< Markus 15 >

1 Da sassafe, sai manyan firistoci da dattawa, da malaman dokoki, da dukan Majalisa, suka yanke shawara. Suka daure Yesu, suka kai shi, suka miƙa shi ga Bilatus.
And, straightway, early, when they had made, a council, the High-priest, with the Elders, and Scribes, and all the High-council, binding Jesus, led him away, and delivered him up unto Pilate.
2 Bilatus ya yi tambaya ya ce, “Kai ne Sarkin Yahudawa?” Yesu ya amsa ya ce, “I, haka yake, kamar yadda ka faɗa.”
And Pilate questioned him—Art, thou, the king of the Jews? And, he, answering him, saith—Thou, sayest.
3 Manyan firistoci suka zarge shi a kan abubuwa da yawa.
And the High-priests began to accuse him, of many things.
4 Don haka Bilatus ya sāke tambayarsa ya ce, “Ba za ka amsa ba? Dubi abubuwa da yawa da suke zarginka da su.”
And, Pilate, again, was questioning him, [saying]—Answerest thou, nothing? See! of how many things, they are accusing thee!
5 Amma har yanzu, Yesu bai ba da amsa ba, Bilatus ya yi mamaki.
But, Jesus, no further, answered, anything, so that Pilate began to marvel.
6 Yanzu fa, al’ada ce a lokacin Bikin, a saki ɗan kurkuku guda wanda mutane suka roƙa.
Now, at feast time, he was wont to release unto them one prisoner, whom they were claiming.
7 Wani mutumin da ake kira Barabbas, yana a kurkuku, tare da waɗansu’yan tawaye da suka yi kisankai a lokacin wani hargitsi.
And there was the so-called Barabbas, with the rebels, bound, even with them who, in the rebellion, had committed, murder.
8 Taron suka matso, suka ce roƙi Bilatus yă yi musu abin da ya saba yi.
And, going up, the multitude began to be claiming—according as he was wont to do for them.
9 Bilatus ya yi tambaya ya ce, “Kuna so in sakar muku Sarkin Yahudawa?”
But, Pilate, answered them, saying—Will ye, I release unto you, the King of the Jews?
10 Don ya san saboda sonkai ne manyan firistoci suka ba da Yesu a gare shi.
For he was getting to know that, for envy, had [the High-priests] delivered him up.
11 Amma manyan firistoci suka zuga taron su sa a saki Barabbas, a maimakon Yesu.
But, the High-priests, stirred up the multitude, that, rather Barabbas, he should release unto them.
12 Bilatus ya tambaye su ya ce, “To, me zan yi da wanda kuke ce da shi, sarkin Yahudawa?”
But, Pilate, again answering, was saying unto them—What then shall I do with him whom ye call, the King of the Jews?
13 Suka yi ihu, suka ce, “A gicciye shi!”
And, they, again, cried out—Crucify him!
14 Bilatus ya yi tambaya ya ce, “Don me? Wane laifi ya yi?” Amma suka ƙara yin ihu suna cewa, “A gicciye shi!”
But, Pilate, was saying unto them—Why! what, evil, hath he done? And, they, vehemently, cried out—Crucify him!
15 Don son yă faranta wa taron rai, sai Bilatus ya sakar musu Barabbas. Ya sa aka yi wa Yesu bulala, sa’an nan ya ba da shi a gicciye.
And Pilate, being minded to do what would satisfy, the multitude, released unto them Barabbas, and delivered up Jesus, having scourged him, that he should be crucified.
16 Sojojin suka tafi da Yesu cikin fadar gwamna (wato, Firetoriyum), suka kira dukan kamfanin sojoji wuri ɗaya.
And, the soldiers, led him away, inside the court, which is a judgment-hall, —and called together the whole band;
17 Suka sa masa wata riga mai ruwan shunayya, suka kuma tuƙa rawanin ƙaya suka sa masa.
and they array him in purple, and set upon him, when they have plaited it; a crown of thorns, —
18 Sai suka fara ce masa, “Ranka yă daɗe sarkin Yahudawa!”
and began to be saluting him—Joy to thee! King of the Jews!
