< Markus 13 >

1 Da yake barin haikalin, sai ɗaya daga cikin almajiransa ya ce masa, “Malam! Dubi irin manya-manyan duwatsun nan! Ka ga irin gine-ginen nan masu kyau mana!”
Saat Yesus meninggalkan rumah Tuhan, salah satu murid-Nya berkata kepada-Nya, “Guru, lihatlah batu-batu besar dan bangunan-bangunan megah ini!”
2 Yesu ya amsa ya ce, “Ka ga dukan manyan gine-ginen nan? Ba wani dutse a nan, da za a bari kan wani da ba za a rushe ba.”
Jawab Yesus, “Kalian perhatikan baik-baik semua bangunan besar ini? Tidak satu pun batu yang akan tersusun di atas batu yang lain. Semuanya akan dirobohkan.”
3 Da Yesu yana zaune a kan Dutsen Zaitun da yake ɗaura da haikali, sai Bitrus, Yaƙub, Yohanna da kuma Andarawus, suka tambaye shi a ɓoye, suka ce,
Saat Yesus duduk di Bukit Zaitun menghadap rumah Tuhan, Petrus, Yakobus, Yohanes, dan Andreas bertanya secara pribadi,
4 “Ka gaya mana, yaushe waɗannan abubuwa za su faru? Wace alama ce kuma za tă nuna cewa, duk waɗannan suna dab da cikawa?”
“Guru, tolong beritahukan kepada kami kapan ini akan terjadi. Apa tanda bahwa semua ini akan segera terpenuhi?”
5 Sai Yesu ya ce musu, “Ku lura fa kada wani yă ruɗe ku.
Yesus mulai memberitahukan mereka, kata-Nya, “Kalian harus hati-hati supaya tidak ada yang menipu kalian.
6 Da yawa za su zo a cikin sunana, suna cewa, ‘Ni ne shi.’ Za su kuwa ruɗi mutane da yawa.
Banyak orang akan datang dan berkata, ‘Aku adalah Kristus.’ Mereka akan menipu banyak orang.
7 Sa’ad da kuka ji labarun yaƙe-yaƙe da jita-jitar yaƙe-yaƙe, kada hankalinku yă tashi. Dole irin waɗannan abubuwa su faru. Amma ƙarshen tukuna.
Jangan kuatir jika kalian mendengar tentang perang di sekitar dan perang di tempat yang jauh. Hal-hal ini harus terjadi tetapi ini bukanlah akhir.
8 Al’umma za tă tasar wa al’umma, mulki kuma yă tasar wa mulki. Za a yi girgizar ƙasa a wurare dabam-dabam, a kuma yi yunwa. Waɗannan dai mafarin azabar naƙuda.
Bangsa akan berperang melawan bangsa, dan kerajaan melawan kerajaan. Akan ada gempa bumi di berbagai tempat, dan kelaparan juga. Ini baru awal, seperti ibu hamil yang rasa sakit untuk melahirkan.
9 “Dole ku yi zaman tsaro. Za a ba da ku ga hukuma, a kuma bulale ku a majami’u. Saboda ni kuma, za ku tsaya a gaban gwamnoni da sarakuna, domin ku ba da shaida a gabansu.
Hati-hati dengan dirimu sendiri! Mereka akan menyerahkan kalian ke pengadilan untuk diadili. Kalian akan dipukuli di tempat pertemuan orang Yahudi. Karena Aku, kalian harus berdiri di hadapan para gubernur dan raja, dan kalian akan menjadi saksi-Ku.
10 Dole sai an fara yin wa’azin bishara ga dukan al’ummai.
Sebelum akhir dunia ini, Kabar Baik tentang Aku harus disampaikan ke semua suku bangsa di seluruh dunia.
11 Sa’ad da aka kama ku, aka kuma kai ku don a yi muku shari’a, kada ku damu da abin da za ku faɗa. Sai dai ku faɗi abin da aka ba ku a lokacin. Gama ba ku kuke magana ba, Ruhu Mai Tsarki ne.
Saat mereka datang untuk menangkap dan mengadilimu, jangan kuatir tentang apa yang harus kamu jawab. Katakan saja apa yang kamu katakan pada saat itu, karena itu bukan kamu yang berbicara, tetapi Roh Kudus.
