< Markus 12 >

1 Sa’an nan ya fara yi musu magana da misalai ya ce, “Wani mutum ya shuka gonar inabi. Ya kewaye ta da katanga, ya haƙa rami domin matsin inabin, ya kuma gina ɗakin gadi. Sai ya ba wa waɗansu manoma hayar gonar inabin, sa’an nan ya yi tafiya.
عیسی برای تعلیم مردم، حکایات و مَثَلهای بسیاری بیان می‌کرد. او یکبار فرمود: «شخصی تاکستانی درست کرد و دور آن دیواری کشید. در آن حوضچه‌ای نیز برای گرفتن آب انگور کَند و یک برج دیدبانی نیز بنا کرد. سپس باغ را به چند باغبان اجاره داد و خود به سفر رفت.
2 Da lokacin girbi ya yi, sai ya aiki wani bawa wajen’yan hayan, don yă karɓo masa’ya’yan inabin daga wurinsu.
در فصل انگورچینی، خدمتکارش را فرستاد تا سهم خود را از محصول باغ بگیرد.
3 Amma suka kama shi, suka yi masa dūka, suka kore shi hannun wofi.
ولی باغبانها او را گرفته، زدند و دست خالی برگرداندند.
4 Sai ya sāke aikan wani bawa wurinsu, amma suka bugi wannan mutum a kai, suka wulaƙanta shi.
«صاحب باغ یک نفر دیگر را فرستاد؛ این بار به او دشنام دادند و او را زدند و سرش را نیز شکستند.
5 Har yanzu ya sāke aikan wani. Wannan kuwa suka kashe. Ya aika waɗansu da yawa; suka bubbuge waɗansu, sauran kuwa suka kashe.
نفر بعدی را نیز کشتند. دیگران را هم یا زدند یا کشتند.
6 “Sauran mutum ɗaya da ya rage ya aika, ɗa, da yake ƙauna. Daga ƙarshe sai ya aike shi, yana cewa, ‘Za su girmama ɗana.’
تا اینکه فقط یک نفر برای صاحب تاکستان باقی ماند، یعنی تنها پسرش. آخر او را فرستاد، با این تصور که به او احترام خواهند گذاشت.
7 “Amma’yan hayan suka ce wa juna, ‘Aha! Wannan shi ne magājin. Ku zo mu kashe shi, gādon kuma yă zama namu.’
«ولی باغبانها به یکدیگر گفتند:”او وارث است؛ پس بیایید او را بکشیم تا باغ مال ما شود.“
8 Sai suka kama shi suka kashe, suka jefa shi bayan gonar inabin.
پس او را گرفتند و کشتند و جنازه‌اش را از باغ بیرون انداختند.
9 “To, me, mai gonar inabin zai yi ke nan? Zai zo yă karkashe dukan’yan hayan nan, ya kuma ba wa waɗansu gonar inabin.
«حال به نظر شما، صاحب باغ چه خواهد کرد؟ او خواهد آمد و همۀ باغبانها را خواهد کشت و باغ را به دیگران اجاره خواهد داد.
10 Ba ku taɓa karanta wannan Nassi ba, “‘Dutsen da magina suka ƙi, shi ne kuwa ya zama dutsen kusurwan gini.
مگر در کتب مقدّس نخوانده‌اید که:”سنگی که معماران دور افکندند، سنگ اصلی ساختمان شده است.
11 Ubangiji ya yi wannan, ya kuma yi kyau a idanunmu’?”
این کارِ خداوند است و در نظر ما عجیب می‌نماید“.»
12 Sai manyan Firistoci da malaman dokoki da shugabanni suka nemi hanyar da za su kama shi, domin sun gane ya yi misalin a kansu ne. Amma suka ji tsoron taron, saboda haka suka bar shi suka yi tafiyarsu.
سران قوم یهود خواستند همان جا او را بگیرند، چون فهمیدند که منظور عیسی از باغبانهای ظالم، اشاره به ایشان می‌باشد. اما از مردم ترسیدند، پس او را به حال خود گذاشتند و رفتند.
