< Markus 13 >
1 Da yake barin haikalin, sai ɗaya daga cikin almajiransa ya ce masa, “Malam! Dubi irin manya-manyan duwatsun nan! Ka ga irin gine-ginen nan masu kyau mana!”
And as he went out of the teple one of his disciples sayde vnto him: Master se what stones and what byldynges are here.
2 Yesu ya amsa ya ce, “Ka ga dukan manyan gine-ginen nan? Ba wani dutse a nan, da za a bari kan wani da ba za a rushe ba.”
And Iesus answered and sayde vnto him: Seist thou these greate byldinges? There shall not be leefte one stone vpon a another that shall not be throwen doune.
3 Da Yesu yana zaune a kan Dutsen Zaitun da yake ɗaura da haikali, sai Bitrus, Yaƙub, Yohanna da kuma Andarawus, suka tambaye shi a ɓoye, suka ce,
And as he sate on moute olivete over agest the teple Peter and Iames and Iohn and Andrew axed him secretly:
4 “Ka gaya mana, yaushe waɗannan abubuwa za su faru? Wace alama ce kuma za tă nuna cewa, duk waɗannan suna dab da cikawa?”
tell vs when shall these thinges be? And what is ye signe whe all these thinges shalbe fulfilled?
5 Sai Yesu ya ce musu, “Ku lura fa kada wani yă ruɗe ku.
And Iesus answered the and bega to saye: take hede lest eny man deceave you.
6 Da yawa za su zo a cikin sunana, suna cewa, ‘Ni ne shi.’ Za su kuwa ruɗi mutane da yawa.
For many shall come in my name sayinge: I am Christ and shall deceave many.
7 Sa’ad da kuka ji labarun yaƙe-yaƙe da jita-jitar yaƙe-yaƙe, kada hankalinku yă tashi. Dole irin waɗannan abubuwa su faru. Amma ƙarshen tukuna.
When ye shall heare of warre and tydinges of warre be ye not troubled. For soche thinges muste nedes be. But the ende is not yet.
8 Al’umma za tă tasar wa al’umma, mulki kuma yă tasar wa mulki. Za a yi girgizar ƙasa a wurare dabam-dabam, a kuma yi yunwa. Waɗannan dai mafarin azabar naƙuda.
For ther shall nacion aryse agaynste nacion and kyngdome agaynst kyngdome. And ther shalbe erth quakes in all quarters and famyshment and troubles. These are the begynnynge of sorowes.
9 “Dole ku yi zaman tsaro. Za a ba da ku ga hukuma, a kuma bulale ku a majami’u. Saboda ni kuma, za ku tsaya a gaban gwamnoni da sarakuna, domin ku ba da shaida a gabansu.
But take ye hede to youre selves. For they shall bringe you vp to ye counsels and into ye synagoges and ye shalbe beaten: ye and shalbe brought before rulers and kynges for my sake for a testimoniall vnto them.
10 Dole sai an fara yin wa’azin bishara ga dukan al’ummai.
And the gospell must fyrste be publysshed amoge all nacions.
11 Sa’ad da aka kama ku, aka kuma kai ku don a yi muku shari’a, kada ku damu da abin da za ku faɗa. Sai dai ku faɗi abin da aka ba ku a lokacin. Gama ba ku kuke magana ba, Ruhu Mai Tsarki ne.
But when they leade you and present you toke noo thought afore honde what ye shall saye nether ymagion: but whatsoever is geve you at the same tyme that speake. For it shall not be ye that shall speake but ye holy goost.
12 “Ɗan’uwa zai ba da ɗan’uwa a kashe. Mahaifi zai ba da ɗansa.’Ya’ya za su tayar wa iyayensu, su kuma sa a kashe su.
Ye and the brother shall delyvre the brother to deeth and the father the sonne and the chyldre shall ryse agaynste their fathers and mothers and shall put them to deeth.
13 Dukan mutane za su ƙi ku saboda ni, amma wanda ya tsaya da ƙarfi har ƙarshe, zai sami ceto.
And ye shalbe hated of all men for my names sake. But whosoever shall endure vnto the ende the same shalbe safe.
14 “Sa’ad da kuka ga ‘abin ƙyama, mai kawo hallaka’tsaye indabai kamata ba (mai karatu ya gane), to, sai waɗanda suke a Yahudiya su gudu zuwa duwatsu.
Moreover whe ye se the abhominacio that betokeneth desolacion wherof is spoken by Daniel the Prophet stonde where it ought not let him that redeth vnderstonde. Then let them that be in Iurie fle to the mountaynes.
15 Kada wani da yake kan rufin gidansa yă sauka, ko yă shiga gida don yă ɗauki wani abu.
And let him that is on the housse toppe not descende doune into the housse nether entre therin to fetche eny thinge oute of his housse.
16 Kada wani da yake gona kuma yă koma don ɗaukar rigarsa.
And let hym that is in the felde not tourne backe agayne vnto the thinges which he leeft behynde him for to take his cloothes with him.
17 Kaiton mata masu ciki, da mata masu renon’ya’ya a waɗancan kwanakin!
Woo is then to them that are wt chylde and to them that geve soucke in thoose dayes.