12 “Ɗan’uwa zai ba da ɗan’uwa a kashe. Mahaifi zai ba da ɗansa.’Ya’ya za su tayar wa iyayensu, su kuma sa a kashe su.
Saudara laki-laki akan menyerahkan saudaranya sendiri untuk dibunuh, dan seorang bapak akan menyerahkan anaknya untuk dibunuh. Anak-anak akan berbalik melawan orang tua mereka dan membuat mereka dihukum mati.
13 Dukan mutane za su ƙi ku saboda ni, amma wanda ya tsaya da ƙarfi har ƙarshe, zai sami ceto.
Kamu akan dibenci oleh semua orang karena Aku, tetapi siapapun yang bertahan sampai akhir akan diselamatkan.
14 “Sa’ad da kuka ga ‘abin ƙyama, mai kawo hallaka’tsaye indabai kamata ba (mai karatu ya gane), to, sai waɗanda suke a Yahudiya su gudu zuwa duwatsu.
Tetapi ketika kalian melihat ‘penyembahan berhala yang menajiskan’ berdiri di tempat yang tidak seharusnya (biar pembaca mengerti), maka mereka yang ada di Yudea harus lari ke gunung.
15 Kada wani da yake kan rufin gidansa yă sauka, ko yă shiga gida don yă ɗauki wani abu.
Dan untuk mereka yang sedang ada di atap rumah — janganlah turun untuk mengambil barang apapun juga yang ada di dalam rumah.
16 Kada wani da yake gona kuma yă koma don ɗaukar rigarsa.
Mereka yang bekerja di ladang — jangan pulang untuk mengambil jubahmu.
17 Kaiton mata masu ciki, da mata masu renon’ya’ya a waɗancan kwanakin!
Pada waktu bencana itu terjadi, benar-benar sulit bagi ibu-ibu yang sedang hamil atau menyusui pada saat itu, karena mereka akan sulit untuk melarikan diri!
18 Ku yi addu’a, kada wannan yă faru a lokacin sanyi.
Berdoalah supaya kesusahan besar itu tidak terjadi selama musim dingin.
19 Domin waɗancan kwanakin za su zama kwanaki na baƙin ciki, waɗanda ba a taɓa yin irinsa ba tun farkon halitta, har yă zuwa yanzu, ba kuwa za a sāke yin irinsa ba.
Karena ini akan menjadi hari-hari penuh kesulitan yang belum pernah terjadi sebelumnya sejak awal penciptaan Allah hingga sekarang, dan kesusahan yang seperti ini tidak akan pernah terjadi lagi.
20 “Da ba don Ubangiji ya rage kwanakin nan ba, da ba wani da zai tsira. Amma saboda zaɓaɓɓu waɗanda ya zaɓa, sai ya rage kwanakin.
Jika Allah tidak mempersingkat hari ini, tidak ada yang akan selamat. Namun demi mereka yang sudah Allah pilih, maka kesusahan itu tidak akan berlangsung lama.
21 A lokacin nan, in wani ya ce muku, ‘Duba, ga Kiristi nan!’ Ko kuwa, ‘Duba, ga shi can!’ Kada ku gaskata.
Jadi, jika ada yang memberitahu kalian, ‘Lihat, inilah Kristus,’ atau ‘lihat, Dia ada di sana,’ jangan kalian percaya.
22 Gama Kiristi masu yawa na ƙarya, da annabawan ƙarya za su firfito, su kuma aikata manyan alamu da ayyukan banmamaki don su ruɗi har da zaɓaɓɓu ma in zai yiwu.
Karena Kristus-Kristus palsu dan nabi-nabi palsu akan muncul, dan mereka akan melakukan tanda-tanda dan mujizat-mujizat untuk menipu orang-orang pilihan Allah, jika itu mungkin.
23 Amma ku kula! Na dai gaya muku kome tun da wuri.
Karena itu kalian harus hati-hati! Aku sudah memberitahukan segalanya kepada kalian sebelum hal-hal itu terjadi.
