< Markus 12 >
1 Sa’an nan ya fara yi musu magana da misalai ya ce, “Wani mutum ya shuka gonar inabi. Ya kewaye ta da katanga, ya haƙa rami domin matsin inabin, ya kuma gina ɗakin gadi. Sai ya ba wa waɗansu manoma hayar gonar inabin, sa’an nan ya yi tafiya.
Then Jesus began to teach them in parables. He said, “A man planted a vineyard, put a hedge around it, and dug a pit for a winepress. He built a watchtower and then leased the vineyard to vine growers. Then he went away on a journey.
2 Da lokacin girbi ya yi, sai ya aiki wani bawa wajen’yan hayan, don yă karɓo masa’ya’yan inabin daga wurinsu.
At the right time, he sent a servant to the vine growers to receive from them some of the fruit of the vineyard.
3 Amma suka kama shi, suka yi masa dūka, suka kore shi hannun wofi.
But they took him, beat him, and sent him away with nothing.
4 Sai ya sāke aikan wani bawa wurinsu, amma suka bugi wannan mutum a kai, suka wulaƙanta shi.
Again he sent to them another servant, and they wounded him in the head and treated him shamefully.
5 Har yanzu ya sāke aikan wani. Wannan kuwa suka kashe. Ya aika waɗansu da yawa; suka bubbuge waɗansu, sauran kuwa suka kashe.
He sent yet another, and this one they killed. They treated many others in the same way, beating some and killing others.
6 “Sauran mutum ɗaya da ya rage ya aika, ɗa, da yake ƙauna. Daga ƙarshe sai ya aike shi, yana cewa, ‘Za su girmama ɗana.’
He had still one more person to send, a beloved son. He was the last one he sent to them. He said, 'They will respect my son.'
7 “Amma’yan hayan suka ce wa juna, ‘Aha! Wannan shi ne magājin. Ku zo mu kashe shi, gādon kuma yă zama namu.’
But the vine growers said to one another, 'This is the heir. Come, let us kill him, and the inheritance will be ours.'
8 Sai suka kama shi suka kashe, suka jefa shi bayan gonar inabin.
They seized him, killed him, and threw him out of the vineyard.
9 “To, me, mai gonar inabin zai yi ke nan? Zai zo yă karkashe dukan’yan hayan nan, ya kuma ba wa waɗansu gonar inabin.
Therefore, what will the owner of the vineyard do? He will come and destroy the vine growers and will give the vineyard to others.
10 Ba ku taɓa karanta wannan Nassi ba, “‘Dutsen da magina suka ƙi, shi ne kuwa ya zama dutsen kusurwan gini.
Have you not read this scripture? 'The stone which the builders rejected has been made the cornerstone.
11 Ubangiji ya yi wannan, ya kuma yi kyau a idanunmu’?”
This was from the Lord, and it is marvelous in our eyes.'”
12 Sai manyan Firistoci da malaman dokoki da shugabanni suka nemi hanyar da za su kama shi, domin sun gane ya yi misalin a kansu ne. Amma suka ji tsoron taron, saboda haka suka bar shi suka yi tafiyarsu.
They sought to arrest Jesus, but they feared the crowd, for they knew that he had spoken this parable against them. So they left him and went away.
13 Daga baya, sai suka tura waɗansu Farisiyawa da mutanen Hiridus zuwa wurin Yesu, domin su sa masa tarko a cikin maganarsa.
Then they sent some of the Pharisees and the Herodians to him to trap him with words.
14 Suka zo wurinsa suka ce, “Malam, mun san kai mutum ne mai mutunci. Ba ka bin ra’ayin mutane, don ba ka nuna bambanci. Amma kana koyar da hanyar Allah bisa ga gaskiya. Daidai ne a biya wa Kaisar haraji, ko babu?
When they came, they said to him, “Teacher, we know that you care for no one's opinion, and you do not show partiality between people. You truly teach the way of God. Is it lawful to pay taxes to Caesar or not? Should we pay or not?”
15 Mu biya ko kada mu biya?” Amma Yesu ya san munafuncinsu, sai ya yi tambaya ya ce, “Don me kuke ƙoƙarin sa mini tarko? Ku kawo mini dinari in ga.”
