< Markus 12 >

1 Sa’an nan ya fara yi musu magana da misalai ya ce, “Wani mutum ya shuka gonar inabi. Ya kewaye ta da katanga, ya haƙa rami domin matsin inabin, ya kuma gina ɗakin gadi. Sai ya ba wa waɗansu manoma hayar gonar inabin, sa’an nan ya yi tafiya.
И поче им говорити у причама: Посади човек виноград, и огради плотом, и ископа пивницу, и начини кулу, и даде га виноградарима, па оде.
2 Da lokacin girbi ya yi, sai ya aiki wani bawa wajen’yan hayan, don yă karɓo masa’ya’yan inabin daga wurinsu.
И кад дође време, посла к виноградарима слугу да прими од виноградара од рода виноградског.
3 Amma suka kama shi, suka yi masa dūka, suka kore shi hannun wofi.
А они ухвативши слугу избише га, и послаше празна.
4 Sai ya sāke aikan wani bawa wurinsu, amma suka bugi wannan mutum a kai, suka wulaƙanta shi.
И опет посла к њима другог слугу; и оног бише камењем и разбише му главу, и послаше га срамотног.
5 Har yanzu ya sāke aikan wani. Wannan kuwa suka kashe. Ya aika waɗansu da yawa; suka bubbuge waɗansu, sauran kuwa suka kashe.
И опет посла другог; и оног убише; и многе друге, једне избише, а друге побише.
6 “Sauran mutum ɗaya da ya rage ya aika, ɗa, da yake ƙauna. Daga ƙarshe sai ya aike shi, yana cewa, ‘Za su girmama ɗana.’
Још дакле имаше јединог свог милог сина, посла и њега најпосле к њима говорећи: Постидеће се сина мог.
7 “Amma’yan hayan suka ce wa juna, ‘Aha! Wannan shi ne magājin. Ku zo mu kashe shi, gādon kuma yă zama namu.’
А виноградари рекоше у себи: Ово је наследник, ходите да га убијемо, и нама ће остати очевина његова.
8 Sai suka kama shi suka kashe, suka jefa shi bayan gonar inabin.
И ухватише га, и убише, и избацише га напоље из винограда.
9 “To, me, mai gonar inabin zai yi ke nan? Zai zo yă karkashe dukan’yan hayan nan, ya kuma ba wa waɗansu gonar inabin.
Шта ће дакле учинити господар од винограда? Доћи ће и погубиће виноградаре, и даће виноград другима.
10 Ba ku taɓa karanta wannan Nassi ba, “‘Dutsen da magina suka ƙi, shi ne kuwa ya zama dutsen kusurwan gini.
Зар нисте читали у писму ово: Камен који одбацише зидари, онај поста глава од угла;
11 Ubangiji ya yi wannan, ya kuma yi kyau a idanunmu’?”
То би од Господа и дивно је у нашим очима?
12 Sai manyan Firistoci da malaman dokoki da shugabanni suka nemi hanyar da za su kama shi, domin sun gane ya yi misalin a kansu ne. Amma suka ji tsoron taron, saboda haka suka bar shi suka yi tafiyarsu.
И гледаху да Га ухвате, али се побојаше народа; јер разумеше да за њих говори причу; и оставивши Га одоше.
13 Daga baya, sai suka tura waɗansu Farisiyawa da mutanen Hiridus zuwa wurin Yesu, domin su sa masa tarko a cikin maganarsa.
И послаше к Њему неке од фарисеја и Иродоваца да би Га ухватили у речи.
14 Suka zo wurinsa suka ce, “Malam, mun san kai mutum ne mai mutunci. Ba ka bin ra’ayin mutane, don ba ka nuna bambanci. Amma kana koyar da hanyar Allah bisa ga gaskiya. Daidai ne a biya wa Kaisar haraji, ko babu?
А они дошавши рекоше Му: Учитељу! Знамо да си истинит, и да не мариш ни за кога; јер не гледаш ко је ко, него заиста путу Божјем учиш; треба ли ћесару давати харач или не? Хоћемо ли дати, или да не дамо?
15 Mu biya ko kada mu biya?” Amma Yesu ya san munafuncinsu, sai ya yi tambaya ya ce, “Don me kuke ƙoƙarin sa mini tarko? Ku kawo mini dinari in ga.”
