< Markus 10 >
1 Sai Yesu ya tashi daga nan ya tafi yankin Yahudiya, da kuma ƙetaren Urdun. Taron mutane suka sāke zuwa wurinsa, ya kuma koya musu kamar yadda ya saba.
UYesu akavuuka iluta ku kighavo ikya Yudea, kukilila imwambo ija kikogha kya Yolidani. Amapugha gha vaanhu ghakava ghiluta kange kwa mwene, pe akavavulanisyagha ndavule lwale lwiho lwake.
2 Waɗansu Farisiyawa suka zo suka gwada shi, ta wurin yin masa tambaya cewa, “Daidai ne bisa ga doka, mutum yă saki matarsa?”
Pepano aVafalisayi vamonga vakaluta kukumughela, vakamposia vakati, “Asi, lukwitikisivua mu ndaghilo siitu umughoosi kukuntavula un'dala ghwake?”
3 Ya amsa ya ce, “Me Musa ya umarce ku?”
UYesu akavaposia akati, “UMoose alyavalaghilike kiki?”
4 Suka ce, “Musa ya ba da izini mutum yă rubuta takardar saki, yă kuma kore ta.”
Vakamwamula vakati, “UMoose alyitikisie kulemba ikalata ija kutavula un'dala na kukumuleka
5 Yesu ya ce, “Saboda taurin kanku ne, Musa ya rubuta muku wannan doka.
UYesu akavavuula akati, “UMoose alyavalembiile ululaghilo uluo, ulwakuva namupulika mu sino muvulanisivua.
6 Amma a farkon halitta, Allah ya ‘halicce su miji da mace.’
Kuhuma uNguluve ipela iisi, “Alyapelile umughoosi nu n'dala.'
7 ‘Saboda wannan dalili, mutum zai bar mahaifinsa da mahaifiyarsa, yă manne wa matarsa,
Mu uluo umuunhu ikumuleka uviise nu ng'ina, neke ivisagha nu n'dala ghwake,
8 su biyun kuma za su zama jiki ɗaya.’Saboda haka, su ba mutum biyu ba ne, amma mutum ɗaya.
vavili ava viiva m'bili ghumo.' Apuo naviiva vavili kange, looli viiva m'bili ghumo.
9 Domin haka, abin da Allah ya haɗa, kada mutum yă raba.”
Lino, kino uNguluve alungile, umuunhu nangalekanisyaghe.”
10 Da suna cikin gida kuma, sai almajiran suka tambayi Yesu game da wannan.
Ye vingiile kange mu nyumba, avavulanisivua vaake vakamposia imhola ija lisio ilio.
11 Ya amsa ya ce, “Duk wanda ya saki matarsa, ya auri wata, yana da laifin aikata zina a kan matar da ya saki.
UYesu akavamula akati, “'Umuunhu ghweni juno itavula un'dala na kutoola ujunge, iiva m'bwafu amhokile un'dala ghwake untasi.
12 In kuma ta saki mijinta ta auri wani, ta yi zina ke nan.”
Ghwope un'dala angamuleke umughoosi na kutolua kwa junge, ghwope iiva m'bwafu.”
13 Mutane suka kawo ƙananan yara wurin Yesu don yă taɓa su, amma almajiran suka kwaɓe su.
Avaanhu vakamuletela uYesu avaana avadebe avabasie kuuti avafuunye, neke avavulanisivua vaake vakavadalikila avaanhu vala.
14 Da Yesu ya ga haka, sai ya yi fushi, ya ce musu, “Ku bar yara ƙanana su zo wurina, kada ku hana su, gama mulkin Allah na irin waɗannan ne.
UYesu ye aluvwene uluo, akakalala, akavavuula avavuulanisivua vaake akati, “Muvaleke avaana avadebe visaghe kulyune. namungavasighaghe' ulwakuva uvutwa vwa Nguluve vwa vaanhu vano vali ndavule avaana ava.
15 Gaskiya nake gaya muku, duk wanda bai karɓi mulkin Allah kamar ƙaramin yaro ba, ba zai taɓa shiga mulkin ba.”
Kyang'haani nikuvavuula niiti, umuunhu ghweni juno naikumwitika uNguluve ndavule umwana un'debe, naalingila mu vutwa vwa Nguluve.”