But Jesus knew their hypocrisy and said to them, “Why do you test me? Bring me a denarius so I can look at it.”
16 Suka kawo masa kuɗin, sai ya tambaye, su ya ce, “Hoton wane ne wannan? Kuma rubutun wane ne wannan?” Suka ce, “Na Kaisar.”
They brought one to Jesus. He said to them, “Whose likeness and inscription is this?” They said, “Caesar's.”
17 Sai Yesu ya ce musu, “Ku ba wa Kaisar abin da yake na Kaisar, ku ba wa Allah kuma abin da yake na Allah.” Suka yi mamakinsa ƙwarai.
Jesus said, “Give to Caesar the things that are Caesar's, and to God the things that are God's.” They marveled at him.
18 Sa’an nan Sadukiyawa da suke cewa, babu tashin matattu, suka zo masa da tambaya.
Then Sadducees, who say there is no resurrection, came to him. They asked him, saying,
19 Suka ce, “Malam, Musa ya rubuta mana cewa, in ɗan’uwan wani mutum ya mutu, ya bar mata babu’ya’ya, dole mutumin ya auri gwauruwar, yă kuma samo wa ɗan’uwansa’ya’ya.
“Teacher, Moses wrote for us, 'If a man's brother dies and leaves a wife behind him, but no child, the man should take the brother's wife, and raise up a descendant for his brother.'
20 To, an yi waɗansu’yan’uwa guda bakwai. Na fari ya yi aure, ya mutu babu’ya’ya.
There were seven brothers; the first took a wife and then died, leaving no children.
21 Na biyun ya auri gwauruwar, sai shi ma ya mutu, babu’ya’ya. Haka kuma na ukun.
Then the second took her and died, leaving no children, and the third likewise.
22 A gaskiya, ba ko ɗaya daga cikin bakwai ɗin da ya bar’ya’ya. Daga ƙarshe, macen ta mutu.
The seven left no children. Last of all, the woman also died.
23 To, a tashin matattu, matar wa za tă zama, don duk su bakwai nan sun aure ta?”
In the resurrection, when they rise again, whose wife will she be? For all seven brothers had her as their wife.”
24 Yesu ya ce, “Ashe, ba a cikin kuskure kuke ba saboda rashin sanin Nassi, ko ikon Allah?
Jesus said, “Is this not the reason you are mistaken, because you do not know the scriptures nor the power of God?
25 Sa’ad da matattu suka tashi, ba za su yi aure ba, ba kuwa za a ba da su ga aure ba. Za su zama kamar yadda mala’iku suke a cikin sama.
For when they rise from the dead, they neither marry nor are given in marriage, but they are like angels in heaven.
26 Game da tashin matattu kuwa, ashe, ba ku karanta a cikin littafin Musa ba, game da labarin ɗan kurmin nan mai cin wuta da Musa ya gani a jeji, yadda Allah ya yi magana da shi ya ce, ‘Ni ne Allah na Ibrahim, Allah na Ishaku da kuma Allah na Yaƙub’?
But concerning the dead that are raised, have you not read in the Book of Moses, in the account about the bush, how God spoke to him and said, 'I am the God of Abraham and the God of Isaac and the God of Jacob'?
27 Shi ba Allah na matattu ba ne, shi Allah na masu rai ne. Kun yi mummunan kuskure!”
He is not the God of the dead, but of the living. You are quite mistaken.”
28 Wani daga cikin malaman dokoki ya zo ya ji suna muhawwara. Da ya lura cewa Yesu ya amsa musu daidai, sai ya tambaye shi ya ce, “A cikin dukan dokoki, wacce ta fi girma duka?”
One of the scribes came and heard their discussion; he saw that Jesus answered them well. He asked him, “What commandment is the most important of all?”
29 Yesu ya ce, “Wadda ta fi girma duka, ita ce wannan. ‘Ku saurara, ya Isra’ila, Ubangiji Allahnmu, Ubangiji ɗaya ne.
Jesus answered, “The most important is, 'Hear, Israel, the Lord our God, the Lord is one.
30 Ka ƙaunaci Ubangiji Allahnka da dukan zuciyarka, da dukan ranka, da dukan hankalinka, da kuma dukan ƙarfinka.’
You must love the Lord your God with all your heart, with all your soul, with all your mind, and with all your strength.'
