< Markus 14 >
1 To, saura kwana biyu ne kaɗai a yi Bikin Ƙetarewa da Bikin Burodi Marar Yisti, sai manyan firistoci da malaman dokoki, suka nemi wani dalili su kama Yesu a ɓoye, su kashe.
And after two days, was the passover of unleavened cakes. And the chief priests and the Scribes sought how they might take him by stratagem, and kill him.
2 Suka ce, “Ba a lokacin Biki ba, don kada mutane su yi tawaye.”
But they said: Not on the festival, lest there be commotion among the people.
3 Yayinda yake a Betani, a gidan wani mutumin da ake kira Siman Kuturu, yana cin abinci, sai wata mace ta zo da wani ɗan tulu na turaren alabasta da aka yi da nardi zalla, mai tsadan gaske. Ta fasa tulun, ta kuma zuba turaren a kansa.
And when he was at Bethany in the house of Simon the leper, as he reclined, a woman came having an alabaster box of precious ointment of spikenard, of great price; and she opened and poured upon the head of Jesus.
4 Waɗansu daga cikin waɗanda suke wurin, suka ji haushi, suka ce wa juna, “Me ya sa za a ɓata turaren nan haka?
And there were certain of the disciples, who were dissatisfied among themselves, and said: Why was this waste of the ointment?
5 Da an sayar da shi, ai, da an sami kuɗi fiye da albashi ma’aikaci na shekara guda, a ba wa matalauta. Sai suka tsawata mata da zafi.”
For it might have been sold for more than three hundred denarii, and been given to the poor. And they were indignant at her.
6 Yesu ya ce, “Ku ƙyale ta mana. Don me kuke damunta? Ta yi abu mai kyau a gare ni.
But Jesus said: Let her alone; why trouble ye her? She hath done an excellent act towards me.
7 Matalauta dai suna tare da ku kullum, za ku kuma iya taimakonsu a duk lokacin da kuke so. Amma ni ba zan kasance da ku kullum ba.
For the poor ye have always with you; and when ye please, ye can do them kind offices: but I am not always with you.
8 Ta yi abin da ta iya yi. Ta zuba turare a jikina kafin lokaci, don shirin jana’izata.
What was in her power, she hath done; and by anticipation, hath perfumed my body, as if for burial.
9 Gaskiya nake gaya muku, duk inda aka yi wa’azin bishara ko’ina a duniya, za a faɗi abin da ta yi, domin tunawa da ita.”
Verily I say to you, That wherever this my gospel shall be proclaimed, in all the world, this also which she hath done shall be told in memory of her.
10 Sai Yahuda Iskariyot, ɗaya daga cikin Sha Biyun nan, ya je wajen manyan firistoci don yă bashe Yesu a gare su.
And Judas Iscariot, one of the twelve, went to the chief priests, in order to betray Jesus to them.
11 Suka yi murna da jin haka, suka yi alkawari za su ba shi kuɗi. Don haka, ya fara neman zarafi yă ba da shi.
And when they heard him, they rejoiced; and they promised to give him money. And he sought for opportunity to betray him.
12 A rana ta fari ta Bikin Burodi Marar Yisti, lokacin da akan yanka ɗan ragon hadayar kafara, bisa ga al’ada ta tunawa da Bikin Ƙetarewa, sai almajiran Yesu suka tambaye shi, suka ce, “Ina kake so mu je mu shirya maka wurin da za ka ci Bikin Ƙetarewa?”
And on the first day of unleavened cakes, on which the Jews slay the passover, his disciples said to him: Where wilt thou that we go, and prepare for thee to eat the passover?
13 Sai ya aiki biyu daga cikin almajiransa ya ce, “Ku shiga cikin birni, za ku sadu da wani ɗauke da tulun ruwa. Ku bi shi.
And he sent two of his disciples, and said to them: Go ye to the city, and behold, there will meet you a man bearing a pitcher of water. Go ye after him,
14 Gidan da ya shiga, ku gaya wa maigidan cewa, ‘Malam yana tambaya, ina ɗakin baƙina, inda zan ci Bikin Ƙetarewa tare da almajiraina?’
and where he entereth in, say ye to the lord of the house: Our Rabbi saith, Where is the place of refreshment, in which I may eat the passover with my disciples?
15 Zai nuna muku wani babban ɗakin sama da aka shirya domin baƙi. Ku yi mana shirin a can.”
And lo, he will show you a large upper room, furnished and prepared: there make ready for us.
16 Almajiran suka tafi, suka shiga cikin birnin, suka kuwa tarar da kome kamar yadda Yesu ya faɗa musu. Sai suka shirya Bikin Ƙetarewa.