19 Suka dinga bugunsa a kā da sanda, suka tattofa masa miyau. Suka durƙusa suka yi masa bangirma na ba’a.
and were striking him on the head with a reed, and were spitting at him, —and, bowing their knees, were doing him homage.
20 Bayan da suka gama yin masa ba’a, suka tuɓe rigar mai ruwan shunayyar, suka sa masa nasa tufafi. Sai suka tafi da shi don a gicciye shi.
And, when they had mocked him, they put off him, the purple, and put on him, his own garments. And they lead him forth, that they may crucify him.
21 Sai ga wani mutum daga Sairin da ake kira Siman, mahaifin Alekzanda da Rufus, yana wucewa kan hanyarsa daga ƙauye. Sai suka tilasta shi yă ɗauki gicciyen.
And they impress a certain passer-by, Simon a Cyrenian, coming from a field, the father of Alexander and Rufus, —that he may carry his cross.
22 Suka kawo Yesu a wurin da ake kira Golgota (wanda yake nufin Wurin Ƙoƙon Kai).
And they bring him unto the Golgotha place, which is, being translated, Skull-place.
23 Sai suka miƙa masa ruwan inabi gauraye da mur, don yă rage zafi, amma bai sha ba.
And they would have given him, myrrhed wine, —who, however, received it not.
24 Sai suka gicciye shi. Suka rarraba tufafinsa, suka jefa ƙuri’a a kansu don su ga abin da kowa zai samu.
And they crucify him, and part asunder his garments, casting a lot upon them—who should have anything.
25 Sa’a ta uku na safe ce kuwa aka gicciye shi.
And it was the third hour, and they crucified him.
26 Akwai rubutu na zarginsa, da ya ce, Sarkin Yahudawa.
And the inscription of his accusation, had been inscribed—THE KING OF THE JEWS.
27 Suka gicciye’yan fashi biyu tare da shi, ɗaya a damansa, ɗayan kuma a hagunsa.
And, with him, they crucify, two robbers, one on his right hand, and one on his left.
29 Masu wucewa suka zazzage shi. Suka kaɗa kai suna cewa, “To, kai da za ka rushe haikali ka kuma gina shi a kwana uku,
And, the passers-by, were reviling him, shaking their heads, and saying—Aha! thou who wast pulling down the shrine, and building one in three days!
30 sai ka sauko daga gicciyen, ka ceci kanka!”
Save thyself, —coming down from the cross.
31 Haka kuma, manyan firistoci da malaman dokoki suka yi masa ba’a a junansu, suna cewa, “Ya ceci waɗansu, amma ya kāsa ceton kansa!
Likewise, the High-priests also, mocking one to another, with the Scribes, were saying—Others, he saved, himself, he cannot save!
32 Bari wannan Kiristi, wannan Sarkin Isra’ila, yă sauko yanzu daga gicciye, don mu ga mu kuma gaskata.” Waɗanda aka gicciye tare da shi ma suka zazzage shi.
The Christ, the King of Israel—let him come down now from the cross, that we may see and believe. And, they who had been crucified with him, were casting it in his teeth.
33 Daga sa’a ta shida har zuwa sa’a ta tara na rana, duhu ya rufe dukan ƙasar.
And, when it was the sixth hour, darkness, came on all the land—until the ninth hour;
34 A daidai sa’a ta tara na rana, sai Yesu ya ɗaga murya da ƙarfi ya ce, “Eloi, Eloi, lama sabaktani?” (Wato, “Ya Allahna, ya Allahna, don me ka yashe ni?”).
and, at the ninth hour, Jesus, uttered a cry, with a loud voice—Eloi! Eloi! lama sabachthanei? which is, being translated—My God! [My God!] to what end, didst thou forsake me?