А Он, знајући њихово лицемерје, рече им: Што ме кушате? Донесите ми новац да видим
16 Suka kawo masa kuɗin, sai ya tambaye, su ya ce, “Hoton wane ne wannan? Kuma rubutun wane ne wannan?” Suka ce, “Na Kaisar.”
А они донесоше. И рече им: Чији је ово образ и натпис? А они Му рекоше: Ћесарев.
17 Sai Yesu ya ce musu, “Ku ba wa Kaisar abin da yake na Kaisar, ku ba wa Allah kuma abin da yake na Allah.” Suka yi mamakinsa ƙwarai.
И одговарајући Исус рече им: Подајте ћесарево ћесару, а Божје Богу. И чудише Му се.
18 Sa’an nan Sadukiyawa da suke cewa, babu tashin matattu, suka zo masa da tambaya.
И дођоше к Њему садукеји који кажу да нема васкрсења, и запиташе Га говорећи:
19 Suka ce, “Malam, Musa ya rubuta mana cewa, in ɗan’uwan wani mutum ya mutu, ya bar mata babu’ya’ya, dole mutumin ya auri gwauruwar, yă kuma samo wa ɗan’uwansa’ya’ya.
Учитељу! Мојсије нам написа: Ако коме брат умре и остави жену а деце не остави, да брат његов узме жену његову и да подигне семе брату свом.
20 To, an yi waɗansu’yan’uwa guda bakwai. Na fari ya yi aure, ya mutu babu’ya’ya.
Седам браће беше: и први узе жену, и умре без порода.
21 Na biyun ya auri gwauruwar, sai shi ma ya mutu, babu’ya’ya. Haka kuma na ukun.
И други узе је, и умре, и ни он не остави порода; тако и трећи.
22 A gaskiya, ba ko ɗaya daga cikin bakwai ɗin da ya bar’ya’ya. Daga ƙarshe, macen ta mutu.
И узеше је седморица, и не оставише порода. А после свих умре и жена.
23 To, a tashin matattu, matar wa za tă zama, don duk su bakwai nan sun aure ta?”
О васкрсењу дакле кад устану кога ће од њих бити жена? Јер је за седморицом била.
24 Yesu ya ce, “Ashe, ba a cikin kuskure kuke ba saboda rashin sanin Nassi, ko ikon Allah?
И одговарајући Исус рече им: Зато ли се ви варате што не знате писма ни силе Божје?
25 Sa’ad da matattu suka tashi, ba za su yi aure ba, ba kuwa za a ba da su ga aure ba. Za su zama kamar yadda mala’iku suke a cikin sama.
Јер кад из мртвих устану, нити ће се женити ни удавати, него су као анђели на небесима.
26 Game da tashin matattu kuwa, ashe, ba ku karanta a cikin littafin Musa ba, game da labarin ɗan kurmin nan mai cin wuta da Musa ya gani a jeji, yadda Allah ya yi magana da shi ya ce, ‘Ni ne Allah na Ibrahim, Allah na Ishaku da kuma Allah na Yaƙub’?
А за мртве да устају нисте ли читали у књигама Мојсијевим како му рече Бог код купине говорећи: Ја сам Бог Авраамов, и Бог Исаков, и Бог Јаковљев?
27 Shi ba Allah na matattu ba ne, shi Allah na masu rai ne. Kun yi mummunan kuskure!”
Није Бог Бог мртвих, него Бог живих. Ви се дакле врло варате.
28 Wani daga cikin malaman dokoki ya zo ya ji suna muhawwara. Da ya lura cewa Yesu ya amsa musu daidai, sai ya tambaye shi ya ce, “A cikin dukan dokoki, wacce ta fi girma duka?”
И приступи један од књижевника који их слушаше како се препиру, и виде да им добро одговара, и запита Га: Која је прва заповест од свих?
29 Yesu ya ce, “Wadda ta fi girma duka, ita ce wannan. ‘Ku saurara, ya Isra’ila, Ubangiji Allahnmu, Ubangiji ɗaya ne.
А Исус одговори му: Прва је заповест од свих: Чуј Израиљу, Господ је Бог наш Господ једини;
30 Ka ƙaunaci Ubangiji Allahnka da dukan zuciyarka, da dukan ranka, da dukan hankalinka, da kuma dukan ƙarfinka.’
И љуби Господа Бога свог свим срцем својим и свом душом својом и свим умом својим и свом снагом својом. Ово је прва заповест.