16 Sai ya ɗauki yaran a hannuwansa, ya ɗibiya musu hannuwansa, ya kuma albarkace su.
Pe akava ikuvaghumbatila avaana vala, akaviika amavoko ghaake pa veene kukuvafuunya.
17 Da Yesu ya kama hanya, sai wani mutum ya ruga da gudu ya zo wajensa, ya durƙusa a gabansa ya ce, “Malam nagari, me zan yi domin in gāji rai madawwami?” (aiōnios )
UYesu ye ivuuka iluta, umuunhu jumonga akiisa luvilo, akafughama pa mwene Yesu, akamposia akati, “Ghwe M'bulanisi ghwe nnofu, nivombe kiki neke niive nu vwumi uvwa kuvusila kusila?” (aiōnios )
18 Yesu ya amsa ya ce, “Don me kake ce da ni mai nagarta? Ai, ba wani nagari, sai Allah kaɗai.
UYesu akamwamula akati, “Kki kukunhambula kuuti nili nnofu? Nakwale unnofu, looli ju Nguluve mwene.
19 Ka san dokokin da suka ce, ‘Kada ka yi kisankai, kada ka yi zina, kada ka yi sata, kada ka ba da shaida ta ƙarya, kada ka cuci wani, ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka.’”
Usimanyile indaghilo isa Nguluve:' Nungabudaghe, nungavwafukaghe, nungahijaghe, nungolekaghe isa vudesi, nungasyangaghe, umwoghopaghe, umwoghopaghe uvaaso nu mamaajo.”
20 Mutumin ya ce, “Malam, ai, tun ina yaro na kiyaye duk waɗannan.”
Umuunhu jula akamwamula akati'”M'bulanisi, isio sooni nisigadiliile kuhuma uvwana vwango.”
21 Yesu ya kalle shi da ƙauna ya ce, “Abu ɗaya ka rasa, ka tafi ka sayar da duk abin da kake da shi, ka ba wa matalauta, za ka kuwa sami dukiya a sama. Sa’an nan ka zo ka bi ni.”
UYesu akamulola, akamughana, akam'buula akati, “Ghwaghilue ikiinu kimo. Ulute ughusie fyoni fino uli nafyo, neke indalama sino upatile uvapeele avakotofu. Apuo pe ghuuva ni kyuma kukyanya. Pepan ghwisaghe umbingililaghe.”
22 Da jin wannan, sai mutumin ya ɓata fuskarsa, ya tafi da baƙin ciki, gama yana da arziki sosai.
Umuunhu jula ye apuliike isio, akiluka ku maaso, akavuuka asukuniile, ulwakuva akasaghagha ulwa kutavula ikyuma kyake kino kyale kinga.
23 Yesu ya dudduba, sai ya ce wa almajiransa, “Yana da wuya fa masu arziki su shiga mulkin Allah!”
UYesu akalola imbale sooni, akavavuula avavulanisivua vaake akati, “LUtalamu kyongo avanya kyuma kukwingila mu vutwa vwa Nguluve!”
24 Almajiransa suka yi mamakin kalmominsa. Amma Yesu ya sāke ce musu, “’Ya’yana, yana da wuya fa a shiga mulkin Allah!
Avavulanisivua vakadegha amasioghaake. UYesu akavavuula kange akati, “Vanango, lutalamu kyongo kukwingilila ku vutwa vwa Nguluve!
25 Ya fi sauƙi raƙumi yă shiga ta kafar allura, da mai arziki yă shiga mulkin Allah.”
Kihuugu ingamila pikila pa kalyoli ka honelo, Kkila ummofu kukwingila mu vutwa vwa Nguluve”
26 Almajiran suka yi mamaki ƙwarai, suka ce wa juna, “To, wa zai sami ceto ke nan?”
Avavulanisivua vaake vakadegha kyogo, vakiposania vakati, “Pe veeni lino juno anoghiile kupokua?
27 Yesu ya kalle su ya ce, “Ga mutum kam, wannan ba mai yiwuwa ba ne, amma ga Allah, wannan mai yiwuwa ne; dukan abubuwa masu yiwuwa ne ga Allah.”
UYesu akavalola akati, “Ku vaannhu lutalamu, neke kwa Nguluve sooni sivombeka.”
28 Bitrus ya ce, “Mun bar kome domin mu bi ka!”
Upeteli akam'buula akati, “loola, usue tufilekile fyoni, tutukuvingilila uve.”