35 Da waɗansu cikin waɗanda suke tsattsaye kusa da wurin suka ji haka, suka ce, “Ku saurara, yana kiran Iliya.”
And, some of the by-standers, having heard, were saying—See! Elijah, he calleth!
36 Wani mutum ya ruga ya je ya jiƙo soso da ruwan tsami, ya soka a sanda ya miƙa wa Yesu yă sha. Ya ce, “Ku ƙyale shi. Bari mu ga ko Iliya zai zo yă saukar da shi.”
And one, running, filled a sponge with vinegar, and, putting it about a reed, was giving him to drink, saying—Stay! let us see whether Elijah is coming, to take him down!
37 Da murya mai ƙarfi, Yesu ya ja numfashinsa na ƙarshe.
But, Jesus, sending out a loud voice, ceased to breathe.
38 Labulen haikali kuwa ya yage kashi biyu, daga sama har ƙasa.
And, the veil of the Temple, was rent into two, from top to bottom.
39 Da jarumin da yake tsaye a gaban Yesu ya ji muryarsa, ya kuma ga yadda ya mutu, sai ya ce, “Gaskiya, wannan mutum Ɗan Allah ne!”
Now the centurion, who was standing near, out over against him, seeing, that, thus, he ceased to breathe, said—Truly, this man, was God’s son!
40 Waɗansu mata suna kallo daga nesa. A cikinsu kuwa akwai Maryamu Magdalin, Maryamu mahaifiyar Yaƙub ƙarami da Yusuf, da kuma Salome.
And there were, women also, from afar, looking on, —among whom were both Mary the Magdalene, and Mary the mother of James the Little and Joses, and Salome;
41 A Galili waɗannan mata ne suka riƙa bin sa suna yin masa hidima. Waɗansu mata da yawa da suka zo tare da shi daga Urushalima, su ma suna nan a can.
who, when he was in Galilee, used to follow him, and minister unto him, —and many other women, who had come up with him unto Jerusalem.
42 Ranar kuwa ita ce ranar Shirye-shirye (wato, ana kashegari Asabbaci). Saboda haka, da yamma ta yi, sai
And evening, already, having begun, since it was a preparation, that is, the eve of a Sabbath,
43 Yusuf daga Arimateya, wani sanannen ɗan Majalisa, wanda dā ma yake jiran zuwan mulkin Allah, ya je wajen Bilatus ba tsoro, ya roƙa a ba shi jikin Yesu.
Joseph of Arimathaea, a noble counsellor, who, also himself, was awaiting the kingdom of God, came; and, venturing, went in unto Pilate, and claimed the body of Jesus.
44 Bilatus ya yi mamaki da ya ji cewa Yesu ya riga ya mutu. Sai ya kira jarumin ya tambaye shi ko Yesu ya riga ya mutu.
But, Pilate, wondered whether, already, he was dead; and, calling near the centurion, questioned him—whether he had, already, died.
45 Da ya ji ta bakin jarumin cewa haka ne, sai ya ba wa Yusuf jikin.
And, getting to know from the centurion, he presented the corpse unto Joseph.
46 Sai Yusuf ya kawo zanen lilin, ya saukar da jikin, ya nannaɗe shi da lilin ɗin, sa’an nan ya sa shi a kabarin da aka fafe a cikin dutse. Sai ya gungura wani dutse ya rufe bakin kabarin.
And, buying a fine Indian cloth, he took him down, and wrapped him about with the cloth, and laid him in a tomb, which had been hewn out of a rock, —and rolled near a stone upon the door of the tomb.
47 Maryamu Magdalin da Maryamu uwar Yusuf sun ga inda aka kwantar da shi.
Now, Mary the Magdalene, and Mary the mother of Joses, were viewing how he had been laid.

< Markus 15 >