< Markus 12 >

1 Sa’an nan ya fara yi musu magana da misalai ya ce, “Wani mutum ya shuka gonar inabi. Ya kewaye ta da katanga, ya haƙa rami domin matsin inabin, ya kuma gina ɗakin gadi. Sai ya ba wa waɗansu manoma hayar gonar inabin, sa’an nan ya yi tafiya.
And he began to speak to them in parables: A man planted a vineyard, and set a hedge around it, and digged a wine-press, and built a tower, and let it out to vine-dressers, and went into another country.
2 Da lokacin girbi ya yi, sai ya aiki wani bawa wajen’yan hayan, don yă karɓo masa’ya’yan inabin daga wurinsu.
And at the proper time, he sent a servant to the vine-dressers, that he might receive from the vine-dressers of the fruit of the vineyard.
3 Amma suka kama shi, suka yi masa dūka, suka kore shi hannun wofi.
And they took him and scourged him, and sent him away without any thing.
4 Sai ya sāke aikan wani bawa wurinsu, amma suka bugi wannan mutum a kai, suka wulaƙanta shi.
And again he sent to them another servant; and at him they threw stones, and wounded him in the head, and sent him away shamefully treated.
5 Har yanzu ya sāke aikan wani. Wannan kuwa suka kashe. Ya aika waɗansu da yawa; suka bubbuge waɗansu, sauran kuwa suka kashe.
And again he sent another; and him they killed. And he sent many others, some of whom they scourged, and some they killed.
6 “Sauran mutum ɗaya da ya rage ya aika, ɗa, da yake ƙauna. Daga ƙarshe sai ya aike shi, yana cewa, ‘Za su girmama ɗana.’
Therefore, having yet one son, his beloved, he sent him also to them last, saying, They will reverence my son.
7 “Amma’yan hayan suka ce wa juna, ‘Aha! Wannan shi ne magājin. Ku zo mu kashe shi, gādon kuma yă zama namu.’
But those vine-dressers said one to another, This is the heir; come, let us kill him, and the inheritance will be ours.
8 Sai suka kama shi suka kashe, suka jefa shi bayan gonar inabin.
And they took him, and killed him, and threw him out of the vineyard.
9 “To, me, mai gonar inabin zai yi ke nan? Zai zo yă karkashe dukan’yan hayan nan, ya kuma ba wa waɗansu gonar inabin.
What, then, will the owner of the vineyard do? He will come and destroy those vine-dressers, and give his vineyard to others.
10 Ba ku taɓa karanta wannan Nassi ba, “‘Dutsen da magina suka ƙi, shi ne kuwa ya zama dutsen kusurwan gini.
Have you not read this scripture: The stone which the builders rejected has become the head of the corner;
11 Ubangiji ya yi wannan, ya kuma yi kyau a idanunmu’?”
this was from the Lord, and it is wondrous in our eyes?
12 Sai manyan Firistoci da malaman dokoki da shugabanni suka nemi hanyar da za su kama shi, domin sun gane ya yi misalin a kansu ne. Amma suka ji tsoron taron, saboda haka suka bar shi suka yi tafiyarsu.
And they sought to take him, but feared the multitude; for they knew that he had spoken the parable against them; and they left him, and went away.
13 Daga baya, sai suka tura waɗansu Farisiyawa da mutanen Hiridus zuwa wurin Yesu, domin su sa masa tarko a cikin maganarsa.
And they sent to him some of the Pharisees and of the Herodians, that they might entrap him in his words.
14 Suka zo wurinsa suka ce, “Malam, mun san kai mutum ne mai mutunci. Ba ka bin ra’ayin mutane, don ba ka nuna bambanci. Amma kana koyar da hanyar Allah bisa ga gaskiya. Daidai ne a biya wa Kaisar haraji, ko babu?
And they came and said to him: Teacher, we know that you are true, and that you care for no one; for you do not regard the person of men, but teach the way of God in truth. Is it lawful to give tribute to Cæsar, or not?
15 Mu biya ko kada mu biya?” Amma Yesu ya san munafuncinsu, sai ya yi tambaya ya ce, “Don me kuke ƙoƙarin sa mini tarko? Ku kawo mini dinari in ga.”
