< Markus 14 >
1 To, saura kwana biyu ne kaɗai a yi Bikin Ƙetarewa da Bikin Burodi Marar Yisti, sai manyan firistoci da malaman dokoki, suka nemi wani dalili su kama Yesu a ɓoye, su kashe.
Now it was the Passover and the Unleavened [cakes], after two days. And the High-priests and Scribes were seeking, how, with guile, they might secure, and lay him;
2 Suka ce, “Ba a lokacin Biki ba, don kada mutane su yi tawaye.”
for they were saying—Not in the feast, lest there be an uproar of the people.
3 Yayinda yake a Betani, a gidan wani mutumin da ake kira Siman Kuturu, yana cin abinci, sai wata mace ta zo da wani ɗan tulu na turaren alabasta da aka yi da nardi zalla, mai tsadan gaske. Ta fasa tulun, ta kuma zuba turaren a kansa.
And, he being in Bethany, in the house of Simon the leper, as he was reclining, there came a woman, holding an alabaster-jar of perfume, pure spikenard, very costly; and breaking the jar she was pouring down [the perfume], upon his head.
4 Waɗansu daga cikin waɗanda suke wurin, suka ji haushi, suka ce wa juna, “Me ya sa za a ɓata turaren nan haka?
But there were some much displeased among themselves—To what end hath, this waste of the perfume happened?
5 Da an sayar da shi, ai, da an sami kuɗi fiye da albashi ma’aikaci na shekara guda, a ba wa matalauta. Sai suka tsawata mata da zafi.”
For this perfume could have been sold for above three hundred denaries, and given unto the destitute! and they were indignant with her.
6 Yesu ya ce, “Ku ƙyale ta mana. Don me kuke damunta? Ta yi abu mai kyau a gare ni.
But, Jesus, said—Let her alone! Why are ye reproaching, her? A seemly work, hath she wrought, in me;
7 Matalauta dai suna tare da ku kullum, za ku kuma iya taimakonsu a duk lokacin da kuke so. Amma ni ba zan kasance da ku kullum ba.
For, always, have ye, the destitute, with you, and whensoever ye please, ye can, unto them, [at any time] do well! But, me, not, always, have ye.
8 Ta yi abin da ta iya yi. Ta zuba turare a jikina kafin lokaci, don shirin jana’izata.
What she had, she used, —She took it beforehand to anoint my body for the burial;
9 Gaskiya nake gaya muku, duk inda aka yi wa’azin bishara ko’ina a duniya, za a faɗi abin da ta yi, domin tunawa da ita.”
And, verily, say unto you—Wheresoever the glad-message shall be proclaimed throughout the whole world, —also what she did, will be told for a memorial of her.
10 Sai Yahuda Iskariyot, ɗaya daga cikin Sha Biyun nan, ya je wajen manyan firistoci don yă bashe Yesu a gare su.
And, Judas Iscariot, who was one of he twelve, went away unto the High-priests, that, him, he might deliver up unto them.
11 Suka yi murna da jin haka, suka yi alkawari za su ba shi kuɗi. Don haka, ya fara neman zarafi yă ba da shi.
Now, when they heard, they rejoiced, and promised to give him, silver; and he was seeking how, at a favourable opportunity, he might, deliver him up.
12 A rana ta fari ta Bikin Burodi Marar Yisti, lokacin da akan yanka ɗan ragon hadayar kafara, bisa ga al’ada ta tunawa da Bikin Ƙetarewa, sai almajiran Yesu suka tambaye shi, suka ce, “Ina kake so mu je mu shirya maka wurin da za ka ci Bikin Ƙetarewa?”
And, on the first day of the unleavened cakes, when, the passover, they were slaying, his disciples say unto him—Where wilt thou, we depart and make ready, that thou mayest eat the passover?
13 Sai ya aiki biyu daga cikin almajiransa ya ce, “Ku shiga cikin birni, za ku sadu da wani ɗauke da tulun ruwa. Ku bi shi.