And his disciples went, and entered the city, and found as he had told them: and they made ready the passover.
17 Da yamma ta yi, sai Yesu ya zo tare da Sha Biyun.
And when it was evening, he came with his twelve.
18 Yayinda suke cin abinci a tebur, sai ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, ɗaya daga cikinku zai bashe ni, wani wanda yake ci tare da ni.”
And as they reclined and ate, Jesus said: Verily I say to you, That one of you that eateth with me, will betray me.
19 Suka cika da baƙin ciki, da ɗaya-ɗaya suka ce masa, “Tabbatacce, ba ni ba ne, ko?”
And they began to be distressed. And they said to him, one by one, Is it I?
20 Ya ce, “Ɗaya daga cikin Sha Biyun ne, wanda yake ci tare da ni a kwano.
And he said to them: It is one of the twelve that dippeth with me in the dish.
21 Ɗan Mutum zai tafi kamar yadda yake a rubuce game da shi, amma kaiton mutumin da ya bashe Ɗan Mutum! Zai fi masa, da ba a haife shi ba.”
And the Son of man goeth, as it is written of him: but woe to that man, by whom the Son of man is betrayed. Better would it have been for that man, if he had not been born.
22 Yayinda suke cin abinci, sai Yesu ya ɗauki burodi, ya yi godiya, ya kakkarya, ya ba wa almajiransa, yana cewa, “Ku karɓa, wannan jikina ne.”
And as they were eating, Jesus took bread, and blessed, and brake, and gave to them, and said to them: Take; this is my body.
23 Sai kuma ya ɗauki kwaf ruwan inabi, ya yi godiya, ya kuma miƙa musu, dukansu suka sha daga ciki.
And he took the cup, and gave thanks, and blessed, and gave to them. And they all drank of it.
24 Sai ya ce musu, “Wannan jinina ne na alkawari, wanda aka zubar da shi saboda mutane da yawa.
And he said to them: This is my blood of the new testament, which is shed in behalf of many.
25 Gaskiya nake gaya muku, ‘Ba zan ƙara sha daga’ya’yan inabi ba, sai ranan nan, da zan sha shi sabo a mulkin Allah.’”
Verily I say to you, That I will not drink again of the product of the vine, until the day in which I shall drink it anew in the kingdom of God.
26 Da suka rera waƙa, sai suka fita, suka tafi Dutsen Zaitun.
And they sang praise, and went out to the mount of Olives.
27 Yesu ya ce musu, “Dukanku za ku ja da baya ku bar ni, gama yana a rubuce cewa, “‘Zan bugi makiyayin tumaki, tumakin kuwa za su warwatse.’
And Jesus said to them: All of you will this night be stumbled in me: for it is written, " I will smite the shepherd, and his sheep will be scattered."
28 Amma bayan na tashi, zan sha gabanku zuwa Galili.”
And when I am risen, I will precede you into Galilee.
29 Bitrus ya ce, “Ko da duka sun ja da baya suka bar ka, ba zan bar ka ba.”
And Cephas said to him: Though they all should be stumbled, yet I will not be.
30 Yesu ya ce, “Gaskiya nake faɗa maka, yau, tabbatacce, a daren nan, kafin zakara yă yi cara sau biyukai da kanka za ka yi mūsun sanina sau uku.”
Jesus said to him: Verily I say to thee, That this day, on this night, before the cock shall crow twice, thou wilt thrice deny me.
31 Amma Bitrus ya yi ta nanatawa da ƙarfi ya ce, “Ko da zan mutu tare da kai, ba zan taɓa yin mūsun saninka ba.” Duk sauran ma suka ce haka.
And he said, in addition: If I were to die with thee, I will not deny thee, my Lord. And like him, spake all the disciples.
32 Suka tafi wani wurin da ake kira Getsemane, Yesu ya kuma ce wa almajiransa, “Ku zauna a nan, yayinda ni kuwa in yi addu’a.”
And they came to the place called Gethsemane; and he said to his disciples, Sit ye here, while I pray.
33 Ya tafi tare da Bitrus, Yaƙub da kuma Yohanna. Sai ya fara baƙin ciki da damuwa ƙwarai.
And he took with him Cephas and James and John, and began to be gloomy and distressed.
34 Sai ya ce musu, “Raina yana cike da baƙin ciki har ma kamar zan mutu. Ku dakata a nan ku yi tsaro.”
And he said to them: My soul hath anguish, even to death. Wait for me here, and be watchful.
35 Sai ya yi gaba kaɗan, ya fāɗi a ƙasa, ya yi addu’a, ya ce in mai yiwuwa ne, a ɗauke masa wannan sa’a.
And he advanced a little, and fell upon the ground, and prayed that, if it were possible, the hour might pass from him.
