arimathia a noble councelour which also loked for ye kyngdome of God came and went in booldly vnto Pylate and begged ye boddy of Iesu.
44 Bilatus ya yi mamaki da ya ji cewa Yesu ya riga ya mutu. Sai ya kira jarumin ya tambaye shi ko Yesu ya riga ya mutu.
And Pylate merveled that he was alredy deed and called vnto him ye Centurion and axed of him whether he had bene eny whyle deed.
45 Da ya ji ta bakin jarumin cewa haka ne, sai ya ba wa Yusuf jikin.
And when he knewe the trueth of the Centurion he gave ye body to Ioseph.
46 Sai Yusuf ya kawo zanen lilin, ya saukar da jikin, ya nannaɗe shi da lilin ɗin, sa’an nan ya sa shi a kabarin da aka fafe a cikin dutse. Sai ya gungura wani dutse ya rufe bakin kabarin.
And he bought a lynnen cloothe and toke him doune and wrapped him in ye lynnen cloothe and layde him in a tombe yt was hewen oute of ye rocke and rolled a stone vnto the doze of the sepulcre.
47 Maryamu Magdalin da Maryamu uwar Yusuf sun ga inda aka kwantar da shi.
And Mary Magdalen and Mary Ioses beheld where he was layde.