< Markus 12 >
1 Sa’an nan ya fara yi musu magana da misalai ya ce, “Wani mutum ya shuka gonar inabi. Ya kewaye ta da katanga, ya haƙa rami domin matsin inabin, ya kuma gina ɗakin gadi. Sai ya ba wa waɗansu manoma hayar gonar inabin, sa’an nan ya yi tafiya.
Then addressing them in parables, he said, A man planted a vineyard, and hedged it about, and dug a place for a wine vat, and built a tower, and having farmed it out, went abroad.
2 Da lokacin girbi ya yi, sai ya aiki wani bawa wajen’yan hayan, don yă karɓo masa’ya’yan inabin daga wurinsu.
The season being come, he sent a servant to the husbandmen, to receive his portion of the fruits of the vineyard.
3 Amma suka kama shi, suka yi masa dūka, suka kore shi hannun wofi.
But they seized him, beat him, and sent him away empty.
4 Sai ya sāke aikan wani bawa wurinsu, amma suka bugi wannan mutum a kai, suka wulaƙanta shi.
Again, he sent to them another servant, whom they wounded in the head with stones, and sent back with disgrace.
5 Har yanzu ya sāke aikan wani. Wannan kuwa suka kashe. Ya aika waɗansu da yawa; suka bubbuge waɗansu, sauran kuwa suka kashe.
He sent another, whom they killed; and of many more that he sent, some they beat, and some they killed.
6 “Sauran mutum ɗaya da ya rage ya aika, ɗa, da yake ƙauna. Daga ƙarshe sai ya aike shi, yana cewa, ‘Za su girmama ɗana.’
At last, having an only son, whom he loved, he sent him also to them; for he said, They will reverence my son.
7 “Amma’yan hayan suka ce wa juna, ‘Aha! Wannan shi ne magājin. Ku zo mu kashe shi, gādon kuma yă zama namu.’
But those husbandmen said among themselves, This is the heir; come, let us kill him, and the inheritance will be our own.
8 Sai suka kama shi suka kashe, suka jefa shi bayan gonar inabin.
Then they laid hold on him, and having thrust him out of the vineyard, they killed him.
9 “To, me, mai gonar inabin zai yi ke nan? Zai zo yă karkashe dukan’yan hayan nan, ya kuma ba wa waɗansu gonar inabin.
What, therefore, will the proprietor of the vineyard do? He will come and destroy the husbandmen, and give the vineyard to others.
10 Ba ku taɓa karanta wannan Nassi ba, “‘Dutsen da magina suka ƙi, shi ne kuwa ya zama dutsen kusurwan gini.
Have you not read this passage of scripture, "A stone which the builders rejected, is made the head of the corner:
11 Ubangiji ya yi wannan, ya kuma yi kyau a idanunmu’?”
this the Lord has performed, and we behold it with admiration?"
12 Sai manyan Firistoci da malaman dokoki da shugabanni suka nemi hanyar da za su kama shi, domin sun gane ya yi misalin a kansu ne. Amma suka ji tsoron taron, saboda haka suka bar shi suka yi tafiyarsu.
And they desired to have seized him, but were afraid of the multitude; for they knew that he spoke the parable against them.
13 Daga baya, sai suka tura waɗansu Farisiyawa da mutanen Hiridus zuwa wurin Yesu, domin su sa masa tarko a cikin maganarsa.
Then the chief priests, the scribes, and the elders, leaving Jesus, went away, and sent to him certain Pharisees and Herodians, to catch him in his words.
14 Suka zo wurinsa suka ce, “Malam, mun san kai mutum ne mai mutunci. Ba ka bin ra’ayin mutane, don ba ka nuna bambanci. Amma kana koyar da hanyar Allah bisa ga gaskiya. Daidai ne a biya wa Kaisar haraji, ko babu?
These coming up, said to him, Rabbi, we know that you are upright, and stand in awe of none; for you respect not the person of men, but teach the way of God faithfully. Is it lawful to give tribute to Cesar, or not?
15 Mu biya ko kada mu biya?” Amma Yesu ya san munafuncinsu, sai ya yi tambaya ya ce, “Don me kuke ƙoƙarin sa mini tarko? Ku kawo mini dinari in ga.”