Must we give, or must we not give? But, knowing their hypocrisy, he said to them: Why do you tempt me? Bring me a denarius, that I may see it.
16 Suka kawo masa kuɗin, sai ya tambaye, su ya ce, “Hoton wane ne wannan? Kuma rubutun wane ne wannan?” Suka ce, “Na Kaisar.”
They brought it; and he said to them: Whose image and superscription is this? They said to him: Cæsar’s.
17 Sai Yesu ya ce musu, “Ku ba wa Kaisar abin da yake na Kaisar, ku ba wa Allah kuma abin da yake na Allah.” Suka yi mamakinsa ƙwarai.
And Jesus answered and said to them: Give to Cæsar the things that are Cæsar’s, and to God the things that are God’s. And they were astonished at him.
18 Sa’an nan Sadukiyawa da suke cewa, babu tashin matattu, suka zo masa da tambaya.
And the Sadducees, who say that there is no resurrection, came to him, and put a question to him, saying:
19 Suka ce, “Malam, Musa ya rubuta mana cewa, in ɗan’uwan wani mutum ya mutu, ya bar mata babu’ya’ya, dole mutumin ya auri gwauruwar, yă kuma samo wa ɗan’uwansa’ya’ya.
Teacher, Moses wrote for us, If any man’s brother die, and leave a wife, and leave no children, his brother shall take his wife, and raise up children for his brother.
20 To, an yi waɗansu’yan’uwa guda bakwai. Na fari ya yi aure, ya mutu babu’ya’ya.
Now there were seven brothers; and the first took a wife, and dying, left no child;
21 Na biyun ya auri gwauruwar, sai shi ma ya mutu, babu’ya’ya. Haka kuma na ukun.
and the second took her, and he died, and left no child; and the third, likewise;
22 A gaskiya, ba ko ɗaya daga cikin bakwai ɗin da ya bar’ya’ya. Daga ƙarshe, macen ta mutu.
and the seven took her, and left no child. Last of all, the woman also died.
23 To, a tashin matattu, matar wa za tă zama, don duk su bakwai nan sun aure ta?”
Therefore, in the resurrection, when they rise, of which of them shall she be the wife? for the seven had her as a wife.
24 Yesu ya ce, “Ashe, ba a cikin kuskure kuke ba saboda rashin sanin Nassi, ko ikon Allah?
And Jesus answered and said to them: Do you not err for this reason, because you know not the scriptures, nor the power of God?
25 Sa’ad da matattu suka tashi, ba za su yi aure ba, ba kuwa za a ba da su ga aure ba. Za su zama kamar yadda mala’iku suke a cikin sama.
For when they rise from the dead, they neither marry, nor are given in marriage, but are as the angels in heaven.
26 Game da tashin matattu kuwa, ashe, ba ku karanta a cikin littafin Musa ba, game da labarin ɗan kurmin nan mai cin wuta da Musa ya gani a jeji, yadda Allah ya yi magana da shi ya ce, ‘Ni ne Allah na Ibrahim, Allah na Ishaku da kuma Allah na Yaƙub’?
But concerning the dead, that they do rise, have you not read in the book of Moses, at The Bush, how God spoke to him, saying, I am the God of Abraham, and the God of Isaac, and the God of Jacob?
27 Shi ba Allah na matattu ba ne, shi Allah na masu rai ne. Kun yi mummunan kuskure!”
He is not the God of the dead, but of the living. Therefore, you do greatly err.
28 Wani daga cikin malaman dokoki ya zo ya ji suna muhawwara. Da ya lura cewa Yesu ya amsa musu daidai, sai ya tambaye shi ya ce, “A cikin dukan dokoki, wacce ta fi girma duka?”
And one of the scribes came, and heard them reasoning together; and perceiving that he had answered them well, he asked him: Which is the first commandment of all?
29 Yesu ya ce, “Wadda ta fi girma duka, ita ce wannan. ‘Ku saurara, ya Isra’ila, Ubangiji Allahnmu, Ubangiji ɗaya ne.
And Jesus answered him: The first commandment of all is, Hear, O Israel, the Lord our God is one Lord.
30 Ka ƙaunaci Ubangiji Allahnka da dukan zuciyarka, da dukan ranka, da dukan hankalinka, da kuma dukan ƙarfinka.’
And you shall love the Lord your God with your whole heart, and with your whole soul, and with your whole mind, and with your whole strength. This is the first commandment.