13 Daga baya, sai suka tura waɗansu Farisiyawa da mutanen Hiridus zuwa wurin Yesu, domin su sa masa tarko a cikin maganarsa.
اما بعداً، چند تن از فریسیان و هیرودیان را به عنوان جاسوس فرستادند تا از گفته‌های عیسی دلیلی بیابند و بازداشتش کنند.
14 Suka zo wurinsa suka ce, “Malam, mun san kai mutum ne mai mutunci. Ba ka bin ra’ayin mutane, don ba ka nuna bambanci. Amma kana koyar da hanyar Allah bisa ga gaskiya. Daidai ne a biya wa Kaisar haraji, ko babu?
پس جاسوسان آمدند و گفتند: «استاد، می‌دانیم مردی صادق هستی، و از کسی ترس نداری زیرا تحت تأثیر ظاهر و مقام افراد قرار نمی‌گیری، بلکه راه خدا را به درستی تعلیم می‌دهی. آیا باید به دولت روم خَراج داد یا نه؟»
15 Mu biya ko kada mu biya?” Amma Yesu ya san munafuncinsu, sai ya yi tambaya ya ce, “Don me kuke ƙoƙarin sa mini tarko? Ku kawo mini dinari in ga.”
عیسی متوجهٔ نیرنگ ایشان شد و فرمود: «چرا می‌خواهید مرا آزمایش کنید. سکه‌ای به من نشان دهید تا بگویم.»
16 Suka kawo masa kuɗin, sai ya tambaye, su ya ce, “Hoton wane ne wannan? Kuma rubutun wane ne wannan?” Suka ce, “Na Kaisar.”
وقتی سکه را به او دادند، پرسید: «نقش و اسم چه کسی روی این سکه است؟» جواب دادند: «قیصر روم.»
17 Sai Yesu ya ce musu, “Ku ba wa Kaisar abin da yake na Kaisar, ku ba wa Allah kuma abin da yake na Allah.” Suka yi mamakinsa ƙwarai.
فرمود: «مال قیصر را به قیصر بدهید، و مال خدا را به خدا!» جواب عیسی ایشان را حیران کرد.
18 Sa’an nan Sadukiyawa da suke cewa, babu tashin matattu, suka zo masa da tambaya.
سپس عده‌ای از صدوقی‌ها که منکر قیامت هستند، نزد او آمدند و پرسیدند:
19 Suka ce, “Malam, Musa ya rubuta mana cewa, in ɗan’uwan wani mutum ya mutu, ya bar mata babu’ya’ya, dole mutumin ya auri gwauruwar, yă kuma samo wa ɗan’uwansa’ya’ya.
«استاد، در تورات موسی آمده است که اگر مردی بی‌اولاد فوت شود، برادر آن مرد باید آن زن بیوه را به همسری بگیرد، و برای برادر خود نسلی باقی بگذارد.
20 To, an yi waɗansu’yan’uwa guda bakwai. Na fari ya yi aure, ya mutu babu’ya’ya.
حال، هفت برادر بودند؛ اولی زنی گرفت و بی‌اولاد مُرد.
21 Na biyun ya auri gwauruwar, sai shi ma ya mutu, babu’ya’ya. Haka kuma na ukun.
پس دومی همسر او را به زنی گرفت، ولی او هم بی‌فرزند مرد. سومی هم او را به زنی گرفت و بی‌اولاد فوت کرد.
22 A gaskiya, ba ko ɗaya daga cikin bakwai ɗin da ya bar’ya’ya. Daga ƙarshe, macen ta mutu.
و به همین ترتیب، همهٔ برادرها مردند ولی هیچ‌کدام صاحب فرزند نشدند. سرانجام آن زن نیز مرد.
23 To, a tashin matattu, matar wa za tă zama, don duk su bakwai nan sun aure ta?”
حال در روز قیامت، آن زن، همسر کدام یک از این برادران خواهد بود؟ چون او در واقع زن همهٔ ایشان بوده است.»
24 Yesu ya ce, “Ashe, ba a cikin kuskure kuke ba saboda rashin sanin Nassi, ko ikon Allah?
عیسی جواب داد: «شما چقدر گمراهید، زیرا نه از کلام خدا چیزی می‌دانید نه از قدرت خدا.