And he sendeth forth two of his disciples, and saith unto them—Go your way into the city, and there will meet you a man, a jar of water, bearing, —follow him;
14 Gidan da ya shiga, ku gaya wa maigidan cewa, ‘Malam yana tambaya, ina ɗakin baƙina, inda zan ci Bikin Ƙetarewa tare da almajiraina?’
and, wheresoever he shall enter, say ye unto the householder—The teacher, saith, Where is my lodging, where, the passover, with my disciples, I may eat?
15 Zai nuna muku wani babban ɗakin sama da aka shirya domin baƙi. Ku yi mana shirin a can.”
And, he, unto you, will shew, a large upper-room, spread ready, and, there, make ye ready for us.
16 Almajiran suka tafi, suka shiga cikin birnin, suka kuwa tarar da kome kamar yadda Yesu ya faɗa musu. Sai suka shirya Bikin Ƙetarewa.
And the disciples went forth, and came into the city, and found, according as he had said unto them, —and they made ready the passover.
17 Da yamma ta yi, sai Yesu ya zo tare da Sha Biyun.
And, when evening arrived, he cometh, with the twelve.
18 Yayinda suke cin abinci a tebur, sai ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, ɗaya daga cikinku zai bashe ni, wani wanda yake ci tare da ni.”
And, as they were reclining and eating, Jesus said—Verily, I say unto you—One from among you, will deliver me up, he that is eating with me.
19 Suka cika da baƙin ciki, da ɗaya-ɗaya suka ce masa, “Tabbatacce, ba ni ba ne, ko?”
They began to be grieved, and to be saying unto him, one by one, —Can it be, I?
20 Ya ce, “Ɗaya daga cikin Sha Biyun ne, wanda yake ci tare da ni a kwano.
And, he, said unto them—One of the twelve, he that is dipping with me into the [one] bowl:
21 Ɗan Mutum zai tafi kamar yadda yake a rubuce game da shi, amma kaiton mutumin da ya bashe Ɗan Mutum! Zai fi masa, da ba a haife shi ba.”
Because, the Son of Man, indeed, goeth his way, —according as it is written concerning him; but alas! for that man, through whom the Son of Man is being delivered up, —Well for him, if that man, had not been born!
22 Yayinda suke cin abinci, sai Yesu ya ɗauki burodi, ya yi godiya, ya kakkarya, ya ba wa almajiransa, yana cewa, “Ku karɓa, wannan jikina ne.”
And, as they were eating, taking a loaf, he blessed and brake, and gave unto them, and said—Take! this, is, my body;
23 Sai kuma ya ɗauki kwaf ruwan inabi, ya yi godiya, ya kuma miƙa musu, dukansu suka sha daga ciki.
And, taking a cup, he offered thanks, and gave unto them; and they, all, drank of it.
24 Sai ya ce musu, “Wannan jinina ne na alkawari, wanda aka zubar da shi saboda mutane da yawa.
And he said unto them—This, is, my blood of the covenant, that is to be poured out in behalf of many.
25 Gaskiya nake gaya muku, ‘Ba zan ƙara sha daga’ya’yan inabi ba, sai ranan nan, da zan sha shi sabo a mulkin Allah.’”
Verily, I say unto you—No more, will I in anywise drink of the fruit of the vine, until that day when I shall be drinking it new, in the kingdom of God.
26 Da suka rera waƙa, sai suka fita, suka tafi Dutsen Zaitun.
And, having sung praise, they went forth unto the Mount of Olives.
27 Yesu ya ce musu, “Dukanku za ku ja da baya ku bar ni, gama yana a rubuce cewa, “‘Zan bugi makiyayin tumaki, tumakin kuwa za su warwatse.’
And Jesus saith unto them—Ye, all, will find cause of stumbling, because it is written, —I will smite the shepherd, and, the sheep, will be scattered abroad;
28 Amma bayan na tashi, zan sha gabanku zuwa Galili.”
But, after my arising, I will go before you into Galilee.