36 Ya ce, “Ya Abba, Uba, kome mai yiwuwa ne a gare ka. Ka ɗauke mini wannan kwaf. Amma ba abin da nake so ba, sai dai abin da kake so.”
And he said: Father, my Father, thou canst do all things. Let this cup pass from me. Yet not my pleasure, but thine.
37 Sai ya koma wajen almajiransa, ya same su suna barci. Ya ce wa Bitrus, “Siman, kana barci ne? Ka kāsa yin tsaro na sa’a ɗaya?
And he came and found them sleeping. And he said to Cephas: Sleepest thou, Simon? Couldst thou not watch with me one hour?
38 Ku yi tsaro, ku kuma yi addu’a, domin kada ku fāɗi cikin jarraba. Ruhu yana so, sai dai jiki raunana ne.”
Watch and pray, lest ye enter into temptation. The spirit is willing and ready, but the body is weak.
39 Ya sāke komawa, ya maimaita addu’ar da ya yi.
And he went again and prayed, speaking the same language.
40 Da ya dawo, ya sāke tarar da su suna barci, domin barci ya cika musu ido. Suka rasa abin da za su ce masa.
And returning he came again and found them sleeping, for their eyes were heavy. And they knew not what to say to him.
41 Da ya koma sau na uku, sai ya ce musu, “Har yanzu kuna barci, kuna hutawa ba? Ya isa! Lokaci ya yi. Duba an ba da Ɗan Mutum a hannun masu zunubi.
And he came the third time, and said to them: Sleep on now, and take rest. The end is near; the hour is come; and lo, the Son of man is betrayed into the hands of sinners.
42 Ku tashi! Mu tafi! Ga mai bashe ni ɗin yana zuwa!”
Arise ye; let us go. Lo, he that betrayeth me is at hand.
43 Yana cikin magana ke nan, sai Yahuda, ɗaya daga cikin Sha Biyun ya bayyana. Ya zo tare da taro da suke riƙe da takuba da sanduna. Manyan firistoci da malaman dokoki, da kuma dattawa ne suka turo taron.
And while he was yet speaking, Judas Iscariot, one of the twelve, arrived, and much people, with swords and clubs, from before the chief priests and Scribes and Elders
44 Mai bashe shi ɗin ya riga ya shirya alama da su cewa, “Wanda na yi wa sumba, shi ne mutumin, ku kama shi, ku riƙe sosai.”
And the traitor who betrayed him, had given them a sign, and said: He whom I shall kiss is the man. Seize promptly, and lead him away
45 Nan da nan Yahuda ya je wurin Yesu ya ce, “Rabbi!” Ya kuma yi masa sumba.
And immediately he came up, and said to him: Rabbi, Rabbi; and kissed him.
46 Mutanen kuwa suka kama Yesu, suka riƙe shi.
And they laid hands on him and took him.
47 Sai wani cikin waɗanda suke tsattsaye kusa ya zāre takobinsa, ya sare kunnen bawan babban firist.
And one of them that stood by, drew a sword, and smote a servant of the high priest, and cut off his ear.
48 Yesu ya ce, “Ina jagoran wani tawaye ne da kuka fito da takuba da kuma sanduna domin ku kama ni?
And Jesus answered and said to them: Have ye come out against me, as against a robber; with swords and clubs, to apprehend me?
49 Kowace rana ina tare da ku, ina koyarwa a filin haikali, ba ku kama ni ba. Amma dole a cika Nassi.”
I was daily with you, while I taught in the temple, and ye seized me not. But this occurs, that the scriptures may be fulfilled.
50 Sai kowa ya yashe shi ya gudu.
Then his disciples left him and fled.
51 Wani saurayin da ba ya sanye da kome sai rigar lilin, yana bin Yesu. Da suka yi ƙoƙarin kama shi,
And a young man followed after him, who was clad with a linen cloth on his naked body: and they laid hold of him.
52 sai ya gudu ya bar rigarsa, ya gudu tsirara.
And he left the linen cloth, and fled naked.
53 Suka kai Yesu wajen babban firist, sai dukan manyan firistoci, dattawa da kuma malaman dokoki suka taru.
And they led away Jesus to Caiaphas the high priest. And with him were assembled all the chief priests and the Scribes and the Elders.
54 Bitrus ya bi shi daga nesa, har cikin filin gidan babban firist. A can, ya zauna tare da masu gadi, yana jin ɗumin wuta.
And Simon followed after him, at a distance; into the hall of the high priest; and he sat with the servants, and warmed himself by the fire.
55 Manyan firistoci da dukan’yan Majalisa, suka shiga neman shaidar laifin da za a tabbatar a kan Yesu, domin su kashe shi. Amma ba su sami ko ɗaya ba.
