< Markus 13 >
1 Da yake barin haikalin, sai ɗaya daga cikin almajiransa ya ce masa, “Malam! Dubi irin manya-manyan duwatsun nan! Ka ga irin gine-ginen nan masu kyau mana!”
Et comme il sortait du temple, un de ses disciples lui dit: Maître, regarde, quelles pierres et quels bâtiments!
2 Yesu ya amsa ya ce, “Ka ga dukan manyan gine-ginen nan? Ba wani dutse a nan, da za a bari kan wani da ba za a rushe ba.”
Et Jésus, répondant, lui dit: Tu vois ces grands bâtiments? il ne sera point laissé pierre sur pierre qui ne soit jetée à bas!
3 Da Yesu yana zaune a kan Dutsen Zaitun da yake ɗaura da haikali, sai Bitrus, Yaƙub, Yohanna da kuma Andarawus, suka tambaye shi a ɓoye, suka ce,
Et comme il était assis sur la montagne des Oliviers, vis-à-vis du temple, Pierre, et Jacques, et Jean, et André, l’interrogèrent en particulier:
4 “Ka gaya mana, yaushe waɗannan abubuwa za su faru? Wace alama ce kuma za tă nuna cewa, duk waɗannan suna dab da cikawa?”
Dis-nous quand ces choses auront lieu, et quel sera le signe quand toutes ces choses devront s’accomplir?
5 Sai Yesu ya ce musu, “Ku lura fa kada wani yă ruɗe ku.
Et Jésus, leur répondant, se mit à dire: Prenez garde que personne ne vous séduise;
6 Da yawa za su zo a cikin sunana, suna cewa, ‘Ni ne shi.’ Za su kuwa ruɗi mutane da yawa.
car plusieurs viendront en mon nom, disant: C’est moi! et ils en séduiront plusieurs.
7 Sa’ad da kuka ji labarun yaƙe-yaƙe da jita-jitar yaƙe-yaƙe, kada hankalinku yă tashi. Dole irin waɗannan abubuwa su faru. Amma ƙarshen tukuna.
Et quand vous entendrez parler de guerres et de bruits de guerres, ne soyez pas troublés, car il faut que [ces choses] arrivent; mais la fin n’est pas encore.
8 Al’umma za tă tasar wa al’umma, mulki kuma yă tasar wa mulki. Za a yi girgizar ƙasa a wurare dabam-dabam, a kuma yi yunwa. Waɗannan dai mafarin azabar naƙuda.
Car nation s’élèvera contre nation, et royaume contre royaume; et il y aura des tremblements de terre en divers lieux; et il y aura des famines et des troubles. Ces choses sont des commencements de douleurs.
9 “Dole ku yi zaman tsaro. Za a ba da ku ga hukuma, a kuma bulale ku a majami’u. Saboda ni kuma, za ku tsaya a gaban gwamnoni da sarakuna, domin ku ba da shaida a gabansu.
Mais vous, prenez garde à vous-mêmes; car ils vous livreront aux sanhédrins et aux synagogues; vous serez battus, et vous serez traduits devant les gouverneurs et les rois à cause de moi, pour leur servir de témoignage.
10 Dole sai an fara yin wa’azin bishara ga dukan al’ummai.
Et il faut que l’évangile soit auparavant prêché dans toutes les nations.
11 Sa’ad da aka kama ku, aka kuma kai ku don a yi muku shari’a, kada ku damu da abin da za ku faɗa. Sai dai ku faɗi abin da aka ba ku a lokacin. Gama ba ku kuke magana ba, Ruhu Mai Tsarki ne.
Et quand ils vous mèneront pour vous livrer, ne soyez pas à l’avance en souci de ce que vous direz, et ne méditez pas [votre discours]; mais tout ce qui vous sera donné en cette heure-là, dites-le; car ce n’est pas vous qui parlez, mais l’Esprit Saint.
12 “Ɗan’uwa zai ba da ɗan’uwa a kashe. Mahaifi zai ba da ɗansa.’Ya’ya za su tayar wa iyayensu, su kuma sa a kashe su.
Et le frère livrera son frère à la mort, et le père son enfant; et les enfants s’élèveront contre leurs parents et les feront mourir;
13 Dukan mutane za su ƙi ku saboda ni, amma wanda ya tsaya da ƙarfi har ƙarshe, zai sami ceto.
et vous serez haïs de tous à cause de mon nom; et celui qui persévérera jusqu’à la fin, celui-là sera sauvé.
14 “Sa’ad da kuka ga ‘abin ƙyama, mai kawo hallaka’tsaye indabai kamata ba (mai karatu ya gane), to, sai waɗanda suke a Yahudiya su gudu zuwa duwatsu.
Et quand vous verrez l’abomination de la désolation établie où elle ne doit pas être (que celui qui lit comprenne), alors que ceux qui sont en Judée s’enfuient dans les montagnes;
15 Kada wani da yake kan rufin gidansa yă sauka, ko yă shiga gida don yă ɗauki wani abu.
et que celui qui est sur le toit ne descende pas dans la maison, et n’y entre pas pour emporter quoi que ce soit hors de sa maison;
16 Kada wani da yake gona kuma yă koma don ɗaukar rigarsa.
et que celui qui est aux champs ne retourne pas en arrière pour emporter son vêtement.
17 Kaiton mata masu ciki, da mata masu renon’ya’ya a waɗancan kwanakin!
Mais malheur à celles qui sont enceintes et à celles qui allaitent en ces jours-là!