29 Bitrus ya ce, “Ko da duka sun ja da baya suka bar ka, ba zan bar ka ba.”
And, Peter, said unto him—Even if, all, shall find cause of stumbling, certainly not, I.
30 Yesu ya ce, “Gaskiya nake faɗa maka, yau, tabbatacce, a daren nan, kafin zakara yă yi cara sau biyukai da kanka za ka yi mūsun sanina sau uku.”
And Jesus saith unto him—Verily, I say unto thee, thou, this day, in this night, before that twice a cock crow, thrice, will deny me.
31 Amma Bitrus ya yi ta nanatawa da ƙarfi ya ce, “Ko da zan mutu tare da kai, ba zan taɓa yin mūsun saninka ba.” Duk sauran ma suka ce haka.
But he, most vehemently, was saying—Even though I must needs die with thee, in nowise, will I, deny thee. Likewise, indeed, were, all besides, saying.
32 Suka tafi wani wurin da ake kira Getsemane, Yesu ya kuma ce wa almajiransa, “Ku zauna a nan, yayinda ni kuwa in yi addu’a.”
And they come into an estate the name of which is Gethsemane, and he saith unto his disciples—Sit ye here, while I pray.
33 Ya tafi tare da Bitrus, Yaƙub da kuma Yohanna. Sai ya fara baƙin ciki da damuwa ƙwarai.
And he taketh Peter and James and John with him, and began to be exceedingly amazed, and in great distress;
34 Sai ya ce musu, “Raina yana cike da baƙin ciki har ma kamar zan mutu. Ku dakata a nan ku yi tsaro.”
and he saith unto them—Encompassed with grief is my soul, unto death: Abide ye here, and be watching.
35 Sai ya yi gaba kaɗan, ya fāɗi a ƙasa, ya yi addu’a, ya ce in mai yiwuwa ne, a ɗauke masa wannan sa’a.
And, going forward a little, he fell upon the ground, and was praying that, if it were possible, the hour might pass from him;
36 Ya ce, “Ya Abba, Uba, kome mai yiwuwa ne a gare ka. Ka ɗauke mini wannan kwaf. Amma ba abin da nake so ba, sai dai abin da kake so.”
and was saying—Abba! O Father! All things, are possible to thee: Bear aside this cup from me; but not what, I, will, but what, thou, [wilt].
37 Sai ya koma wajen almajiransa, ya same su suna barci. Ya ce wa Bitrus, “Siman, kana barci ne? Ka kāsa yin tsaro na sa’a ɗaya?
And he cometh and findeth them sleeping, and saith unto Peter—Simon! art thou sleeping? Hadst thou not strength, one hour, to watch?
38 Ku yi tsaro, ku kuma yi addu’a, domin kada ku fāɗi cikin jarraba. Ruhu yana so, sai dai jiki raunana ne.”
Be watching and praying, that ye enter not into temptation: the, spirit, indeed, is willing, but, the flesh, weak.
39 Ya sāke komawa, ya maimaita addu’ar da ya yi.
And, again, departing, he prayed, [the same thing, saying].
40 Da ya dawo, ya sāke tarar da su suna barci, domin barci ya cika musu ido. Suka rasa abin da za su ce masa.
And, again, coming, he found them sleeping, for their eyes were being, weighed down, —and they knew not what to answer him.
41 Da ya koma sau na uku, sai ya ce musu, “Har yanzu kuna barci, kuna hutawa ba? Ya isa! Lokaci ya yi. Duba an ba da Ɗan Mutum a hannun masu zunubi.
And he cometh the third time, and saith unto them—Ye are sleeping the remaining time and taking your rest: —It is enough! the hour hath come! Lo! the Son of Man is being delivered up into the hands of sinners.
42 Ku tashi! Mu tafi! Ga mai bashe ni ɗin yana zuwa!”
Be rousing yourselves, let us be leading on! Lo! he that is delivering me up, hath drawn near.