And the chief priests and all the assembly sought for testimony against Jesus, to put him to death: but they found it not.
56 Da yawa suka ba da shaidar ƙarya a kansa, amma shaidarsu ba tă zo ɗaya ba.
For while many testified against him, their testimonies were inadequate.
57 Sai waɗansu suka miƙe tsaye, suka ba da wannan shaida ƙarya a kansa, suka ce,
And some false witnesses stood up against him, and said:
58 “Mun ji shi ya ce, ‘Zan rushe wannan haikali da mutum ya gina, cikin kwana uku, in sāke gina wani wanda ba ginin mutum ba.’”
We have heard him say: I will destroy this temple, which is made with hands; and in three days I will build another not made with hands.
59 Duk da haka ma, shaidarsu ba tă zo ɗaya ba.
Nor even thus were their testimonies adequate.
60 Sai babban firist ya tashi a gabansu, ya tambayi Yesu ya ce, “Ba za ka amsa ba? Wane shaida ke nan waɗannan mutane suke kawowa a kanka?”
And the high priest arose in the midst, and interrogated Jesus and said: Returnest thou no answer? What do these testify against thee?
61 Amma Yesu ya yi shiru, bai kuwa amsa ba. Babban firist ya sāke tambayarsa ya ce, “Kai ne Kiristi, Ɗan Mai Albarka?”
And Jesus was silent, and made no reply. And again the chief priest interrogated him, and said: Art thou the Messiah, the Son of the Blessed?
62 Yesu ya ce, “Ni ne. Za ku kuwa ga Ɗan Mutum yana zaune a hannun dama na Mai Iko, yana kuma zuwa a cikin gizagizan sama.”
And Jesus said to him: I am. And ye will see the Son of man sitting on the right hand of power, and he will come on the clouds of heaven.
63 Babban firist ya yage tufafinsa, ya yi ce, “Ina dalilin neman waɗansu shaidu kuma?
And the high priest rent his tunic, and said: What need of witnesses have we, any more?
64 Kun dai ji saɓon. Me kuka gani?” Duka suka yanke masa hukuncin kisa.
Behold, from his own mouth ye have heard blasphemy. How doth it appear to you? And they all decided, that he deserved to die.
65 Sai waɗansu suka fara tattofa masa miyau, suka rufe masa idanu, suka bubbuge shi da hannuwansu, suka ce, “Yi annabci!” Masu gadin kuma suka ɗauke shi, suka yi masa duka.
And some began to spit in his face, and to buffet him, saying: Prophesy thou. And the servants smote him on the cheeks.
66 Yayinda Bitrus yake ƙasa a filin gidan, sai wata yarinya, baiwa, ɗaya daga cikin ma’aikatan babban firist, ta zo can.
And as Simon was below in the court, a maid of the high priest came,
67 Da ta ga Bitrus yana jin ɗumi, sai ta dube shi da kyau. Ta ce, “Kai ma kana tare da Yesu, Banazare.”
and saw him warming himself; and she looked upon him, and said to him: And thou too wast with Jesus the Nazarean.
68 Amma ya yi mūsu ya ce, “Ban san abin da kike magana ba, balle ma in fahimce ki.” Sai ya fita zuwa zaure.
But he denied, and said: l know not what thou sayest. And he went out into the porch; and the cock crew.
69 Da baiwar ta gan shi a can, sai ta sāke gaya wa waɗanda suke tsattsaye a wurin, ta ce, “Wannan mutum yana ɗaya daga cikinsu.”
And the maid saw him again, and she began to say to those standing by, This man also is one of them.
70 Sai ya sāke yin musu. Bayan ɗan lokaci kaɗan, sai waɗanda suke tsattsaye kusa suka ce wa Bitrus, “Lalle, kana ɗaya daga cikinsu, gama kai mutumin Galili ne.”
And he again denied it. And a little after, those standing there said again to Cephas: Surely, thou art one of them; for thou art likewise a Galilean, and thy speech answers to it.
71 Sai ya fara la’antar kansa, yana rantsuwa musu, yana cewa, “Ban san wannan mutumin da kuke magana a kai ba.”
And he began to imprecate, and swore: I know not that man, of whom ye speak.
72 Nan da nan zakara ya yi cara sau na biyu. Sai Bitrus ya tuna da maganar da Yesu ya yi masa cewa, “Kafin zakara yă yi cara sau biyu, za ka yi mūsun sanina sau uku.” Sai ya fashe da kuka.
And immediately the cock crew the second time. And Simon remembered the declaration of Jesus, who said to him: Before the cock shall crow twice, thou wilt thrice deny me. And he began to weep.