31 Na biyun ita ce, ‘Ka ƙaunaci maƙwabcinka kamar kanka.’Ba wata doka da ta fi waɗannan.”
And the second, which is like it, is this: You shall love your neighbor as yourself. There is no other commandment greater than these.
32 Mutumin ya ce, “Malam, ka faɗi daidai. Daidai ne da ka ce, Allah ɗaya ne, babu kuma wani sai shi.
And the scribe said to him: Teacher, in truth you have well said, that there is one God, and there is no other beside him;
33 Nuna ƙauna ga Allah da dukan zuciyarka, da dukan ganewarka, da dukan ƙarfinka, da kuma nuna ƙauna ga maƙwabcinka kamar kanka, ya fi dukan hadayun ƙonawa da sadakoki.”
and to love him with the whole heart, and with the whole understanding, and with the whole soul, and with the whole strength, and to love one’s neighbor as himself, is more than all whole burnt-offerings and sacrifices.
34 Da Yesu ya ga ya amsa da hikima, sai ya ce masa, “Ba ka da nisa da mulkin Allah.” Daga lokacin, ba wanda ya yi karambani yin masa wata tambaya.
And Jesus perceiving that he answered with understanding, said to him: You are not far from the kingdom of God. And no one, after that, ventured to ask him a question.
35 Yayinda Yesu yake koyarwa a filin haikalin, sai ya yi tambaya ya ce, “Yaya malaman dokoki suke cewa Kiristi ɗan Dawuda ne?
And Jesus, as he was teaching in the temple, answered and said: How say the scribes that the Christ is the son of David?
36 Dawuda da kansa ya yi magana ta wurin Ruhu Mai Tsarki ya ce, “‘Ubangiji ya ce wa Ubangijina, “Zauna a hannun damana sai na sa abokan gābanka a ƙarƙashin sawunka.”’
For David himself said by the Holy Spirit: The Lord said to my Lord, Sit at my right hand, till I make thy enemies thy footstool.
37 Dawuda da kansa ya kira shi ‘Ubangiji.’ To, ta yaya zai zama ɗansa?” Taro mai yawa suka saurare shi da murna.
David himself, then, calls him Lord; and how is he his son? And the great multitude heard him with pleasure.
38 Sa’ad da Yesu yake koyarwa ya ce, “Ku lura da malaman dokoki. Sukan so yin tafiya a manyan riguna, a kuma dinga gaishe su a wuraren kasuwanci.
And he said to them in his teaching: Beware of the scribes, who love to walk in robes, and love salutations in the markets,
39 Sukan kuma nemi wuraren zama mafi daraja a majami’u, da kuma wuraren zaman manya a bukukkuwa.
and the first seats in the synagogues, and the first places at suppers;
40 Suna ƙwace gidajen gwauraye, kuma don nuna iyawa, sukan yi dogayen addu’o’i. Irin mutanen nan, za su sha hukunci mai tsanani sosai.”
who eat up the houses of widows, and, as a pretext, make long prayers: these shall receive more abundant condemnation.
41 Yesu ya zauna ɗaura da inda ake bayarwa, ya kuma dubi yadda taron suke sa kuɗinsu a cikin ɗakunan ajiya haikali. Masu arziki da yawa suka zuba kuɗaɗe masu yawa.
And Jesus, sitting opposite the treasury, observed how the multitude threw money into the treasury. And many rich persons threw in much.
42 Amma wata matalauciya gwauruwa, ta zo ta saka anini biyu, da suka yi daidai da rabin kobo.
And there came one poor widow, and she threw in two mites, which make a farthing.
43 Yesu ya kira almajiransa wurinsa ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, abin da matalauciya gwauruwan nan ta zuba cikin ɗakunan ajiya nan ya fi na sauran dukan.
And he called his disciples to him, and said to them: Verily I say to you, this poor widow has thrown in more than all that have thrown into the treasury.
44 Dukansu sun bayar ne daga cikin arzikinsu; ita kuwa, daga cikin talaucinta, ta ba da kome, duk abin da take da shi na rayuwa.”
For all have thrown in out of their abundance; but she, out of her poverty, has thrown in all that she had, her whole living.

< Markus 12 >