< Markus 14 >
1 To, saura kwana biyu ne kaɗai a yi Bikin Ƙetarewa da Bikin Burodi Marar Yisti, sai manyan firistoci da malaman dokoki, suka nemi wani dalili su kama Yesu a ɓoye, su kashe.
It was now two days before the Festival of the Passover and the Unleavened bread. The Chief Priests and the Teachers of the Law were looking for an opportunity to arrest Jesus by stealth, and to put him to death;
2 Suka ce, “Ba a lokacin Biki ba, don kada mutane su yi tawaye.”
for they said: “Not during the Festival, for fear of a riot.”
3 Yayinda yake a Betani, a gidan wani mutumin da ake kira Siman Kuturu, yana cin abinci, sai wata mace ta zo da wani ɗan tulu na turaren alabasta da aka yi da nardi zalla, mai tsadan gaske. Ta fasa tulun, ta kuma zuba turaren a kansa.
When Jesus was still at Bethany, in the house of Simon the leper, while he was at table, a woman came with an alabaster jar of choice spikenard perfume of great value. She broke the jar, and poured the perfume on his head.
4 Waɗansu daga cikin waɗanda suke wurin, suka ji haushi, suka ce wa juna, “Me ya sa za a ɓata turaren nan haka?
Some of those who were present said to one another indignantly: “Why has the perfume been wasted like this?
5 Da an sayar da shi, ai, da an sami kuɗi fiye da albashi ma’aikaci na shekara guda, a ba wa matalauta. Sai suka tsawata mata da zafi.”
This perfume could have been sold for more than thirty pounds, and the money given to the poor.”
6 Yesu ya ce, “Ku ƙyale ta mana. Don me kuke damunta? Ta yi abu mai kyau a gare ni.
“Let her alone,” said Jesus, as they began to find fault with her, “why are you troubling her? This is a beautiful deed that she has done for me.
7 Matalauta dai suna tare da ku kullum, za ku kuma iya taimakonsu a duk lokacin da kuke so. Amma ni ba zan kasance da ku kullum ba.
You always have the poor with you, and whenever you wish you can do good to them; but you will not always have me.
8 Ta yi abin da ta iya yi. Ta zuba turare a jikina kafin lokaci, don shirin jana’izata.
She has done what she could; she has perfumed my body beforehand for my burial.
9 Gaskiya nake gaya muku, duk inda aka yi wa’azin bishara ko’ina a duniya, za a faɗi abin da ta yi, domin tunawa da ita.”
And I tell you, wherever, in the whole world, the Good News is proclaimed, what this woman has done will be told in memory of her.”
10 Sai Yahuda Iskariyot, ɗaya daga cikin Sha Biyun nan, ya je wajen manyan firistoci don yă bashe Yesu a gare su.
After this, Judas Iscariot, one of the Twelve, went to the Chief Priests, to betray Jesus to them.
11 Suka yi murna da jin haka, suka yi alkawari za su ba shi kuɗi. Don haka, ya fara neman zarafi yă ba da shi.
They were glad to hear what he said, and promised to pay him. So he looked for a way to betray Jesus opportunely.
12 A rana ta fari ta Bikin Burodi Marar Yisti, lokacin da akan yanka ɗan ragon hadayar kafara, bisa ga al’ada ta tunawa da Bikin Ƙetarewa, sai almajiran Yesu suka tambaye shi, suka ce, “Ina kake so mu je mu shirya maka wurin da za ka ci Bikin Ƙetarewa?”
On the first day of the Festival of the Unleavened bread, when it was customary to kill the Passover lambs, his disciples said to Jesus: “Where do you wish us to go and make preparations for your eating the Passover?”
13 Sai ya aiki biyu daga cikin almajiransa ya ce, “Ku shiga cikin birni, za ku sadu da wani ɗauke da tulun ruwa. Ku bi shi.
Jesus sent forward two of his disciples and said to them: “Go into the city, and there a man carrying a pitcher of water will meet you; follow him;
14 Gidan da ya shiga, ku gaya wa maigidan cewa, ‘Malam yana tambaya, ina ɗakin baƙina, inda zan ci Bikin Ƙetarewa tare da almajiraina?’
and, wherever he goes in, say to the owner of the house ‘The Teacher says — Where is my room where I am to eat the Passover with my disciples?’
15 Zai nuna muku wani babban ɗakin sama da aka shirya domin baƙi. Ku yi mana shirin a can.”
He will himself show you a large upstairs room, set out ready; and there make preparations for us.”
16 Almajiran suka tafi, suka shiga cikin birnin, suka kuwa tarar da kome kamar yadda Yesu ya faɗa musu. Sai suka shirya Bikin Ƙetarewa.
So the disciples set out and went into the city, and found everything just as Jesus had told them; and they prepared the Passover.
