< Markus 10 >

1 Sai Yesu ya tashi daga nan ya tafi yankin Yahudiya, da kuma ƙetaren Urdun. Taron mutane suka sāke zuwa wurinsa, ya kuma koya musu kamar yadda ya saba.
Partant de là, il vint aux confins de la Judée, au-delà du Jourdain; et le peuple s’assembla de nouveau près de lui, et, selon sa coutume, il recommença à les instruire.
2 Waɗansu Farisiyawa suka zo suka gwada shi, ta wurin yin masa tambaya cewa, “Daidai ne bisa ga doka, mutum yă saki matarsa?”
Et les pharisiens s’approchant, lui demandèrent s’il est permis à un homme de renvoyer sa femme; c’était pour le tenter.
3 Ya amsa ya ce, “Me Musa ya umarce ku?”
Mais Jésus répondant, leur dit: Que vous a ordonné Moïse?
4 Suka ce, “Musa ya ba da izini mutum yă rubuta takardar saki, yă kuma kore ta.”
Ils répliquèrent: Moïse a permis d’écrire un acte de répudiation, et de la renvoyer.
5 Yesu ya ce, “Saboda taurin kanku ne, Musa ya rubuta muku wannan doka.
Jésus leur répondant, dit: C’est à cause de la dureté de votre cœur, qu’il vous a écrit ce précepte.
6 Amma a farkon halitta, Allah ya ‘halicce su miji da mace.’
Mais au commencement de la création, Dieu fit un homme et une femme.
7 ‘Saboda wannan dalili, mutum zai bar mahaifinsa da mahaifiyarsa, yă manne wa matarsa,
C’est pourquoi l’homme quittera son père et sa mère, et s’attachera à sa femme;
8 su biyun kuma za su zama jiki ɗaya.’Saboda haka, su ba mutum biyu ba ne, amma mutum ɗaya.
Et ils seront deux dans une seule chair. Ainsi ils ne sont plus deux, mais une seule chair.
9 Domin haka, abin da Allah ya haɗa, kada mutum yă raba.”
Ce que Dieu donc a uni, que l’homme ne le sépare point.
10 Da suna cikin gida kuma, sai almajiran suka tambayi Yesu game da wannan.
Dans la maison, ses disciples l’interrogèrent encore sur le même sujet.
11 Ya amsa ya ce, “Duk wanda ya saki matarsa, ya auri wata, yana da laifin aikata zina a kan matar da ya saki.
Et il leur dit: Quiconque renvoie sa femme et en épouse une autre, commet un adultère à l’égard de celle-là.
12 In kuma ta saki mijinta ta auri wani, ta yi zina ke nan.”
Et si une femme quitte son mari et en épouse un autre, elle se rend adultère.
13 Mutane suka kawo ƙananan yara wurin Yesu don yă taɓa su, amma almajiran suka kwaɓe su.
Cependant on lui présentait de petits enfants pour qu’il les touchât. Mais ses disciples menaçaient ceux qui les présentaient.
14 Da Yesu ya ga haka, sai ya yi fushi, ya ce musu, “Ku bar yara ƙanana su zo wurina, kada ku hana su, gama mulkin Allah na irin waɗannan ne.
Jésus, les voyant, fut indigné, et leur dit: Laissez ces petits enfants venir à moi, et ne les en empêchez point; car à de tels est le royaume de Dieu.
15 Gaskiya nake gaya muku, duk wanda bai karɓi mulkin Allah kamar ƙaramin yaro ba, ba zai taɓa shiga mulkin ba.”
En vérité, je vous le dis: Quiconque n’aura point reçu le royaume de Dieu comme un petit enfant, n’y entrera point.
16 Sai ya ɗauki yaran a hannuwansa, ya ɗibiya musu hannuwansa, ya kuma albarkace su.
Et les embrassant et imposant les mains sur eux, il les bénissait.
17 Da Yesu ya kama hanya, sai wani mutum ya ruga da gudu ya zo wajensa, ya durƙusa a gabansa ya ce, “Malam nagari, me zan yi domin in gāji rai madawwami?” (aiōnios g166)
Comme il se mettait en chemin, quelqu’un accourant et fléchissant le genou, lui demanda: Bon maître, que ferai-je pour avoir la vie éternelle? (aiōnios g166)
18 Yesu ya amsa ya ce, “Don me kake ce da ni mai nagarta? Ai, ba wani nagari, sai Allah kaɗai.
Jésus lui répondit: Pourquoi m’appelles-tu bon? Nul n’est bon, que Dieu seul.