43 Yana cikin magana ke nan, sai Yahuda, ɗaya daga cikin Sha Biyun ya bayyana. Ya zo tare da taro da suke riƙe da takuba da sanduna. Manyan firistoci da malaman dokoki, da kuma dattawa ne suka turo taron.
And, straightway, while yet he is speaking, Judas Iscariot, one of the twelve, cometh near, and, with him, a multitude, with swords and clubs, from the High-priests and the Scribes and the Elders.
44 Mai bashe shi ɗin ya riga ya shirya alama da su cewa, “Wanda na yi wa sumba, shi ne mutumin, ku kama shi, ku riƙe sosai.”
He that is delivering him up hath given an agreed sign unto them, saying—Whomsoever I shall kiss, he, it is! Secure him, and be leading away, safely.
45 Nan da nan Yahuda ya je wurin Yesu ya ce, “Rabbi!” Ya kuma yi masa sumba.
And, coming, straightway, stepping forward to him, he saith—Rabbi! and openly kissed him.
46 Mutanen kuwa suka kama Yesu, suka riƙe shi.
And, they, thrust their hands on him, and secured him.
47 Sai wani cikin waɗanda suke tsattsaye kusa ya zāre takobinsa, ya sare kunnen bawan babban firist.
[A certain] one of the by-standers, drawing a sword, smote the servant of the High priest, and took off his, ear.
48 Yesu ya ce, “Ina jagoran wani tawaye ne da kuka fito da takuba da kuma sanduna domin ku kama ni?
And Jesus, answering, said unto them—As against a robber, came ye forth, with swords and clubs, to arrest me?
49 Kowace rana ina tare da ku, ina koyarwa a filin haikali, ba ku kama ni ba. Amma dole a cika Nassi.”
Daily, was I with you, in the temple, teaching; and ye secured me not. But, that, the Scriptures, may be fulfilled…
50 Sai kowa ya yashe shi ya gudu.
And they, all, forsook, him, and fled.
51 Wani saurayin da ba ya sanye da kome sai rigar lilin, yana bin Yesu. Da suka yi ƙoƙarin kama shi,
And, a certain young man, was following with him, having cast about himself a fine Indian cloth, over his naked body, —and they are securing him;
52 sai ya gudu ya bar rigarsa, ya gudu tsirara.
but, he, leaving behind the cloth, fled naked.
53 Suka kai Yesu wajen babban firist, sai dukan manyan firistoci, dattawa da kuma malaman dokoki suka taru.
And they led away Jesus unto the High-priest; and all the High-priests and the Elders and the Scribes gather together.
54 Bitrus ya bi shi daga nesa, har cikin filin gidan babban firist. A can, ya zauna tare da masu gadi, yana jin ɗumin wuta.
And, Peter, afar of, followed him, as far as within, into the court of the High-priest; and was sitting with the attendants, and warming himself by the light.
55 Manyan firistoci da dukan’yan Majalisa, suka shiga neman shaidar laifin da za a tabbatar a kan Yesu, domin su kashe shi. Amma ba su sami ko ɗaya ba.
Now, the High-priest, and all the High-council, were seeking, against Jesus, testimony, with the intent to put him to death, —and were not finding any;
56 Da yawa suka ba da shaidar ƙarya a kansa, amma shaidarsu ba tă zo ɗaya ba.
for, many, were bearing false-witness against him, and the testimonies were not, agreed.
57 Sai waɗansu suka miƙe tsaye, suka ba da wannan shaida ƙarya a kansa, suka ce,
And some, standing up, were bearing false-witness against him, saying—
58 “Mun ji shi ya ce, ‘Zan rushe wannan haikali da mutum ya gina, cikin kwana uku, in sāke gina wani wanda ba ginin mutum ba.’”
We, heard him saying, I, will pull down this shrine, the one made by hand, and, in three days, another, not made by hand, will I raise.
59 Duk da haka ma, shaidarsu ba tă zo ɗaya ba.
And, not even so, was the testimony, agreed.