Shall we give, or shall we not give? He, perceiving their artifice, answered, Why would you entangle me? Bring me a denarius, that I may see it.
16 Suka kawo masa kuɗin, sai ya tambaye, su ya ce, “Hoton wane ne wannan? Kuma rubutun wane ne wannan?” Suka ce, “Na Kaisar.”
When they had brought, he asked them, Whose is the image and inscription? They answered, Cesar's.
17 Sai Yesu ya ce musu, “Ku ba wa Kaisar abin da yake na Kaisar, ku ba wa Allah kuma abin da yake na Allah.” Suka yi mamakinsa ƙwarai.
Jesus replied, Render to Cesar that which is Cesar's, and to God that which is God's. And they wondered at him.
18 Sa’an nan Sadukiyawa da suke cewa, babu tashin matattu, suka zo masa da tambaya.
Then Sadducees came to him, who say that there is no future life, and proposed this questions:
19 Suka ce, “Malam, Musa ya rubuta mana cewa, in ɗan’uwan wani mutum ya mutu, ya bar mata babu’ya’ya, dole mutumin ya auri gwauruwar, yă kuma samo wa ɗan’uwansa’ya’ya.
Rabbi, Moses has enacted, that if a man's brother die, survived by a wife without children, he shall marry the widow, and raise issue to his brother.
20 To, an yi waɗansu’yan’uwa guda bakwai. Na fari ya yi aure, ya mutu babu’ya’ya.
Now there were seven brothers. The first took a wife, and dying, left no issue.
21 Na biyun ya auri gwauruwar, sai shi ma ya mutu, babu’ya’ya. Haka kuma na ukun.
The second married her, and died; neither did he leave any issue; so did also the third.
22 A gaskiya, ba ko ɗaya daga cikin bakwai ɗin da ya bar’ya’ya. Daga ƙarshe, macen ta mutu.
Thus all seven married her, and left no issue. Last of all, the woman also died.
23 To, a tashin matattu, matar wa za tă zama, don duk su bakwai nan sun aure ta?”
At the resurrection, therefore, when they are risen, to which of the seven will she belong; for she has been the wife of them all?
24 Yesu ya ce, “Ashe, ba a cikin kuskure kuke ba saboda rashin sanin Nassi, ko ikon Allah?
Jesus answering, said to them, Is not this the source of your error, your not knowing the scriptures, nor the power of God?
25 Sa’ad da matattu suka tashi, ba za su yi aure ba, ba kuwa za a ba da su ga aure ba. Za su zama kamar yadda mala’iku suke a cikin sama.
For there will be neither marrying, nor giving in marriage, among them who rise from the dead. They will then resemble the angels.
26 Game da tashin matattu kuwa, ashe, ba ku karanta a cikin littafin Musa ba, game da labarin ɗan kurmin nan mai cin wuta da Musa ya gani a jeji, yadda Allah ya yi magana da shi ya ce, ‘Ni ne Allah na Ibrahim, Allah na Ishaku da kuma Allah na Yaƙub’?
But as to the dead, that they are raised, have you not read in the book of Moses, how God spoke to him in the bush, saying, "I am the God of Abraham, and the God of Isaac, and the God of Jacob."
27 Shi ba Allah na matattu ba ne, shi Allah na masu rai ne. Kun yi mummunan kuskure!”
God is not a God of the dead, but of the living. Therefore you greatly err.
28 Wani daga cikin malaman dokoki ya zo ya ji suna muhawwara. Da ya lura cewa Yesu ya amsa musu daidai, sai ya tambaye shi ya ce, “A cikin dukan dokoki, wacce ta fi girma duka?”
A scribe, who had heard them dispute, perceiving the justness of his reply, came to him, and proposed this question: Which is the chief commandment of all?
29 Yesu ya ce, “Wadda ta fi girma duka, ita ce wannan. ‘Ku saurara, ya Isra’ila, Ubangiji Allahnmu, Ubangiji ɗaya ne.
Jesus answered, The chief of all the commandments is, "Hearken, Israel, the Lord is our God. The Lord is one:"
30 Ka ƙaunaci Ubangiji Allahnka da dukan zuciyarka, da dukan ranka, da dukan hankalinka, da kuma dukan ƙarfinka.’
and, "You shall love the Lord your God with all your heart, and with all your soul, and with all your mind, and with all your strength." This is the first commandment.
