< Markus 13 >

1 Da yake barin haikalin, sai ɗaya daga cikin almajiransa ya ce masa, “Malam! Dubi irin manya-manyan duwatsun nan! Ka ga irin gine-ginen nan masu kyau mana!”
And as he is going forth out of the temple, one of his disciples saith to him, 'Teacher, see! what stones! and what buildings!'
2 Yesu ya amsa ya ce, “Ka ga dukan manyan gine-ginen nan? Ba wani dutse a nan, da za a bari kan wani da ba za a rushe ba.”
and Jesus answering said to him, 'Seest thou these great buildings? there may not be left a stone upon a stone, that may not be thrown down.'
3 Da Yesu yana zaune a kan Dutsen Zaitun da yake ɗaura da haikali, sai Bitrus, Yaƙub, Yohanna da kuma Andarawus, suka tambaye shi a ɓoye, suka ce,
And as he is sitting at the mount of the Olives, over-against the temple, Peter, and James, and John, and Andrew, were questioning him by himself,
4 “Ka gaya mana, yaushe waɗannan abubuwa za su faru? Wace alama ce kuma za tă nuna cewa, duk waɗannan suna dab da cikawa?”
'Tell us when these things shall be? and what [is] the sign when all these may be about to be fulfilled?'
5 Sai Yesu ya ce musu, “Ku lura fa kada wani yă ruɗe ku.
And Jesus answering them, began to say, 'Take heed lest any one may lead you astray,
6 Da yawa za su zo a cikin sunana, suna cewa, ‘Ni ne shi.’ Za su kuwa ruɗi mutane da yawa.
for many shall come in my name, saying — I am [he], and many they shall lead astray;
7 Sa’ad da kuka ji labarun yaƙe-yaƙe da jita-jitar yaƙe-yaƙe, kada hankalinku yă tashi. Dole irin waɗannan abubuwa su faru. Amma ƙarshen tukuna.
and when ye may hear of wars and reports of wars, be not troubled, for these behove to be, but the end [is] not yet;
8 Al’umma za tă tasar wa al’umma, mulki kuma yă tasar wa mulki. Za a yi girgizar ƙasa a wurare dabam-dabam, a kuma yi yunwa. Waɗannan dai mafarin azabar naƙuda.
for nation shall rise against nation, and kingdom against kingdom, and there shall be earthquakes in divers places, and there shall be famines and troubles; beginnings of sorrows [are] these.
9 “Dole ku yi zaman tsaro. Za a ba da ku ga hukuma, a kuma bulale ku a majami’u. Saboda ni kuma, za ku tsaya a gaban gwamnoni da sarakuna, domin ku ba da shaida a gabansu.
'And take ye heed to yourselves, for they shall deliver you up to sanhedrims, and to synagogues, ye shall be beaten, and before governors and kings ye shall be set for my sake, for a testimony to them;
10 Dole sai an fara yin wa’azin bishara ga dukan al’ummai.
and to all the nations it behoveth first that the good news be proclaimed.
11 Sa’ad da aka kama ku, aka kuma kai ku don a yi muku shari’a, kada ku damu da abin da za ku faɗa. Sai dai ku faɗi abin da aka ba ku a lokacin. Gama ba ku kuke magana ba, Ruhu Mai Tsarki ne.
'And when they may lead you, delivering up, be not anxious beforehand what ye may speak, nor premeditate, but whatever may be given to you in that hour, that speak ye, for it is not ye who are speaking, but the Holy Spirit.
12 “Ɗan’uwa zai ba da ɗan’uwa a kashe. Mahaifi zai ba da ɗansa.’Ya’ya za su tayar wa iyayensu, su kuma sa a kashe su.
'And brother shall deliver up brother to death, and father child, and children shall rise up against parents, and shall put them to death,
13 Dukan mutane za su ƙi ku saboda ni, amma wanda ya tsaya da ƙarfi har ƙarshe, zai sami ceto.
and ye shall be hated by all because of my name, but he who hath endured to the end — he shall be saved.
14 “Sa’ad da kuka ga ‘abin ƙyama, mai kawo hallaka’tsaye indabai kamata ba (mai karatu ya gane), to, sai waɗanda suke a Yahudiya su gudu zuwa duwatsu.
'And when ye may see the abomination of the desolation, that was spoken of by Daniel the prophet, standing where it ought not, (whoever is reading let him understand), then those in Judea, let them flee to the mountains;
15 Kada wani da yake kan rufin gidansa yă sauka, ko yă shiga gida don yă ɗauki wani abu.
and he upon the house-top, let him not come down to the house, nor come in to take anything out of his house;
16 Kada wani da yake gona kuma yă koma don ɗaukar rigarsa.
and he who is in the field, let him not turn to the things behind, to take up his garment.