29 Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, babu wanda zai bar gida, ko’yan’uwa maza da mata, ko mahaifiya, ko mahaifi, ko’ya’ya, ko gonaki saboda ni, da kuma bishara,
UYesu akati, Kyang'haani nikuvavuula, umuunhu juno ajilekile inyumba, nambe avanine, nambe avalumbu, nambe ung'ina, nambe uviise, nambe avaana, nambe amaghunda vwimila une ni Mhola iNofu,
30 sa’an nan yă kāsa samun ninkinsu ɗari a zamanin yanzu (na gidaje, da’yan’uwa mata, da’yan’uwa maza, da uwaye, da’ya’ya, da gonaki amma tare da tsanani) a lahira kuma yă sami rai madawwami. (aiōn , aiōnios )
ujuo mu masiki agha pelua figha kukila fino afilekile. pelua inyumba, avanine, na valumbu, nu ng'ina na vaana na maghunda. Nasi mhumuko sikumwaghagha. Kange unsiki ghuno ghukwisa alapelua uvwumi uvwa kuvusila kusila. (aiōn , aiōnios )
31 Amma da yawa da suke na farko, za su zama na ƙarshe, na ƙarshe kuma, za su zama na farko.”
Neke vinga vano va kwanda valaaava va vusililo, ava vusililo valaava vakwanda.
32 Suna haurawa a hanyarsu zuwa Urushalima ke nan, Yesu yana a gaba, almajiran suna bin sa suna mamaki, waɗanda suke bi kuma suna ji tsoro. Ya sāke kai Sha Biyun nan gefe, ya gaya musu abin da zai faru da shi.
UYesu na vavulanisivua vaake valyale mu sila vifiluta ku Yelusalemu. UYesu akava ikuvalongolela. Avavulanisua vaake vakadegha, nava vaanhu vano vakavigisaniagha vakoghopa. Pepano UYesu akavatoola kange vala kjigho na vavili, akaluta navoope palubale, akatengula pikuvavuula sino kyaivombelua.
33 Ya ce, “Za mu haura zuwa Urushalima, za a bashe Ɗan Mutum, ga manyan firistoci da malaman dokoki. Za su yi masa hukuncin kisa, a kuma ba da shi ga Al’ummai,
Akati, “Lolagha! Taluta ku Yelusalemu, ukuo une ne Mwa ghwa Muunhu niluta Kukwohehelua ku vavaha va vatekesi na vavulanisi va ndaghilo. Aveene kyavikuhigha kuuti nibududue. kange kyavikumbiika mu mavoko gha vano na Vayahudii,
34 waɗanda za su yi masa ba’a, su tofa masa miyau, su yi masa bulala, su kuma kashe shi. Bayan kwana uku kuma yă tashi.”
voope vikunyovelegha, vikufunyilagha amati, vikung'hopagha ni mijeledi na kukumbunda. neke ikighono ikya vutatu nisyuka.
35 Sai Yaƙub da Yohanna,’ya’yan Zebedi maza suka zo wurinsa suka ce, “Malam, muna so ka yi mana duk abin da muka roƙa.”
Pepano avakina Sebedaayi uYakovo nu Yohani, vakaluta kwa yesu vakati, “m'bulanisi, tusuuma utuvombele luno tulodonda.”
36 Ya tambaye su ya ce, “Me kuke so in yi muku?”
UYesu akavaposia akati, “Mulonda nivavombele kiki?
37 Suka amsa suka ce, “Ka bar ɗayanmu yă zauna a damarka, ɗayan kuma a hagunka, a cikin ɗaukakarka.”
Vakamwamula vakati, “Ghuliiva ghutema mu vuvaha vwako, tusuuma na jusue tuvisaghe nuuvu, jumo ilake ulubale lwako ilwa kundio, ujunge ulwa kung'highi.”
38 Yesu ya ce, “Ba ku san abin da kuke roƙo ba. Za ku iya shan kwaf da zan sha, ko a yi muku baftisma da baftismar da aka yi mini?”
UYesu akavavuula akati, “Namukagwile luno musuuma. Ndepoonu mutavwile ulwa vufue luno nikwofughua une?”
39 Suka ce, “Za mu iya.” Yesu ya ce musu, “Za ku sha kwaf da zan sha, a kuma yi muku baftisma da aka yi mini,
Vakamwamula vakati, “Eena, tunoghiliile.” UYesu akavavuula akati, “Isila ija lupumuko jino nikilila une.