18 Ku yi addu’a, kada wannan yă faru a lokacin sanyi.
But praye that youre flyght be not in the wynter.
19 Domin waɗancan kwanakin za su zama kwanaki na baƙin ciki, waɗanda ba a taɓa yin irinsa ba tun farkon halitta, har yă zuwa yanzu, ba kuwa za a sāke yin irinsa ba.
For ther shalbe in those dayes suche tribulacion as was not from the begynninge of creatures which God created vnto this tyme nether shalbe.
20 “Da ba don Ubangiji ya rage kwanakin nan ba, da ba wani da zai tsira. Amma saboda zaɓaɓɓu waɗanda ya zaɓa, sai ya rage kwanakin.
And excepte yt the Lorde shuld shorten those dayes no ma shuld be saved. But for the electes sake which he hath chosen he hath shortened those dayes.
21 A lokacin nan, in wani ya ce muku, ‘Duba, ga Kiristi nan!’ Ko kuwa, ‘Duba, ga shi can!’ Kada ku gaskata.
And then yf eny man saye to you: loo here is Christ: loo he is there beleve not.
22 Gama Kiristi masu yawa na ƙarya, da annabawan ƙarya za su firfito, su kuma aikata manyan alamu da ayyukan banmamaki don su ruɗi har da zaɓaɓɓu ma in zai yiwu.
For falce Christes shall aryse and falce Prophetes and shall shewe myracles and wondres to deceave yf it were possible evyn the electe.
23 Amma ku kula! Na dai gaya muku kome tun da wuri.
But take ye hede: beholde I have shewed you all thinges before.
24 “Amma waɗancan kwanaki, bayan baƙin azaban nan, “‘rana za tă yi duhu, wata kuma ba zai ba da haskensa ba;
Moreover in thoose dayes after that tribulacio the sunne shall wexe darke and the mone shall not geve her light
25 taurari za su fāffāɗo daga sararin sama. Za a kuma girgiza manyan abubuwan da suke a sararin sama.’
and the starres of heven shall fall: and the powers wich are in heven shall move.
26 “Sa’an nan, mutane za su ga Ɗan Mutum yana zuwa cikin gizagizai da iko, da ɗaukaka mai girma.
And then shall they se the sonne of man comynge in the cloudes with greate power and glory.
27 Zai kuma aiko mala’ikunsa su tattaro zaɓaɓɓunsa daga kusurwoyi huɗun nan, daga iyakar duniya har yă zuwa iyakar sama.
And then shall he sende his angels and shall gaddre to gedder his electe from the fower wyndes and from the one ende of the worlde to the other.
28 “To, sai ku yi koyi da itacen ɓaure. Da zarar rassansa suka yi taushi, ganyayensa kuma suka toho, kun san cewa damina ta yi kusa ke nan.
Learne a similitude of ye fygge tree. When his braunches are yet tender and hath brought forthe leves ye knowe that sommer is neare.
29 Haka ma, in kuka ga waɗannan abubuwa suna faruwa, ku san cewa ya yi kusan zuwa, yana ma dab da bakin ƙofa.
So in lyke maner when ye se these thinges come to passe: vnderstond that it ys nye even at the dores.
30 Gaskiya nake gaya muku, zamanin nan ba zai shuɗe ba sai duk abubuwan nan sun faru.
Verely I saye vnto you yt this generacion shall not passe tyll all these thinges be done.
31 Sama da ƙasa za su shuɗe, amma kalmomina ba za su taɓa shuɗewa ba.
Heven and erth shall passe but my wordes shall not passe.
32 “Game da wannan rana ko sa’a kuwa, ba wanda ya sani, ko mala’ikun da suke sama, ko Ɗan, sai Uban kaɗai.
But of the daye and the houre knoweth no ma: no not the angels which are in heven: nether the sonne him silfe save the father only.
33 Ku lura fa! Ku zauna a shirye! Don ba ku san lokacin da shi zai zo ba.
Take hede watche and praye for ye knowe not when the tyme ys.
34 Yana kama da mutumin da zai yi tafiya. Yakan bar gidansa a hannun bayinsa, kowa da nasa aikin da aka sa shi, yă kuma ce wa wanda yake gadin ƙofa, yă yi tsaro.
As a man which is gone in to a straunge countrey and hath lefte hys housse and geven auctorite to his servautes and to every man hys worke and commaunded the porter to watche.
35 “Saboda haka, sai ku zauna a shirye, domin ba ku san lokacin da maigidan zai dawo ba, ko da yamma ne, ko da tsakar dare ne, ko lokacin da zakara na cara ne, ko kuma da safe ne.
Watche therfore for ye knowe not when the master of ye housse will come whether at eve or at mydnyght whether at the cocke crowynge or in the daunynge:
36 In ya zo kwaram, kada ka bari yă tarar da kai kana barci.
lest yf he come sodenly he shuld fynde you slepynge.
37 Abin da na faɗa muku, na faɗa wa kowa. ‘Ku yi tsaro!’”
And that I saye vnto you I saye vnto all men watche.