17 Da yamma ta yi, sai Yesu ya zo tare da Sha Biyun.
In the evening he went there with the Twelve,
18 Yayinda suke cin abinci a tebur, sai ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, ɗaya daga cikinku zai bashe ni, wani wanda yake ci tare da ni.”
and when they had taken their places and were eating, Jesus said: “I tell you that one of you is going to betray me — one who is eating with me.”
19 Suka cika da baƙin ciki, da ɗaya-ɗaya suka ce masa, “Tabbatacce, ba ni ba ne, ko?”
They were grieved at this, and began to say to him, one after another: “Can it be I?”
20 Ya ce, “Ɗaya daga cikin Sha Biyun ne, wanda yake ci tare da ni a kwano.
“It is one of you Twelve,” said Jesus, “the one who is dipping his bread beside me into the dish.
21 Ɗan Mutum zai tafi kamar yadda yake a rubuce game da shi, amma kaiton mutumin da ya bashe Ɗan Mutum! Zai fi masa, da ba a haife shi ba.”
True, the Son of Man must go, as Scripture says of him, yet alas for that man by whom the Son of Man is being betrayed! For that man ‘it would be better never to have been born!’”
22 Yayinda suke cin abinci, sai Yesu ya ɗauki burodi, ya yi godiya, ya kakkarya, ya ba wa almajiransa, yana cewa, “Ku karɓa, wannan jikina ne.”
While they were eating, Jesus took some bread, and, after saying the blessing, broke it, and gave it to them, and said: “Take it; this is my body.”
23 Sai kuma ya ɗauki kwaf ruwan inabi, ya yi godiya, ya kuma miƙa musu, dukansu suka sha daga ciki.
Then he took a cup, and, after saying the thanksgiving, gave it to them, and they all drank from it.
24 Sai ya ce musu, “Wannan jinina ne na alkawari, wanda aka zubar da shi saboda mutane da yawa.
“This is my Covenant-blood,” he said, “which is poured out on behalf of many.
25 Gaskiya nake gaya muku, ‘Ba zan ƙara sha daga’ya’yan inabi ba, sai ranan nan, da zan sha shi sabo a mulkin Allah.’”
I tell you that I shall never again drink of the juice of the grape, until that day when I shall drink it new in the Kingdom of God.”
26 Da suka rera waƙa, sai suka fita, suka tafi Dutsen Zaitun.
They then sang a hymn, and went out up the Mount of Olives,
27 Yesu ya ce musu, “Dukanku za ku ja da baya ku bar ni, gama yana a rubuce cewa, “‘Zan bugi makiyayin tumaki, tumakin kuwa za su warwatse.’
presently Jesus said to them: “All of you will fall away; for Scripture says — ‘I will strike down the Shepherd, and the sheep will be scattered.’
28 Amma bayan na tashi, zan sha gabanku zuwa Galili.”
Yet, after I have risen, I shall go before you into Galilee.”
29 Bitrus ya ce, “Ko da duka sun ja da baya suka bar ka, ba zan bar ka ba.”
“Even if every one else falls away,” said Peter, “yet I shall not.”
30 Yesu ya ce, “Gaskiya nake faɗa maka, yau, tabbatacce, a daren nan, kafin zakara yă yi cara sau biyukai da kanka za ka yi mūsun sanina sau uku.”
“I tell you,” answered Jesus, “that you yourself today — yes, this very night — before the cock crows twice, will disown me three times.”
31 Amma Bitrus ya yi ta nanatawa da ƙarfi ya ce, “Ko da zan mutu tare da kai, ba zan taɓa yin mūsun saninka ba.” Duk sauran ma suka ce haka.
But Peter vehemently protested: “Even if I must die with you, I shall never disown you!” And they all said the same.
32 Suka tafi wani wurin da ake kira Getsemane, Yesu ya kuma ce wa almajiransa, “Ku zauna a nan, yayinda ni kuwa in yi addu’a.”
Presently they came to a garden known as Gethsemane, and Jesus said to his disciples “Sit down here while I pray.”
33 Ya tafi tare da Bitrus, Yaƙub da kuma Yohanna. Sai ya fara baƙin ciki da damuwa ƙwarai.
He took with him Peter, James, and John; and began to show signs of great dismay and deep distress of mind.
34 Sai ya ce musu, “Raina yana cike da baƙin ciki har ma kamar zan mutu. Ku dakata a nan ku yi tsaro.”
“I am sad at heart,” he said, “sad even to death; wait here, and watch.”
35 Sai ya yi gaba kaɗan, ya fāɗi a ƙasa, ya yi addu’a, ya ce in mai yiwuwa ne, a ɗauke masa wannan sa’a.
Going on a little further, he threw himself on the ground, and began to pray that, if it were possible, he might be spared that hour.