25 Sa’ad da matattu suka tashi, ba za su yi aure ba, ba kuwa za a ba da su ga aure ba. Za su zama kamar yadda mala’iku suke a cikin sama.
زیرا در روز قیامت، انسانها دیگر ازدواج نمی‌کنند بلکه مثل فرشتگان آسمان خواهند بود.
26 Game da tashin matattu kuwa, ashe, ba ku karanta a cikin littafin Musa ba, game da labarin ɗan kurmin nan mai cin wuta da Musa ya gani a jeji, yadda Allah ya yi magana da shi ya ce, ‘Ni ne Allah na Ibrahim, Allah na Ishaku da kuma Allah na Yaƙub’?
«اما دربارهٔ زنده شدن مردگان، مگر سرگذشت موسی و بوتهٔ سوزان را در کتاب تورات نخوانده‌اید؟ در آنجا خدا به موسی فرمود: من هستم خدای ابراهیم، خدای اسحاق و خدای یعقوب.
27 Shi ba Allah na matattu ba ne, shi Allah na masu rai ne. Kun yi mummunan kuskure!”
پس خدا، خدای مردگان نیست، بلکه خدای زندگان می‌باشد. حال می‌بینید چقدر در اشتباهید!»
28 Wani daga cikin malaman dokoki ya zo ya ji suna muhawwara. Da ya lura cewa Yesu ya amsa musu daidai, sai ya tambaye shi ya ce, “A cikin dukan dokoki, wacce ta fi girma duka?”
یکی از علمای دین که در آنجا ایستاده بود و به گفت و گوی ایشان گوش می‌داد، وقتی دید عیسی چه جواب دندان‌شکنی به آنان داد، پرسید: «از تمام احکام خدا، کدام یک از همه مهمتر است؟»
29 Yesu ya ce, “Wadda ta fi girma duka, ita ce wannan. ‘Ku saurara, ya Isra’ila, Ubangiji Allahnmu, Ubangiji ɗaya ne.
عیسی پاسخ داد: «مهمترین حکم این است:”بشنو، ای اسرائیل، خداوند خدای ما، خداوند یکتاست.
30 Ka ƙaunaci Ubangiji Allahnka da dukan zuciyarka, da dukan ranka, da dukan hankalinka, da kuma dukan ƙarfinka.’
خداوند، خدای خود را با تمامی دل و با تمامی جان و با تمامی فکر و با تمامی قوّت خود دوست بدار.“
31 Na biyun ita ce, ‘Ka ƙaunaci maƙwabcinka kamar kanka.’Ba wata doka da ta fi waɗannan.”
«و دومین حکم مهم این است:”همسایه‌ات را همچون جان خویش دوست بدار.“«هیچ دستوری مهمتر از این دو نیست.»
32 Mutumin ya ce, “Malam, ka faɗi daidai. Daidai ne da ka ce, Allah ɗaya ne, babu kuma wani sai shi.
عالِم مذهبی در جواب عیسی گفت: «استاد، کاملاً درست فرمودید. فقط یک خدا وجود دارد و غیر از او خدای دیگری نیست.
33 Nuna ƙauna ga Allah da dukan zuciyarka, da dukan ganewarka, da dukan ƙarfinka, da kuma nuna ƙauna ga maƙwabcinka kamar kanka, ya fi dukan hadayun ƙonawa da sadakoki.”
و من قبول دارم که دوست داشتن خدا با تمامی دل و با تمامی عقل و با تمامی قوت خود و دوست داشتن همسایه همچون جان خویش مهمتر از همۀ هدایا و قربانیهاست.»
34 Da Yesu ya ga ya amsa da hikima, sai ya ce masa, “Ba ka da nisa da mulkin Allah.” Daga lokacin, ba wanda ya yi karambani yin masa wata tambaya.
عیسی که دید این شخص متوجهٔ حقیقت شده است، فرمود: «تو از ملکوت خدا دور نیستی.» پس از آن دیگر کسی جرأت نکرد سؤالی از او بپرسد.
