< Markus 13 >
1 Da yake barin haikalin, sai ɗaya daga cikin almajiransa ya ce masa, “Malam! Dubi irin manya-manyan duwatsun nan! Ka ga irin gine-ginen nan masu kyau mana!”
As he was going out of the temple, one of his disciples said to him, Rabbi, look what prodigious stones and stately buildings are here!
2 Yesu ya amsa ya ce, “Ka ga dukan manyan gine-ginen nan? Ba wani dutse a nan, da za a bari kan wani da ba za a rushe ba.”
Jesus answering, said to him, You see these great buildings. They shall be so razed, that one stone will not be left upon another.
3 Da Yesu yana zaune a kan Dutsen Zaitun da yake ɗaura da haikali, sai Bitrus, Yaƙub, Yohanna da kuma Andarawus, suka tambaye shi a ɓoye, suka ce,
Afterward, as he was sitting on the Mount of Olives, opposite the temple, Peter, and James, and John, and Andrew, asked him privately,
4 “Ka gaya mana, yaushe waɗannan abubuwa za su faru? Wace alama ce kuma za tă nuna cewa, duk waɗannan suna dab da cikawa?”
Tell us, when will this happen? and what will be the sign, when all this is to be accomplished?
5 Sai Yesu ya ce musu, “Ku lura fa kada wani yă ruɗe ku.
Jesus answering them, took occasion to say, Take heed that no man seduce you;
6 Da yawa za su zo a cikin sunana, suna cewa, ‘Ni ne shi.’ Za su kuwa ruɗi mutane da yawa.
for many will assume my character, saying, I am the person, and will seduce many.
7 Sa’ad da kuka ji labarun yaƙe-yaƙe da jita-jitar yaƙe-yaƙe, kada hankalinku yă tashi. Dole irin waɗannan abubuwa su faru. Amma ƙarshen tukuna.
But when you hear of wars and rumors of wars, be not alarmed; for this must happen, but the end is not yet.
8 Al’umma za tă tasar wa al’umma, mulki kuma yă tasar wa mulki. Za a yi girgizar ƙasa a wurare dabam-dabam, a kuma yi yunwa. Waɗannan dai mafarin azabar naƙuda.
For nation will rise against nation, and kingdom against kingdom; and there will be earthquakes in sundry places, and there will be famines and commotions. These are the prelude of woes.
9 “Dole ku yi zaman tsaro. Za a ba da ku ga hukuma, a kuma bulale ku a majami’u. Saboda ni kuma, za ku tsaya a gaban gwamnoni da sarakuna, domin ku ba da shaida a gabansu.
But take heed to yourselves; for they will deliver you to councils; and you will be beaten in the synagogues, and brought before governors and kings for my sake, to bear testimony to them.
10 Dole sai an fara yin wa’azin bishara ga dukan al’ummai.
The good tidings, however, must first be published among all nations.
11 Sa’ad da aka kama ku, aka kuma kai ku don a yi muku shari’a, kada ku damu da abin da za ku faɗa. Sai dai ku faɗi abin da aka ba ku a lokacin. Gama ba ku kuke magana ba, Ruhu Mai Tsarki ne.
But when they conduct you, to deliver you up, have no anxiety beforehand, nor premeditate what you shall speak: but whatever shall be suggested to you in that moment, speak; for it is not you that shall speak, but the Holy Spirit.
12 “Ɗan’uwa zai ba da ɗan’uwa a kashe. Mahaifi zai ba da ɗansa.’Ya’ya za su tayar wa iyayensu, su kuma sa a kashe su.
Then the brother will deliver up the brother to death; and the father the child; and children will arise against their parents, and procure their death.
13 Dukan mutane za su ƙi ku saboda ni, amma wanda ya tsaya da ƙarfi har ƙarshe, zai sami ceto.
And on my account you shall be universally hated; but the man who perseveres to the end, shall be saved.
14 “Sa’ad da kuka ga ‘abin ƙyama, mai kawo hallaka’tsaye indabai kamata ba (mai karatu ya gane), to, sai waɗanda suke a Yahudiya su gudu zuwa duwatsu.
But when you shall see standing on forbidden ground, the desolating abomination, (reader, attend!) then let those in Judea flee to the mountains;
15 Kada wani da yake kan rufin gidansa yă sauka, ko yă shiga gida don yă ɗauki wani abu.
and let not him who shall be on the roof, go down into the house, nor enter it, to carry anything out of his house:
16 Kada wani da yake gona kuma yă koma don ɗaukar rigarsa.
and let not him who shall be in the field, turn back to fetch his mantle.
17 Kaiton mata masu ciki, da mata masu renon’ya’ya a waɗancan kwanakin!
But alas for the women with child, and for them who give suck in those days!