24 “Amma waɗancan kwanaki, bayan baƙin azaban nan, “‘rana za tă yi duhu, wata kuma ba zai ba da haskensa ba;
Inilah yang akan terjadi setelah masalah itu: ‘matahari akan menjadi gelap, bulan tidak akan bersinar lagi,
25 taurari za su fāffāɗo daga sararin sama. Za a kuma girgiza manyan abubuwan da suke a sararin sama.’
bintang-bintang akan jatuh dari langit, dan kekuatan surgawi akan terguncang.’
26 “Sa’an nan, mutane za su ga Ɗan Mutum yana zuwa cikin gizagizai da iko, da ɗaukaka mai girma.
Pada waktu itu semua orang akan melihat Anak Manusia datang di antara awan-awan, dengan kuasa dan kemuliaan yang besar dari surga.
27 Zai kuma aiko mala’ikunsa su tattaro zaɓaɓɓunsa daga kusurwoyi huɗun nan, daga iyakar duniya har yă zuwa iyakar sama.
Dia akan mengutus para malaikat, dan mengumpulkan semua orang pilihan-Nya dari mana pun mereka berada, dari bagian terjauh di bumi hingga titik terjauh di surga.
28 “To, sai ku yi koyi da itacen ɓaure. Da zarar rassansa suka yi taushi, ganyayensa kuma suka toho, kun san cewa damina ta yi kusa ke nan.
Ambil pelajaran dari pohon ara. Ketika ranting-rantingnya sudah menjadi lunak dan tunas-tunasnya mulai mengeluarkan daun, kalian tahu bahwa musim panas sudah dekat.
29 Haka ma, in kuka ga waɗannan abubuwa suna faruwa, ku san cewa ya yi kusan zuwa, yana ma dab da bakin ƙofa.
Ketika kalian melihat tanda-tanda itu mulai terjadi, kalian harus tahu bahwa waktu kedatangan-Ku kembali sudah dekat!
30 Gaskiya nake gaya muku, zamanin nan ba zai shuɗe ba sai duk abubuwan nan sun faru.
Saya katakan yang sebenarnya, generasi ini tidak akan berakhir sampai semua hal ini terjadi.
31 Sama da ƙasa za su shuɗe, amma kalmomina ba za su taɓa shuɗewa ba.
Langit dan bumi akan berakhir, tetapi perkataan-Ku tetap berlaku untuk selama-lamanya.
32 “Game da wannan rana ko sa’a kuwa, ba wanda ya sani, ko mala’ikun da suke sama, ko Ɗan, sai Uban kaɗai.
Tidak ada yang tahu hari atau jam kapan ini akan terjadi — para malaikat di surga pun tidak tahu, dan Anak pun tidak; hanya Bapa sendiri yang tahu.
33 Ku lura fa! Ku zauna a shirye! Don ba ku san lokacin da shi zai zo ba.
Jadi kalian harus berhati-hati, tetap berjaga-jaga dan berdoa! Karena kamu tidak tahu kapan ini akan terjadi.
34 Yana kama da mutumin da zai yi tafiya. Yakan bar gidansa a hannun bayinsa, kowa da nasa aikin da aka sa shi, yă kuma ce wa wanda yake gadin ƙofa, yă yi tsaro.
Ini seperti seorang pria yang pergi dalam perjalanan. Sebelum dia meninggalkan rumahnya, dia membagi tugas kepada setiap pelayannya dan menjelaskan tanggung jawab mereka masing-masing. Dia juga menyuruh penjaga pintu untuk menjaga baik-baik sampai dia kembali.
35 “Saboda haka, sai ku zauna a shirye, domin ba ku san lokacin da maigidan zai dawo ba, ko da yamma ne, ko da tsakar dare ne, ko lokacin da zakara na cara ne, ko kuma da safe ne.
Jadi tetap bersiap-siap dan berjaga-jaga, karena kamu tidak tahu kapan pemilik rumah akan kembali. Mungkin di sore hari, di tengah malam, sebelum matahari terbit, atau di pagi hari.
36 In ya zo kwaram, kada ka bari yă tarar da kai kana barci.
Jangan sampai waktu pemilik rumah datang, ternyata kalian sedang tidur.
37 Abin da na faɗa muku, na faɗa wa kowa. ‘Ku yi tsaro!’”
Apa yang saya katakan, saya memberitahu semua orang: Perhatikan!”

< Markus 13 >