31 Na biyun ita ce, ‘Ka ƙaunaci maƙwabcinka kamar kanka.’Ba wata doka da ta fi waɗannan.”
The second resembles it: "You shall love your neighbor as yourself." There is no commandment greater than these.
32 Mutumin ya ce, “Malam, ka faɗi daidai. Daidai ne da ka ce, Allah ɗaya ne, babu kuma wani sai shi.
The scribe replied, Truly, Rabbi, you have answered well. There is one, and only one;
33 Nuna ƙauna ga Allah da dukan zuciyarka, da dukan ganewarka, da dukan ƙarfinka, da kuma nuna ƙauna ga maƙwabcinka kamar kanka, ya fi dukan hadayun ƙonawa da sadakoki.”
and to love him with all the heart, and with all the spirit, and with all the soul, and with all the strength; and to love one's self, is more than all burnt offerings and sacrifices.
34 Da Yesu ya ga ya amsa da hikima, sai ya ce masa, “Ba ka da nisa da mulkin Allah.” Daga lokacin, ba wanda ya yi karambani yin masa wata tambaya.
Jesus observing how pertinently he had answered, said to him, You are not far from the kingdom of God. After that, no person ventured to put questions to him.
35 Yayinda Yesu yake koyarwa a filin haikalin, sai ya yi tambaya ya ce, “Yaya malaman dokoki suke cewa Kiristi ɗan Dawuda ne?
As Jesus was teaching in the temple, he asked them, Why do you scribes assert, that the Messiah must be a son of David?
36 Dawuda da kansa ya yi magana ta wurin Ruhu Mai Tsarki ya ce, “‘Ubangiji ya ce wa Ubangijina, “Zauna a hannun damana sai na sa abokan gābanka a ƙarƙashin sawunka.”’
Yet David, himself, speaking by the Holy Spirit, says, "The Lord, said to my Lord, Sit at my right hand, until I make your foes your footstool."
37 Dawuda da kansa ya kira shi ‘Ubangiji.’ To, ta yaya zai zama ɗansa?” Taro mai yawa suka saurare shi da murna.
David himself, therefore, calls him his Lord; how then can he be his son? And the common people heard him with delight.
38 Sa’ad da Yesu yake koyarwa ya ce, “Ku lura da malaman dokoki. Sukan so yin tafiya a manyan riguna, a kuma dinga gaishe su a wuraren kasuwanci.
Further, in teaching, he said to them, Beware of the scribes, who affect to walk in robes; who love salutations in public places,
39 Sukan kuma nemi wuraren zama mafi daraja a majami’u, da kuma wuraren zaman manya a bukukkuwa.
and the principal seats in the synagogues, and the uppermost places at entertainments;
40 Suna ƙwace gidajen gwauraye, kuma don nuna iyawa, sukan yi dogayen addu’o’i. Irin mutanen nan, za su sha hukunci mai tsanani sosai.”
who devour the families of widows, and use long prayers for a disguise. They shall undergo the severest punishment.
41 Yesu ya zauna ɗaura da inda ake bayarwa, ya kuma dubi yadda taron suke sa kuɗinsu a cikin ɗakunan ajiya haikali. Masu arziki da yawa suka zuba kuɗaɗe masu yawa.
And Jesus sitting opposite the treasury, observed the people throwing money into the treasury; and many rich persons put in much.
42 Amma wata matalauciya gwauruwa, ta zo ta saka anini biyu, da suka yi daidai da rabin kobo.
Then the poor widow came, who threw in two mites, (which make a farthing.)
43 Yesu ya kira almajiransa wurinsa ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, abin da matalauciya gwauruwan nan ta zuba cikin ɗakunan ajiya nan ya fi na sauran dukan.
Jesus having called his disciples, said to them, Indeed, I say to you, that this poor widow has given more than any of those who have thrown into the treasury;
44 Dukansu sun bayar ne daga cikin arzikinsu; ita kuwa, daga cikin talaucinta, ta ba da kome, duk abin da take da shi na rayuwa.”
for they all have contributed out of their superfluous stores; whereas she has given all the little she had--her whole living.