19 Ka san dokokin da suka ce, ‘Kada ka yi kisankai, kada ka yi zina, kada ka yi sata, kada ka ba da shaida ta ƙarya, kada ka cuci wani, ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka.’”
Tu connais les commandements: Ne commets point d’adultère; ne tue point; ne dérobe point; ne rends point de faux témoignage; ne fais point de fraude; honore ton père et ta, mère.
20 Mutumin ya ce, “Malam, ai, tun ina yaro na kiyaye duk waɗannan.”
Mais le jeune homme reprenant la parole, lui dit: Maître, j’ai observé tous ces préceptes dès ma jeunesse.
21 Yesu ya kalle shi da ƙauna ya ce, “Abu ɗaya ka rasa, ka tafi ka sayar da duk abin da kake da shi, ka ba wa matalauta, za ka kuwa sami dukiya a sama. Sa’an nan ka zo ka bi ni.”
Jésus, l’ayant regardé, l’aima, et lui dit: Une seule chose te manque; va, vends tout ce que tu as, donne-le aux pauvres, et tu auras un trésor dans le ciel: puis viens et suis-moi.
22 Da jin wannan, sai mutumin ya ɓata fuskarsa, ya tafi da baƙin ciki, gama yana da arziki sosai.
Mais, affligé de cette parole, il s’en alla triste, car il avait de grands biens.
23 Yesu ya dudduba, sai ya ce wa almajiransa, “Yana da wuya fa masu arziki su shiga mulkin Allah!”
Alors Jésus regardant autour de lui, dit à ses disciples: Qu’il est difficile que ceux qui ont des richesses entrent dans le royaume de Dieu!
24 Almajiransa suka yi mamakin kalmominsa. Amma Yesu ya sāke ce musu, “’Ya’yana, yana da wuya fa a shiga mulkin Allah!
Or ses disciples étaient tout étonnés de ce discours; mais Jésus prenant de nouveau la parole, leur dit: Mes enfants bien-aimés, qu’il est difficile à ceux qui se confient dans les richesses, d’entrer dans le royaume de Dieu!
25 Ya fi sauƙi raƙumi yă shiga ta kafar allura, da mai arziki yă shiga mulkin Allah.”
Il est plus facile à un chameau de passer par le chas d’une aiguille, qu’à un riche d’entrer dans le royaume de Dieu.
26 Almajiran suka yi mamaki ƙwarai, suka ce wa juna, “To, wa zai sami ceto ke nan?”
Et ils demeuraient encore plus étonnés, se disant l’un à l’autre: Et qui peut donc être sauvé?
27 Yesu ya kalle su ya ce, “Ga mutum kam, wannan ba mai yiwuwa ba ne, amma ga Allah, wannan mai yiwuwa ne; dukan abubuwa masu yiwuwa ne ga Allah.”
Mais Jésus les regardant, dit: Aux hommes, cela est impossible, mais non pas à Dieu; car tout est possible à Dieu.
28 Bitrus ya ce, “Mun bar kome domin mu bi ka!”
Alors Pierre se mit à lui dire: Voici que nous avons, nous, tout quitté pour vous suivre;
29 Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, babu wanda zai bar gida, ko’yan’uwa maza da mata, ko mahaifiya, ko mahaifi, ko’ya’ya, ko gonaki saboda ni, da kuma bishara,
Jésus répondant, dit: En vérité, je vous le dis, nul n’aura quitté maison, ou frères, ou sœurs, ou père, ou mère, ou fils, ou terres à cause de moi et à cause de l’Evangile,
30 sa’an nan yă kāsa samun ninkinsu ɗari a zamanin yanzu (na gidaje, da’yan’uwa mata, da’yan’uwa maza, da uwaye, da’ya’ya, da gonaki amma tare da tsanani) a lahira kuma yă sami rai madawwami. (aiōn g165, aiōnios g166)
Qui ne reçoive maintenant, en ce temps même, cent fois autant de maisons, de frères, de sœurs, de mères, de fils et de terres, avec des persécutions, et, dans le siècle à venir, la vie éternelle. (aiōn g165, aiōnios g166)
31 Amma da yawa da suke na farko, za su zama na ƙarshe, na ƙarshe kuma, za su zama na farko.”
Mais beaucoup de premiers seront les derniers, et beaucoup de derniers, les premiers.