60 Sai babban firist ya tashi a gabansu, ya tambayi Yesu ya ce, “Ba za ka amsa ba? Wane shaida ke nan waɗannan mutane suke kawowa a kanka?”
And, the High-priest rising up into the midst, questioned Jesus, saying—Answerest thou, nothing? What are these, against thee, witnessing?
61 Amma Yesu ya yi shiru, bai kuwa amsa ba. Babban firist ya sāke tambayarsa ya ce, “Kai ne Kiristi, Ɗan Mai Albarka?”
But, he, was silent, and answered, nothing. Again, the High-priest was questioning him, and saith unto him—Art, thou, the Christ the Son of the Blessed?
62 Yesu ya ce, “Ni ne. Za ku kuwa ga Ɗan Mutum yana zaune a hannun dama na Mai Iko, yana kuma zuwa a cikin gizagizan sama.”
And Jesus said—I, am; and ye shall see the Son of Man—sitting, on the right hand, of Power, and coming with the clouds of heaven.
63 Babban firist ya yage tufafinsa, ya yi ce, “Ina dalilin neman waɗansu shaidu kuma?
And, the High-priest, having rent asunder his inner-garments, saith—What, further, need have we, of witnesses?
64 Kun dai ji saɓon. Me kuka gani?” Duka suka yanke masa hukuncin kisa.
Heard ye the profanity? What, to you, doth it appear? And they, all, condemned him to be, worthy, of, death.
65 Sai waɗansu suka fara tattofa masa miyau, suka rufe masa idanu, suka bubbuge shi da hannuwansu, suka ce, “Yi annabci!” Masu gadin kuma suka ɗauke shi, suka yi masa duka.
And some began to be spitting at him, and, covering up his face, and to be buffeting him, and saying to him—Prophesy! And, the attendants, with smart blows, took him.
66 Yayinda Bitrus yake ƙasa a filin gidan, sai wata yarinya, baiwa, ɗaya daga cikin ma’aikatan babban firist, ta zo can.
And, Peter, being, below in the court, there cometh one of the maid-servants of the High-priest;
67 Da ta ga Bitrus yana jin ɗumi, sai ta dube shi da kyau. Ta ce, “Kai ma kana tare da Yesu, Banazare.”
and, seeing Peter warming himself, having looked at him, saith—And, thou, wast, with the Nazarene—with Jesus.
68 Amma ya yi mūsu ya ce, “Ban san abin da kike magana ba, balle ma in fahimce ki.” Sai ya fita zuwa zaure.
But, he, denied, saying—I neither know [him], nor do I well understand what, thou, sayest; and went out into the porch.
69 Da baiwar ta gan shi a can, sai ta sāke gaya wa waɗanda suke tsattsaye a wurin, ta ce, “Wannan mutum yana ɗaya daga cikinsu.”
And, the maid-servant, seeing him, began, again, to be saying unto the by-standers—This one, is, from among them.
70 Sai ya sāke yin musu. Bayan ɗan lokaci kaɗan, sai waɗanda suke tsattsaye kusa suka ce wa Bitrus, “Lalle, kana ɗaya daga cikinsu, gama kai mutumin Galili ne.”
But, he, again, was denying. And, after a little again, the by-standers, were saying unto Peter—Truly, thou, art, from among them; for thou art, a Galilaean, also.
71 Sai ya fara la’antar kansa, yana rantsuwa musu, yana cewa, “Ban san wannan mutumin da kuke magana a kai ba.”
And, he, began to be cursing and swearing—I know not this man, of whom ye are speaking!
72 Nan da nan zakara ya yi cara sau na biyu. Sai Bitrus ya tuna da maganar da Yesu ya yi masa cewa, “Kafin zakara yă yi cara sau biyu, za ka yi mūsun sanina sau uku.” Sai ya fashe da kuka.
And, straightway, a second time, a cock, crowed; and Peter was reminded of the declaration, how Jesus had said to him—Before a cock, twice, crow, thrice, wilt thou deny me. And, when he thought thereon, he began to weep.