40 amma zama a damana ko haguna, ba ni nake ba da izinin ba. Waɗannan wurare na waɗanda aka riga aka shirya musu ne.”
Neke kukuvapeela kuuva nuune mu vuvaha vwago, jumo kundio jughe kung'highi kulyune, navutavulilua vwango. Looli uNhaata ghwango ghwe juno alavapeela vano avaling'hanikisie ng'haani.”
41 Da sauran goman suka ji wannan, sai suka yi fushi da Yaƙub da Yohanna.
Avavulanisivua avange kijigho ye vapuliike iso, vatatengula kukunkalalila uYakovo nu Yohani.
42 Yesu ya kira su ya ce musu, “Kun sani waɗanda aka san su da mulkin al’ummai sukan nuna musu iko, hakimansu ma sukan gasa musu iko.
Pepano u Yesu akavakemeela vooni, akavavuula akati, “Mukagwile kuuti avatwa va iisi vitema avaanhu vaave ni ngufu. kange vihufia ingufu isa vutavulilua vwave ku vavanda neke vavakundaghe mu sooni.
43 Ba haka ya kamata yă zama da ku ba. A maimakon, duk wanda yake so yă zama babba a cikinku, dole yă zama bawanku.
Neke kulyumue nafye lungavisaghe. looli umuunhu juno ilonda kuuva m'baha ujuo avisaghe m'bombi ghwinu.
44 Duk wanda kuma yake so yă zama na farko, dole yă zama bawan kowa.
Naju muunhu juno ilonda kuuva mulongosi, avisaghe nkami ghwa vooni.
45 Gama ko Ɗan Mutum ma, bai zo domin a bauta masa ba, amma don yă yi bauta, yă kuma ba da ransa fansa saboda mutane da yawa.”
Na juune ne Mwana ghwa Muunhu nanilisile kuvombelua, looli nilisile kukuvavombela avange na kuhumia uvwumi vwango kuuti nivavange vinga.”
46 Sai suka iso Yeriko. Sa’ad da Yesu da almajiransa tare da taro mai yawa suke barin birnin, wani makaho da ake kira Bartimawus kuwa (wato, “ɗan Timawus”), yana zaune a gefen hanya yana bara.
Pepano uYesu na vavulanisivua vaake vakafika mu likaaja ilya Yeliko Pambele ye vihuma palikimo ni lipugha lya vaanhu mu likaaja ilio, vakamwagha um'bofu ujuo akasumagha ifiinu. Ikighono iko, alikalile palubale pa sila.
47 Da ya ji cewa Yesu Banazare ne, sai ya ɗaga murya, yana cewa, “Yesu Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai!”
Ye apuliike kuuti ghwe Yesu uMunasaleti ikila mu sila jila, akatengula pikemeela fiijo akati, “Ghwe Yesu Mwana ghwa David, usungukile!”
48 Mutane da yawa suka kwaɓe shi, suka ce yă yi shiru, amma ya ƙara ɗaga murya yana cewa, “Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai!”
Avaanhu vinga vakava vikun'dalikila na kukum'buula kuuti ajike, neke umwene akaghina kukemeela fiijo akati, “Ghwe mwana ghwa Dvidi, usungukile!”
49 Yesu ya tsaya ya ce, “Ku kira shi.” Sai suka kira makahon suka ce, “Ka yi farin ciki! Tashi tsaye! Yana kiranka.”
UYesu akiima akati, “Munkemeela um'bofu jula vakati, “Ghukangasasyaghe, ima, ikukukemeela.”
50 Ya jefar da mayafinsa waje ɗaya, ya yi wuf, ya zo wurin Yesu.
Pepano akataagha umwenda ghwake, akiimang'haning'haani iluta kwa Yesu.
51 Yesu ya tambaye shi ya ce, “Me kake so in yi maka?” Makahon ya ce, “Rabbi, ina so in sami ganin gari.”
UYesu akamposia akati, “Ghulonda nikuvombele kiki? Um'bofu jula akati, “M'bulanisi, nililonda nilolaghe.”
52 Yesu ya ce, “Je ka, bangaskiyarka ta warkar da kai.” Nan da nan, ya sami ganin gari, ya kuma bi Yesu suka tafi.
UYesu akam'buula akati, “Lutagha, usokile vwimila ulwitiko lwako.” Unsiki ghunghuo um'bofu jula akalolagha, kama'bingilila uYesu mu sila.