< Markus 15 >
1 Da sassafe, sai manyan firistoci da dattawa, da malaman dokoki, da dukan Majalisa, suka yanke shawara. Suka daure Yesu, suka kai shi, suka miƙa shi ga Bilatus.
And straightaway in the morning the chief priests with the elders and scholars and the whole council, having made a plan, after binding Jesus, they took him away, and delivered him up to Pilate.
2 Bilatus ya yi tambaya ya ce, “Kai ne Sarkin Yahudawa?” Yesu ya amsa ya ce, “I, haka yake, kamar yadda ka faɗa.”
And Pilate questioned him, Are thou the king of the Jews? And having answered, he said to him, Thou say.
3 Manyan firistoci suka zarge shi a kan abubuwa da yawa.
And the chief priests accused him of many things.
4 Don haka Bilatus ya sāke tambayarsa ya ce, “Ba za ka amsa ba? Dubi abubuwa da yawa da suke zarginka da su.”
And Pilate again questioned him, saying, Thou answer nothing? Behold how many things they testify against thee.
5 Amma har yanzu, Yesu bai ba da amsa ba, Bilatus ya yi mamaki.
But Jesus answered nothing any more, so as for Pilate to wonder.
6 Yanzu fa, al’ada ce a lokacin Bikin, a saki ɗan kurkuku guda wanda mutane suka roƙa.
Now during a feast he released to them one prisoner, whomever they requested.
7 Wani mutumin da ake kira Barabbas, yana a kurkuku, tare da waɗansu’yan tawaye da suka yi kisankai a lokacin wani hargitsi.
And a man who was called Barabbas was with the rebels who were bound, men who had committed murder during the insurrection.
8 Taron suka matso, suka ce roƙi Bilatus yă yi musu abin da ya saba yi.
And having cried aloud, the multitude began to ask as he was always doing for them.
9 Bilatus ya yi tambaya ya ce, “Kuna so in sakar muku Sarkin Yahudawa?”
And Pilate answered them, saying, Do ye wish that I would release to you the king of the Jews?
10 Don ya san saboda sonkai ne manyan firistoci suka ba da Yesu a gare shi.
For he knew that the chief priests had delivered him up because of envy.
11 Amma manyan firistoci suka zuga taron su sa a saki Barabbas, a maimakon Yesu.
But the chief priests incited the crowd, so that he would release Barabbas to them instead.
12 Bilatus ya tambaye su ya ce, “To, me zan yi da wanda kuke ce da shi, sarkin Yahudawa?”
And again having answered, Pilate said to them, What then do ye wish I would do to the man whom ye call the king of the Jews?
13 Suka yi ihu, suka ce, “A gicciye shi!”
And they cried out again, Crucify him.
14 Bilatus ya yi tambaya ya ce, “Don me? Wane laifi ya yi?” Amma suka ƙara yin ihu suna cewa, “A gicciye shi!”
And Pilate said to them, For what evil has he done? But they cried out even more, Crucify him.
15 Don son yă faranta wa taron rai, sai Bilatus ya sakar musu Barabbas. Ya sa aka yi wa Yesu bulala, sa’an nan ya ba da shi a gicciye.
And Pilate, wanting to do what was sufficient for the crowd, released Barabbas to them. And he delivered Jesus, after scourging, so that he might be crucified.
16 Sojojin suka tafi da Yesu cikin fadar gwamna (wato, Firetoriyum), suka kira dukan kamfanin sojoji wuri ɗaya.
And the soldiers led him away inside the courtyard, which is the Praetorium, and they call together the whole band.
17 Suka sa masa wata riga mai ruwan shunayya, suka kuma tuƙa rawanin ƙaya suka sa masa.
And they put purple clothing on him, and clothe him with a woven crown of thorns,
18 Sai suka fara ce masa, “Ranka yă daɗe sarkin Yahudawa!”
and began to salute him, Hail, king of the Jews!
19 Suka dinga bugunsa a kā da sanda, suka tattofa masa miyau. Suka durƙusa suka yi masa bangirma na ba’a.
And they struck his head with a reed, and spat upon him, and bowing their knees worshiped him.
20 Bayan da suka gama yin masa ba’a, suka tuɓe rigar mai ruwan shunayyar, suka sa masa nasa tufafi. Sai suka tafi da shi don a gicciye shi.
And when they had mocked him, they took the purple garment off of him, and dressed him with his own garments. And they lead him out so that they might crucify him.
21 Sai ga wani mutum daga Sairin da ake kira Siman, mahaifin Alekzanda da Rufus, yana wucewa kan hanyarsa daga ƙauye. Sai suka tilasta shi yă ɗauki gicciyen.
And they draft a certain Simon, a Cyrenian passing by coming from the countryside, the father of Alexander and Rufus, so that he would take his cross.
22 Suka kawo Yesu a wurin da ake kira Golgota (wanda yake nufin Wurin Ƙoƙon Kai).
And they bring him to the place Golgotha, which is, being interpreted, the place of a skull.
23 Sai suka miƙa masa ruwan inabi gauraye da mur, don yă rage zafi, amma bai sha ba.
And they gave him wine mingled with myrrh to drink, but he did not take it.
24 Sai suka gicciye shi. Suka rarraba tufafinsa, suka jefa ƙuri’a a kansu don su ga abin da kowa zai samu.
And having crucified him, they divided his garments, casting a lot for them, who would take what.
25 Sa’a ta uku na safe ce kuwa aka gicciye shi.
And it was the third hour, and they crucified him.