36 Ya ce, “Ya Abba, Uba, kome mai yiwuwa ne a gare ka. Ka ɗauke mini wannan kwaf. Amma ba abin da nake so ba, sai dai abin da kake so.”
“Abba, Father,” he said, “all things are possible to thee; take away this cup from me; yet, not what I will, but what thou willest.”
37 Sai ya koma wajen almajiransa, ya same su suna barci. Ya ce wa Bitrus, “Siman, kana barci ne? Ka kāsa yin tsaro na sa’a ɗaya?
Then he came and found the three Apostles asleep. “Simon,” he said to Peter, “are you asleep? Could not you watch for one hour?
38 Ku yi tsaro, ku kuma yi addu’a, domin kada ku fāɗi cikin jarraba. Ruhu yana so, sai dai jiki raunana ne.”
Watch and pray,” he said to them all, “that you may not fall into temptation. True, the spirit is eager, but human nature is weak.”
39 Ya sāke komawa, ya maimaita addu’ar da ya yi.
Again he went away, and prayed in the same words;
40 Da ya dawo, ya sāke tarar da su suna barci, domin barci ya cika musu ido. Suka rasa abin da za su ce masa.
and coming back again he found them asleep, for their eyes were heavy; and they did not know what to say to him.
41 Da ya koma sau na uku, sai ya ce musu, “Har yanzu kuna barci, kuna hutawa ba? Ya isa! Lokaci ya yi. Duba an ba da Ɗan Mutum a hannun masu zunubi.
A third time he came, and said to them: “Sleep on now, and rest yourselves. Enough! My time has come. Hark! the Son of Man is being betrayed into the hands of wicked men.
42 Ku tashi! Mu tafi! Ga mai bashe ni ɗin yana zuwa!”
Up, and let us be going. Look! my betrayer is close at hand.”
43 Yana cikin magana ke nan, sai Yahuda, ɗaya daga cikin Sha Biyun ya bayyana. Ya zo tare da taro da suke riƙe da takuba da sanduna. Manyan firistoci da malaman dokoki, da kuma dattawa ne suka turo taron.
And just then, while he was still speaking, Judas, who was one of the Twelve, came up; and with him a crowd of people, with swords and clubs, sent by the Chief Priests, the Teachers of the Law, and the Councillors.
44 Mai bashe shi ɗin ya riga ya shirya alama da su cewa, “Wanda na yi wa sumba, shi ne mutumin, ku kama shi, ku riƙe sosai.”
Now the betrayer had arranged a signal with them. “The man whom I kiss,” he had said, “will be the one; arrest him and take him away safely.”
45 Nan da nan Yahuda ya je wurin Yesu ya ce, “Rabbi!” Ya kuma yi masa sumba.
As soon as Judas came, he went up to Jesus at once, and said: “Rabbi!” and kissed him.
46 Mutanen kuwa suka kama Yesu, suka riƙe shi.
Then the men seized Jesus, and arrested him.
47 Sai wani cikin waɗanda suke tsattsaye kusa ya zāre takobinsa, ya sare kunnen bawan babban firist.
One of those who were standing by drew his sword, and struck at the High Priest’s servant, and cut off his ear.
48 Yesu ya ce, “Ina jagoran wani tawaye ne da kuka fito da takuba da kuma sanduna domin ku kama ni?
But Jesus interposed, and said to the men: “Have you come out, as if after a robber, with swords and clubs, to take me?
49 Kowace rana ina tare da ku, ina koyarwa a filin haikali, ba ku kama ni ba. Amma dole a cika Nassi.”
I have been among you day after day in the Temple Courts teaching, and yet you did not arrest me; but this is in fulfilment of the Scriptures.”
50 Sai kowa ya yashe shi ya gudu.
And all the Apostles forsook him, and fled.
51 Wani saurayin da ba ya sanye da kome sai rigar lilin, yana bin Yesu. Da suka yi ƙoƙarin kama shi,
One young man did indeed follow him, wrapped only in a linen sheet. They tried to arrest him;
52 sai ya gudu ya bar rigarsa, ya gudu tsirara.
but he left the sheet in their hands, and fled naked.
53 Suka kai Yesu wajen babban firist, sai dukan manyan firistoci, dattawa da kuma malaman dokoki suka taru.
Then they took Jesus to the High Priest; and all the Chief Priests, the Councillors, and the Teachers of the Law assembled.
54 Bitrus ya bi shi daga nesa, har cikin filin gidan babban firist. A can, ya zauna tare da masu gadi, yana jin ɗumin wuta.
Peter, who had followed Jesus at a distance into the court-yard of the High Priest, was sitting there among the police-officers, warming himself at the blaze of the fire.
55 Manyan firistoci da dukan’yan Majalisa, suka shiga neman shaidar laifin da za a tabbatar a kan Yesu, domin su kashe shi. Amma ba su sami ko ɗaya ba.