18 Ku yi addu’a, kada wannan yă faru a lokacin sanyi.
Pray, then, that your flight happen not in the winter;
19 Domin waɗancan kwanakin za su zama kwanaki na baƙin ciki, waɗanda ba a taɓa yin irinsa ba tun farkon halitta, har yă zuwa yanzu, ba kuwa za a sāke yin irinsa ba.
because there shall be such affliction in those days, as has not been before, from the beginning of the world, which God created, nor shall be ever after.
20 “Da ba don Ubangiji ya rage kwanakin nan ba, da ba wani da zai tsira. Amma saboda zaɓaɓɓu waɗanda ya zaɓa, sai ya rage kwanakin.
Had the Lord assigned it a long duration, no soul could escape; but for the sake of the people whom he had elected, he has made its duration the shorter.
21 A lokacin nan, in wani ya ce muku, ‘Duba, ga Kiristi nan!’ Ko kuwa, ‘Duba, ga shi can!’ Kada ku gaskata.
Then if any one shall say to you, Lo! the Messiah is here, or Lo! he is yonder, believe it not.
22 Gama Kiristi masu yawa na ƙarya, da annabawan ƙarya za su firfito, su kuma aikata manyan alamu da ayyukan banmamaki don su ruɗi har da zaɓaɓɓu ma in zai yiwu.
For false Messiahs and false prophets will arise, who will perform wonders and prodigies, in order to impose, if possible, even on the elect.
23 Amma ku kula! Na dai gaya muku kome tun da wuri.
Be you, therefore, upon your guard: remember, I have warned you of everything.
24 “Amma waɗancan kwanaki, bayan baƙin azaban nan, “‘rana za tă yi duhu, wata kuma ba zai ba da haskensa ba;
But in those days, after that affliction, the sun shall be darkened, and the moon shall withhold her light,
25 taurari za su fāffāɗo daga sararin sama. Za a kuma girgiza manyan abubuwan da suke a sararin sama.’
and the stars of heaven shall fall; and the powers which are in heaven shall be shaken.
26 “Sa’an nan, mutane za su ga Ɗan Mutum yana zuwa cikin gizagizai da iko, da ɗaukaka mai girma.
Then they shall see the Son of Man coming in the clouds with great power and glory.
27 Zai kuma aiko mala’ikunsa su tattaro zaɓaɓɓunsa daga kusurwoyi huɗun nan, daga iyakar duniya har yă zuwa iyakar sama.
Then he will send his messengers, and assemble his elect from the four quarters of the world, from the extremities of heaven and earth.
28 “To, sai ku yi koyi da itacen ɓaure. Da zarar rassansa suka yi taushi, ganyayensa kuma suka toho, kun san cewa damina ta yi kusa ke nan.
Learn now a similitude from the fig tree. When its branches become tender, and put forth leaves, you know that the summer is nigh.
29 Haka ma, in kuka ga waɗannan abubuwa suna faruwa, ku san cewa ya yi kusan zuwa, yana ma dab da bakin ƙofa.
In like manner, when you shall see these things happen, know that he is near, even at the door.
30 Gaskiya nake gaya muku, zamanin nan ba zai shuɗe ba sai duk abubuwan nan sun faru.
Indeed, I say to you, that this generation shall not pass, till all these things be accomplished.
31 Sama da ƙasa za su shuɗe, amma kalmomina ba za su taɓa shuɗewa ba.
For heaven and earth shall fail: but my words shall not fail.
32 “Game da wannan rana ko sa’a kuwa, ba wanda ya sani, ko mala’ikun da suke sama, ko Ɗan, sai Uban kaɗai.
But of that day, or of that hour, knows none, (not the angels; no, not the Son, ) but the Father.
33 Ku lura fa! Ku zauna a shirye! Don ba ku san lokacin da shi zai zo ba.
Be circumspect, be vigilant, and pray; for you know not when that time will be.
34 Yana kama da mutumin da zai yi tafiya. Yakan bar gidansa a hannun bayinsa, kowa da nasa aikin da aka sa shi, yă kuma ce wa wanda yake gadin ƙofa, yă yi tsaro.
When a man intends to travel, he leaves his household in charge to his servants, assigns to every one his task, and orders the porter to watch.
35 “Saboda haka, sai ku zauna a shirye, domin ba ku san lokacin da maigidan zai dawo ba, ko da yamma ne, ko da tsakar dare ne, ko lokacin da zakara na cara ne, ko kuma da safe ne.
Watch you, therefore; for you know not when the master of the house will return, (whether in the evening, or at midnight, or at cock-crowing, or in the morning; )
36 In ya zo kwaram, kada ka bari yă tarar da kai kana barci.
lest coming suddenly, he find you asleep.
37 Abin da na faɗa muku, na faɗa wa kowa. ‘Ku yi tsaro!’”
Now what I say to you, I say to all, Watch.