26 Akwai rubutu na zarginsa, da ya ce, Sarkin Yahudawa.
And the inscription of his accusation was inscribed, THE KING OF THE JEWS.
27 Suka gicciye’yan fashi biyu tare da shi, ɗaya a damansa, ɗayan kuma a hagunsa.
And they crucify two robbers with him, one at his right hand, and one at his left.
And the scripture was fulfilled, which says, And he was reckoned with lawless men.
29 Masu wucewa suka zazzage shi. Suka kaɗa kai suna cewa, “To, kai da za ka rushe haikali ka kuma gina shi a kwana uku,
And those who passed by railed at him, wagging their heads, and saying, Ha! Thou who destroy the temple, and build it in three days,
30 sai ka sauko daga gicciyen, ka ceci kanka!”
save thyself, and come down from the cross.
31 Haka kuma, manyan firistoci da malaman dokoki suka yi masa ba’a a junansu, suna cewa, “Ya ceci waɗansu, amma ya kāsa ceton kansa!
Likewise also the chief priests mocking among each other with the scholars said, He saved others, he cannot save himself.
32 Bari wannan Kiristi, wannan Sarkin Isra’ila, yă sauko yanzu daga gicciye, don mu ga mu kuma gaskata.” Waɗanda aka gicciye tare da shi ma suka zazzage shi.
Let the Christ, the king of Israel, come down now from the cross, that we may see and believe in him. And those who were crucified with him reviled him.
33 Daga sa’a ta shida har zuwa sa’a ta tara na rana, duhu ya rufe dukan ƙasar.
And having become the sixth hour, darkness occurred over the whole land until the ninth hour.
34 A daidai sa’a ta tara na rana, sai Yesu ya ɗaga murya da ƙarfi ya ce, “Eloi, Eloi, lama sabaktani?” (Wato, “Ya Allahna, ya Allahna, don me ka yashe ni?”).
And at the ninth hour Jesus cried out in a great voice, saying, Eloi, Eloi, lama sabachthani? which is, being interpreted, My God, my God, why have thou forsaken me?
35 Da waɗansu cikin waɗanda suke tsattsaye kusa da wurin suka ji haka, suka ce, “Ku saurara, yana kiran Iliya.”
And some of those who stood by, when they heard it, said, Behold, he calls Elijah.
36 Wani mutum ya ruga ya je ya jiƙo soso da ruwan tsami, ya soka a sanda ya miƙa wa Yesu yă sha. Ya ce, “Ku ƙyale shi. Bari mu ga ko Iliya zai zo yă saukar da shi.”
And one having ran, and having filled a sponge of vinegar, and having placed it on a reed, gave him to drink, saying, Leave be. We might see if Elijah comes to take him down.
37 Da murya mai ƙarfi, Yesu ya ja numfashinsa na ƙarshe.
And having given out a great voice, Jesus expired.
38 Labulen haikali kuwa ya yage kashi biyu, daga sama har ƙasa.
And the curtain of the temple was torn in two from the top to the bottom.
39 Da jarumin da yake tsaye a gaban Yesu ya ji muryarsa, ya kuma ga yadda ya mutu, sai ya ce, “Gaskiya, wannan mutum Ɗan Allah ne!”
And when the centurion, who stood from opposite him, saw that he expired, having cried out this way, he said, Truly this man was the Son of God.
40 Waɗansu mata suna kallo daga nesa. A cikinsu kuwa akwai Maryamu Magdalin, Maryamu mahaifiyar Yaƙub ƙarami da Yusuf, da kuma Salome.
And there were also women looking on from a distance, among whom were also Mary Magdalene, and Mary the mother of James the small man, and of Joses, and Salome;
41 A Galili waɗannan mata ne suka riƙa bin sa suna yin masa hidima. Waɗansu mata da yawa da suka zo tare da shi daga Urushalima, su ma suna nan a can.
women who also followed him and served him when he was in Galilee, also many other women who came up with him to Jerusalem.
42 Ranar kuwa ita ce ranar Shirye-shirye (wato, ana kashegari Asabbaci). Saboda haka, da yamma ta yi, sai
And now having become evening, since it was the Preparation, that is, pre-sabbath,
43 Yusuf daga Arimateya, wani sanannen ɗan Majalisa, wanda dā ma yake jiran zuwan mulkin Allah, ya je wajen Bilatus ba tsoro, ya roƙa a ba shi jikin Yesu.
Joseph of Arimathaea came, an honorable councilman who also himself was awaiting the kingdom of God, emboldened, he went in near Pilate, and requested the body of Jesus.
44 Bilatus ya yi mamaki da ya ji cewa Yesu ya riga ya mutu. Sai ya kira jarumin ya tambaye shi ko Yesu ya riga ya mutu.
And Pilate wondered if he died already. And having summoned the centurion, he questioned him if he was already dead.
45 Da ya ji ta bakin jarumin cewa haka ne, sai ya ba wa Yusuf jikin.
And having ascertained from the centurion, he granted the body to Joseph.
46 Sai Yusuf ya kawo zanen lilin, ya saukar da jikin, ya nannaɗe shi da lilin ɗin, sa’an nan ya sa shi a kabarin da aka fafe a cikin dutse. Sai ya gungura wani dutse ya rufe bakin kabarin.
And having bought fine linen, and having taken him down, he wrapped him in the linen, and laid him in a sepulcher, being that which had been hewn out of rock. And he rolled a stone to the door of the sepulcher.
47 Maryamu Magdalin da Maryamu uwar Yusuf sun ga inda aka kwantar da shi.
And Mary Magdalene and Mary the mother of Joses saw where he was laid.