Meanwhile the Chief Priest and the whole of the High Council were trying to get such evidence against Jesus as would warrant his being put to death, but they could not find any;
56 Da yawa suka ba da shaidar ƙarya a kansa, amma shaidarsu ba tă zo ɗaya ba.
for, though there were many who gave false evidence against him, yet their evidence did not agree.
57 Sai waɗansu suka miƙe tsaye, suka ba da wannan shaida ƙarya a kansa, suka ce,
Presently some men stood up, and gave this false evidence against him —
58 “Mun ji shi ya ce, ‘Zan rushe wannan haikali da mutum ya gina, cikin kwana uku, in sāke gina wani wanda ba ginin mutum ba.’”
“We ourselves heard him say ‘I will destroy this Temple made with hands, and in three days build another made without hands.’”
59 Duk da haka ma, shaidarsu ba tă zo ɗaya ba.
Yet not even on that point did their evidence agree.
60 Sai babban firist ya tashi a gabansu, ya tambayi Yesu ya ce, “Ba za ka amsa ba? Wane shaida ke nan waɗannan mutane suke kawowa a kanka?”
Then the High Priest stood forward, and questioned Jesus. “Have you no answer to make?” he asked. “What is this evidence which these men are giving against you?”
61 Amma Yesu ya yi shiru, bai kuwa amsa ba. Babban firist ya sāke tambayarsa ya ce, “Kai ne Kiristi, Ɗan Mai Albarka?”
But Jesus remained silent, and made no answer. A second time the High Priest questioned him. “Are you,” he asked, “the Christ, the Son of the Blessed One?”
62 Yesu ya ce, “Ni ne. Za ku kuwa ga Ɗan Mutum yana zaune a hannun dama na Mai Iko, yana kuma zuwa a cikin gizagizan sama.”
“I am,” replied Jesus, “and you shall all see the Son of Man sitting on the right hand of the Almighty; and ‘coming in the clouds of heaven’.”
63 Babban firist ya yage tufafinsa, ya yi ce, “Ina dalilin neman waɗansu shaidu kuma?
At this the High Priest tore his vestments. “Why do we want any more witnesses?” he exclaimed.
64 Kun dai ji saɓon. Me kuka gani?” Duka suka yanke masa hukuncin kisa.
“You heard his blasphemy? What is your verdict?” They all condemned him, declaring that he deserved death.
65 Sai waɗansu suka fara tattofa masa miyau, suka rufe masa idanu, suka bubbuge shi da hannuwansu, suka ce, “Yi annabci!” Masu gadin kuma suka ɗauke shi, suka yi masa duka.
Some of those present began to spit at him, and to blindfold his eyes, and strike him, saying, as they did so, “Now play the Prophet!” and even the police-officers received him with blows.
66 Yayinda Bitrus yake ƙasa a filin gidan, sai wata yarinya, baiwa, ɗaya daga cikin ma’aikatan babban firist, ta zo can.
While Peter was in the court-yard down below, one of the High Priest’s maidservants came up;
67 Da ta ga Bitrus yana jin ɗumi, sai ta dube shi da kyau. Ta ce, “Kai ma kana tare da Yesu, Banazare.”
and, seeing Peter warming himself, she looked closely at him, and exclaimed: “Why, you were with Jesus, the Nazarene!”
68 Amma ya yi mūsu ya ce, “Ban san abin da kike magana ba, balle ma in fahimce ki.” Sai ya fita zuwa zaure.
But Peter denied it. “I do not know or understand what you mean,” he replied. Then he went out into the porch;
69 Da baiwar ta gan shi a can, sai ta sāke gaya wa waɗanda suke tsattsaye a wurin, ta ce, “Wannan mutum yana ɗaya daga cikinsu.”
and there the maidservant, on seeing him, began to say again to the by-standers: “This is one of them!”
70 Sai ya sāke yin musu. Bayan ɗan lokaci kaɗan, sai waɗanda suke tsattsaye kusa suka ce wa Bitrus, “Lalle, kana ɗaya daga cikinsu, gama kai mutumin Galili ne.”
But Peter again denied it. Soon afterwards the bystanders again said to him: “You certainly are one of them; why you are a Galilean!”
71 Sai ya fara la’antar kansa, yana rantsuwa musu, yana cewa, “Ban san wannan mutumin da kuke magana a kai ba.”
But he began to swear with the most solemn imprecations: “I do not know the man you are speaking about.”
72 Nan da nan zakara ya yi cara sau na biyu. Sai Bitrus ya tuna da maganar da Yesu ya yi masa cewa, “Kafin zakara yă yi cara sau biyu, za ka yi mūsun sanina sau uku.” Sai ya fashe da kuka.
At that moment, for the second time, a cock crowed; and Peter remembered the words that Jesus had said to him — ‘Before a cock has crowed twice, you will disown me three times’; and, as he thought of it, he began to weep.