31 Na biyun ita ce, ‘Ka ƙaunaci maƙwabcinka kamar kanka.’Ba wata doka da ta fi waɗannan.”
The second commandment is this, 'You must love your neighbor as yourself.' There is no other greater commandment than these.”
32 Mutumin ya ce, “Malam, ka faɗi daidai. Daidai ne da ka ce, Allah ɗaya ne, babu kuma wani sai shi.
The scribe said, “Good, Teacher! You have truly said that God is one, and that there is no other besides him.
33 Nuna ƙauna ga Allah da dukan zuciyarka, da dukan ganewarka, da dukan ƙarfinka, da kuma nuna ƙauna ga maƙwabcinka kamar kanka, ya fi dukan hadayun ƙonawa da sadakoki.”
To love him with all the heart and with all the understanding and with all the strength, and to love one's neighbor as oneself, is even more than all burnt offerings and sacrifices.”
34 Da Yesu ya ga ya amsa da hikima, sai ya ce masa, “Ba ka da nisa da mulkin Allah.” Daga lokacin, ba wanda ya yi karambani yin masa wata tambaya.
When Jesus saw that he had given a wise answer, he said to him, “You are not far from the kingdom of God.” After that, no one dared to ask Jesus any more questions.
35 Yayinda Yesu yake koyarwa a filin haikalin, sai ya yi tambaya ya ce, “Yaya malaman dokoki suke cewa Kiristi ɗan Dawuda ne?
While Jesus was teaching in the temple courts, he said, “How is it that the scribes say the Christ is the son of David?
36 Dawuda da kansa ya yi magana ta wurin Ruhu Mai Tsarki ya ce, “‘Ubangiji ya ce wa Ubangijina, “Zauna a hannun damana sai na sa abokan gābanka a ƙarƙashin sawunka.”’
David himself, in the Holy Spirit, said, 'The Lord said to my Lord, “Sit at my right hand, until I make your enemies your footstool.”'
37 Dawuda da kansa ya kira shi ‘Ubangiji.’ To, ta yaya zai zama ɗansa?” Taro mai yawa suka saurare shi da murna.
David himself calls him 'Lord,' so how can the Christ be David's son?” The large crowd gladly listened to him.
38 Sa’ad da Yesu yake koyarwa ya ce, “Ku lura da malaman dokoki. Sukan so yin tafiya a manyan riguna, a kuma dinga gaishe su a wuraren kasuwanci.
In his teaching Jesus said, “Beware of the scribes, who like to walk in long robes and they like the greetings they receive in the marketplaces
39 Sukan kuma nemi wuraren zama mafi daraja a majami’u, da kuma wuraren zaman manya a bukukkuwa.
and they like to have the chief seats in the synagogues and chief places at feasts.
40 Suna ƙwace gidajen gwauraye, kuma don nuna iyawa, sukan yi dogayen addu’o’i. Irin mutanen nan, za su sha hukunci mai tsanani sosai.”
They also devour widows' houses, and they pray long prayers for people to see. These men will receive greater condemnation.”
41 Yesu ya zauna ɗaura da inda ake bayarwa, ya kuma dubi yadda taron suke sa kuɗinsu a cikin ɗakunan ajiya haikali. Masu arziki da yawa suka zuba kuɗaɗe masu yawa.
Then Jesus sat down across from an offering box in the temple area; he was watching people as they dropped their money into the box. Many rich people put in large amounts of money.
42 Amma wata matalauciya gwauruwa, ta zo ta saka anini biyu, da suka yi daidai da rabin kobo.
Then a poor widow came and put in two mites, worth about a penny.
43 Yesu ya kira almajiransa wurinsa ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, abin da matalauciya gwauruwan nan ta zuba cikin ɗakunan ajiya nan ya fi na sauran dukan.
He called his disciples and said to them, “Truly I say to you, this poor widow has put in more than all of them who contributed to the offering box.
44 Dukansu sun bayar ne daga cikin arzikinsu; ita kuwa, daga cikin talaucinta, ta ba da kome, duk abin da take da shi na rayuwa.”
For all of them gave out of their abundance. But this widow, out of her poverty, put in all of the money which she had to live on. “