18 Ku yi addu’a, kada wannan yă faru a lokacin sanyi.
Et priez que [cela] n’ait pas lieu en hiver;
19 Domin waɗancan kwanakin za su zama kwanaki na baƙin ciki, waɗanda ba a taɓa yin irinsa ba tun farkon halitta, har yă zuwa yanzu, ba kuwa za a sāke yin irinsa ba.
car ces jours-là seront une tribulation telle qu’il n’y en a point eu de semblable depuis le commencement de la création que Dieu a créée, jusqu’à maintenant, et qu’il n’y en aura jamais.
20 “Da ba don Ubangiji ya rage kwanakin nan ba, da ba wani da zai tsira. Amma saboda zaɓaɓɓu waɗanda ya zaɓa, sai ya rage kwanakin.
Et si le Seigneur n’avait abrégé ces jours, nulle chair n’aurait été sauvée; mais à cause des élus qu’il a élus, il a abrégé les jours.
21 A lokacin nan, in wani ya ce muku, ‘Duba, ga Kiristi nan!’ Ko kuwa, ‘Duba, ga shi can!’ Kada ku gaskata.
Et alors, si quelqu’un vous dit: Voici, le Christ est ici, ou: Voici, il est là, ne le croyez pas.
22 Gama Kiristi masu yawa na ƙarya, da annabawan ƙarya za su firfito, su kuma aikata manyan alamu da ayyukan banmamaki don su ruɗi har da zaɓaɓɓu ma in zai yiwu.
Car il s’élèvera de faux christs et de faux prophètes; et ils montreront des signes et des prodiges, pour séduire, si possible, même les élus.
23 Amma ku kula! Na dai gaya muku kome tun da wuri.
Mais vous, soyez sur vos gardes! voici, je vous ai tout dit à l’avance.
24 “Amma waɗancan kwanaki, bayan baƙin azaban nan, “‘rana za tă yi duhu, wata kuma ba zai ba da haskensa ba;
Mais en ces jours-là, après cette tribulation, le soleil sera obscurci, et la lune ne donnera pas sa lumière,
25 taurari za su fāffāɗo daga sararin sama. Za a kuma girgiza manyan abubuwan da suke a sararin sama.’
et les étoiles du ciel tomberont, et les puissances qui sont dans les cieux seront ébranlées.
26 “Sa’an nan, mutane za su ga Ɗan Mutum yana zuwa cikin gizagizai da iko, da ɗaukaka mai girma.
Et alors ils verront le fils de l’homme venant sur les nuées avec une grande puissance et avec gloire:
27 Zai kuma aiko mala’ikunsa su tattaro zaɓaɓɓunsa daga kusurwoyi huɗun nan, daga iyakar duniya har yă zuwa iyakar sama.
et alors il enverra ses anges, et il rassemblera ses élus des quatre vents, depuis le bout de la terre jusqu’au bout du ciel.
28 “To, sai ku yi koyi da itacen ɓaure. Da zarar rassansa suka yi taushi, ganyayensa kuma suka toho, kun san cewa damina ta yi kusa ke nan.
Mais apprenez du figuier la parabole [qu’il vous offre]: Quand déjà son rameau est tendre et qu’il pousse des feuilles, vous connaissez que l’été est proche.
29 Haka ma, in kuka ga waɗannan abubuwa suna faruwa, ku san cewa ya yi kusan zuwa, yana ma dab da bakin ƙofa.
De même aussi vous, quand vous verrez arriver ces choses, sachez que cela est proche, à la porte.
30 Gaskiya nake gaya muku, zamanin nan ba zai shuɗe ba sai duk abubuwan nan sun faru.
En vérité, je vous dis que cette génération ne passera point que toutes ces choses ne soient arrivées.
31 Sama da ƙasa za su shuɗe, amma kalmomina ba za su taɓa shuɗewa ba.
Le ciel et la terre passeront, mais mes paroles ne passeront point.
32 “Game da wannan rana ko sa’a kuwa, ba wanda ya sani, ko mala’ikun da suke sama, ko Ɗan, sai Uban kaɗai.
Mais quant à ce jour-là, ou à l’heure, personne n’en a connaissance, pas même les anges qui sont dans le ciel, ni même le Fils, mais le Père.
33 Ku lura fa! Ku zauna a shirye! Don ba ku san lokacin da shi zai zo ba.
Prenez garde, veillez et priez, car vous ne savez pas quand ce temps sera.
34 Yana kama da mutumin da zai yi tafiya. Yakan bar gidansa a hannun bayinsa, kowa da nasa aikin da aka sa shi, yă kuma ce wa wanda yake gadin ƙofa, yă yi tsaro.
– C’est comme un homme allant hors du pays, laissant sa maison, et donnant de l’autorité à ses esclaves, et à chacun son ouvrage…; et il commanda au portier de veiller.
35 “Saboda haka, sai ku zauna a shirye, domin ba ku san lokacin da maigidan zai dawo ba, ko da yamma ne, ko da tsakar dare ne, ko lokacin da zakara na cara ne, ko kuma da safe ne.
Veillez donc; car vous ne savez pas quand le maître de la maison viendra, le soir, ou à minuit, ou au chant du coq, ou au matin;
36 In ya zo kwaram, kada ka bari yă tarar da kai kana barci.
de peur qu’arrivant tout à coup, il ne vous trouve dormant.
37 Abin da na faɗa muku, na faɗa wa kowa. ‘Ku yi tsaro!’”
Or ce que je vous dis, à vous, je le dis à tous: Veillez.