35 Yayinda Yesu yake koyarwa a filin haikalin, sai ya yi tambaya ya ce, “Yaya malaman dokoki suke cewa Kiristi ɗan Dawuda ne?
یک روز که عیسی در معبد به مردم تعلیم می‌داد، پرسید: «چرا علمای دین می‌گویند که مسیح موعود، پسر داوود است؟
36 Dawuda da kansa ya yi magana ta wurin Ruhu Mai Tsarki ya ce, “‘Ubangiji ya ce wa Ubangijina, “Zauna a hannun damana sai na sa abokan gābanka a ƙarƙashin sawunka.”’
در حالی که داوود خودش، وقتی از روح خدا به او الهام شد، چنین گفت:”خداوند به خداوند من گفت: به دست راست من بنشین تا دشمنانت را به زیر پایت بیفکنم.“
37 Dawuda da kansa ya kira shi ‘Ubangiji.’ To, ta yaya zai zama ɗansa?” Taro mai yawa suka saurare shi da murna.
اگر داوود خودش، مسیح را”خداوند من“می‌خواند، چگونه ممکن است مسیح پسر او باشد؟» مردم از این گونه سؤالات بسیار لذت می‌بردند و با شور و علاقهٔ فراوان به سخنان او گوش می‌دادند.
38 Sa’ad da Yesu yake koyarwa ya ce, “Ku lura da malaman dokoki. Sukan so yin tafiya a manyan riguna, a kuma dinga gaishe su a wuraren kasuwanci.
باز خطاب به مردم فرمود: «از این علمای متظاهر دینی دوری کنید که دوست دارند با قباهای بلند، خودنمایی کنند و به هنگام عبور از کوچه و بازار، مردم به ایشان تعظیم کنند؛
39 Sukan kuma nemi wuraren zama mafi daraja a majami’u, da kuma wuraren zaman manya a bukukkuwa.
و چقدر دوست دارند که در کنیسه‌ها بهترین جا را داشته باشند و در ضیافت‌ها بر صدر مجلس بنشینند.
40 Suna ƙwace gidajen gwauraye, kuma don nuna iyawa, sukan yi dogayen addu’o’i. Irin mutanen nan, za su sha hukunci mai tsanani sosai.”
اما حتی وقتی دعاهای طولانی می‌کنند و تظاهر به دینداری می‌نمایند، تمام هوش و حواسشان به این است که چگونه اموال بیوه‌زنان را تصاحب کنند. از این رو مجازات آنان بسیار شدید خواهد بود.»
41 Yesu ya zauna ɗaura da inda ake bayarwa, ya kuma dubi yadda taron suke sa kuɗinsu a cikin ɗakunan ajiya haikali. Masu arziki da yawa suka zuba kuɗaɗe masu yawa.
سپس عیسی به مکانی از معبد رفت که در آنجا صندوق اعانات قرار داشت. او به مردمی که پول خود را در صندوق می‌انداختند، می‌نگریست. بعضی که ثروتمند بودند، مبلغ زیادی تقدیم می‌کردند.
42 Amma wata matalauciya gwauruwa, ta zo ta saka anini biyu, da suka yi daidai da rabin kobo.
در آن میان، بیوه‌زن فقیری آمد و دو سکهٔ ناچیز در صندوق انداخت.
43 Yesu ya kira almajiransa wurinsa ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, abin da matalauciya gwauruwan nan ta zuba cikin ɗakunan ajiya nan ya fi na sauran dukan.
عیسی شاگردان خود را فرا خواند و به ایشان فرمود: «آنچه این بیوه‌زن فقیر در صندوق انداخت، از تمام آنچه که این ثروتمندان هدیه کردند، بیشتر بود.
44 Dukansu sun bayar ne daga cikin arzikinsu; ita kuwa, daga cikin talaucinta, ta ba da kome, duk abin da take da shi na rayuwa.”
چون آنها قسمت کوچکی از آنچه را که احتیاج نداشتند دادند، ولی این زن فقیر هر چه داشت، یعنی تمام روزی خود را داد.»

< Markus 12 >