31 Na biyun ita ce, ‘Ka ƙaunaci maƙwabcinka kamar kanka.’Ba wata doka da ta fi waɗannan.”
И друга је као и ова: Љуби ближњег свог као самог себе. Друге заповести веће од ових нема.
32 Mutumin ya ce, “Malam, ka faɗi daidai. Daidai ne da ka ce, Allah ɗaya ne, babu kuma wani sai shi.
И рече Му књижевник: Добро, учитељу! Право си казао да је један Бог, и нема другог осим Њега;
33 Nuna ƙauna ga Allah da dukan zuciyarka, da dukan ganewarka, da dukan ƙarfinka, da kuma nuna ƙauna ga maƙwabcinka kamar kanka, ya fi dukan hadayun ƙonawa da sadakoki.”
И љубити Га свим срцем и свим разумом и свом душом и свом снагом, и љубити ближњег као самог себе, веће је од свих жртава и прилога.
34 Da Yesu ya ga ya amsa da hikima, sai ya ce masa, “Ba ka da nisa da mulkin Allah.” Daga lokacin, ba wanda ya yi karambani yin masa wata tambaya.
А Исус видевши како паметно одговори рече му: Ниси далеко од царства Божјег. И нико више не смеше да Га запита.
35 Yayinda Yesu yake koyarwa a filin haikalin, sai ya yi tambaya ya ce, “Yaya malaman dokoki suke cewa Kiristi ɗan Dawuda ne?
И одговори Исус и рече учећи у цркви: Како говоре књижевници да је Христос син Давидов?
36 Dawuda da kansa ya yi magana ta wurin Ruhu Mai Tsarki ya ce, “‘Ubangiji ya ce wa Ubangijina, “Zauna a hannun damana sai na sa abokan gābanka a ƙarƙashin sawunka.”’
Јер сам Давид каза Духом Светим: Рече Господ Господу мом: Седи мени с десне стране, док положим непријатеље Твоје подножје ногама Твојим.
37 Dawuda da kansa ya kira shi ‘Ubangiji.’ To, ta yaya zai zama ɗansa?” Taro mai yawa suka saurare shi da murna.
Сам дакле Давид назива Га Господом, и откуда му је син? И многи народ слушаше Га с радошћу.
38 Sa’ad da Yesu yake koyarwa ya ce, “Ku lura da malaman dokoki. Sukan so yin tafiya a manyan riguna, a kuma dinga gaishe su a wuraren kasuwanci.
И говораше им у науци својој: Чувајте се књижевника који иду у дугачким хаљинама, и траже да им се клања по улицама,
39 Sukan kuma nemi wuraren zama mafi daraja a majami’u, da kuma wuraren zaman manya a bukukkuwa.
И првих места по зборницама, и зачеља на гозбама.
40 Suna ƙwace gidajen gwauraye, kuma don nuna iyawa, sukan yi dogayen addu’o’i. Irin mutanen nan, za su sha hukunci mai tsanani sosai.”
Ови што једу куће удовичке, и лажно се моле Богу дуго, биће још више осуђени.
41 Yesu ya zauna ɗaura da inda ake bayarwa, ya kuma dubi yadda taron suke sa kuɗinsu a cikin ɗakunan ajiya haikali. Masu arziki da yawa suka zuba kuɗaɗe masu yawa.
И седавши Исус према Божјој хазни гледаше како народ меће новце у Божју хазну. И многи богати метаху много.
42 Amma wata matalauciya gwauruwa, ta zo ta saka anini biyu, da suka yi daidai da rabin kobo.
И дошавши једна сиромашна удовица метну две лепте, које чине један кодрант.
43 Yesu ya kira almajiransa wurinsa ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, abin da matalauciya gwauruwan nan ta zuba cikin ɗakunan ajiya nan ya fi na sauran dukan.
И дозвавши ученике своје рече им: Заиста вам кажем: ова сиромашна удовица метну више од свих који мећу у Божју хазну.
44 Dukansu sun bayar ne daga cikin arzikinsu; ita kuwa, daga cikin talaucinta, ta ba da kome, duk abin da take da shi na rayuwa.”
Јер сви метнуше од сувишка свог; а она од сиротиње своје метну све што имаше, сву храну своју.

< Markus 12 >