17 Kaiton mata masu ciki, da mata masu renon’ya’ya a waɗancan kwanakin!
'And woe to those with child, and to those giving suck, in those days;
18 Ku yi addu’a, kada wannan yă faru a lokacin sanyi.
and pray ye that your flight may not be in winter,
19 Domin waɗancan kwanakin za su zama kwanaki na baƙin ciki, waɗanda ba a taɓa yin irinsa ba tun farkon halitta, har yă zuwa yanzu, ba kuwa za a sāke yin irinsa ba.
for those days shall be tribulation, such as hath not been from the beginning of the creation that God created, till now, and may not be;
20 “Da ba don Ubangiji ya rage kwanakin nan ba, da ba wani da zai tsira. Amma saboda zaɓaɓɓu waɗanda ya zaɓa, sai ya rage kwanakin.
and if the Lord did not shorten the days, no flesh had been saved; but because of the chosen, whom He did choose to Himself, He did shorten the days.
21 A lokacin nan, in wani ya ce muku, ‘Duba, ga Kiristi nan!’ Ko kuwa, ‘Duba, ga shi can!’ Kada ku gaskata.
'And then, if any may say to you, Lo, here [is] the Christ, or, Lo, there, ye may not believe;
22 Gama Kiristi masu yawa na ƙarya, da annabawan ƙarya za su firfito, su kuma aikata manyan alamu da ayyukan banmamaki don su ruɗi har da zaɓaɓɓu ma in zai yiwu.
for there shall rise false Christs and false prophets, and they shall give signs and wonders, to seduce, if possible, also the chosen;
23 Amma ku kula! Na dai gaya muku kome tun da wuri.
and ye, take heed; lo, I have foretold you all things.
24 “Amma waɗancan kwanaki, bayan baƙin azaban nan, “‘rana za tă yi duhu, wata kuma ba zai ba da haskensa ba;
'But in those days, after that tribulation, the sun shall be darkened, and the moon shall not give her light,
25 taurari za su fāffāɗo daga sararin sama. Za a kuma girgiza manyan abubuwan da suke a sararin sama.’
and the stars of the heaven shall be falling, and the powers that are in the heavens shall be shaken.
26 “Sa’an nan, mutane za su ga Ɗan Mutum yana zuwa cikin gizagizai da iko, da ɗaukaka mai girma.
'And then they shall see the Son of Man coming in clouds with much power and glory,
27 Zai kuma aiko mala’ikunsa su tattaro zaɓaɓɓunsa daga kusurwoyi huɗun nan, daga iyakar duniya har yă zuwa iyakar sama.
and then he shall send his messengers, and gather together his chosen from the four winds, from the end of the earth unto the end of heaven.
28 “To, sai ku yi koyi da itacen ɓaure. Da zarar rassansa suka yi taushi, ganyayensa kuma suka toho, kun san cewa damina ta yi kusa ke nan.
'And from the fig-tree learn ye the simile: when the branch may already become tender, and may put forth the leaves, ye know that nigh is the summer;
29 Haka ma, in kuka ga waɗannan abubuwa suna faruwa, ku san cewa ya yi kusan zuwa, yana ma dab da bakin ƙofa.
so ye, also, when these ye may see coming to pass, ye know that it is nigh, at the doors.
30 Gaskiya nake gaya muku, zamanin nan ba zai shuɗe ba sai duk abubuwan nan sun faru.
Verily I say to you, that this generation may not pass away till all these things may come to pass;
31 Sama da ƙasa za su shuɗe, amma kalmomina ba za su taɓa shuɗewa ba.
the heaven and the earth shall pass away, but my words shall not pass away.
32 “Game da wannan rana ko sa’a kuwa, ba wanda ya sani, ko mala’ikun da suke sama, ko Ɗan, sai Uban kaɗai.
'And concerning that day and the hour no one hath known — not even the messengers who are in the heaven, not even the Son — except the Father.
33 Ku lura fa! Ku zauna a shirye! Don ba ku san lokacin da shi zai zo ba.
Take heed, watch and pray, for ye have not known when the time is;
34 Yana kama da mutumin da zai yi tafiya. Yakan bar gidansa a hannun bayinsa, kowa da nasa aikin da aka sa shi, yă kuma ce wa wanda yake gadin ƙofa, yă yi tsaro.
as a man who is gone abroad, having left his house, and given to his servants the authority, and to each one his work, did command also the porter that he may watch;
35 “Saboda haka, sai ku zauna a shirye, domin ba ku san lokacin da maigidan zai dawo ba, ko da yamma ne, ko da tsakar dare ne, ko lokacin da zakara na cara ne, ko kuma da safe ne.
watch ye, therefore, for ye have not known when the lord of the house doth come, at even, or at midnight, or at cock-crowing, or at the morning;
36 In ya zo kwaram, kada ka bari yă tarar da kai kana barci.
lest, having come suddenly, he may find you sleeping;
37 Abin da na faɗa muku, na faɗa wa kowa. ‘Ku yi tsaro!’”
and what I say to you, I say to all, Watch.'

< Markus 13 >