32 Suna haurawa a hanyarsu zuwa Urushalima ke nan, Yesu yana a gaba, almajiran suna bin sa suna mamaki, waɗanda suke bi kuma suna ji tsoro. Ya sāke kai Sha Biyun nan gefe, ya gaya musu abin da zai faru da shi.
Or ils étaient en chemin pour monter à Jérusalem; Jésus marchait devant eux, et ils en étaient tout étonnés, et ils le suivaient pleins de crainte. Et prenant encore à part les douze, il commença à leur dire ce qui devait lui arriver.
33 Ya ce, “Za mu haura zuwa Urushalima, za a bashe Ɗan Mutum, ga manyan firistoci da malaman dokoki. Za su yi masa hukuncin kisa, a kuma ba da shi ga Al’ummai,
Voilà que nous montons à Jérusalem, et le Fils de l’homme sera livré aux princes des prêtres, aux scribes et aux anciens; ils le condamneront à mort, et le livreront aux gentils;
34 waɗanda za su yi masa ba’a, su tofa masa miyau, su yi masa bulala, su kuma kashe shi. Bayan kwana uku kuma yă tashi.”
Et ils l’insulteront, cracheront sur lui, le flagelleront, et le tueront; et le troisième jour il ressuscitera.
35 Sai Yaƙub da Yohanna,’ya’yan Zebedi maza suka zo wurinsa suka ce, “Malam, muna so ka yi mana duk abin da muka roƙa.”
Alors s’approchèrent de lui Jacques et Jean, fils de Zébédée, disant: Maître, nous voudrions que tout ce que nous vous demanderons, vous le fissiez pour nous.
36 Ya tambaye su ya ce, “Me kuke so in yi muku?”
Mais il leur répondit: Que voulez-vous que je fasse pour vous?
37 Suka amsa suka ce, “Ka bar ɗayanmu yă zauna a damarka, ɗayan kuma a hagunka, a cikin ɗaukakarka.”
Et ils dirent: Accordez-nous que nous soyons assis l’un à votre droite et l’autre à votre gauche, dans votre gloire,
38 Yesu ya ce, “Ba ku san abin da kuke roƙo ba. Za ku iya shan kwaf da zan sha, ko a yi muku baftisma da baftismar da aka yi mini?”
Mais Jésus leur dit: Vous ne savez ce que vous demandez: pouvez-vous boire le calice que je bois, ou être baptisés du baptême dont je suis baptisé?
39 Suka ce, “Za mu iya.” Yesu ya ce musu, “Za ku sha kwaf da zan sha, a kuma yi muku baftisma da aka yi mini,
Ils lui répondirent: Nous le pouvons. Mais Jésus leur dit: À la vérité, le calice que je bois, vous le boirez, et vous serez baptisés du baptême dont je suis baptisé;
40 amma zama a damana ko haguna, ba ni nake ba da izinin ba. Waɗannan wurare na waɗanda aka riga aka shirya musu ne.”
Mais d’être assis à ma droite ou à ma gauche, il ne m’appartient pas de vous l’accorder à vous, mais à ceux à qui il a été préparé.
41 Da sauran goman suka ji wannan, sai suka yi fushi da Yaƙub da Yohanna.
Or, entendant cela, les dix s’indignèrent contre Jacques et Jean.
42 Yesu ya kira su ya ce musu, “Kun sani waɗanda aka san su da mulkin al’ummai sukan nuna musu iko, hakimansu ma sukan gasa musu iko.
Mais Jésus les appelant, dit: Vous savez que ceux qui passent pour régner sur les nations, les dominent, et que leurs princes ont puissance sur elles.
43 Ba haka ya kamata yă zama da ku ba. A maimakon, duk wanda yake so yă zama babba a cikinku, dole yă zama bawanku.
Il n’en est pas ainsi parmi vous; mais quiconque voudra devenir le plus grand, sera votre serviteur;
44 Duk wanda kuma yake so yă zama na farko, dole yă zama bawan kowa.
Et quiconque voudra être le premier parmi vous, sera le serviteur de tous.
45 Gama ko Ɗan Mutum ma, bai zo domin a bauta masa ba, amma don yă yi bauta, yă kuma ba da ransa fansa saboda mutane da yawa.”
Car le Fils de l’homme même n’est pas venu pour être servi, mais pour servir, et donner sa vie pour la rédemption d’un grand nombre.
46 Sai suka iso Yeriko. Sa’ad da Yesu da almajiransa tare da taro mai yawa suke barin birnin, wani makaho da ake kira Bartimawus kuwa (wato, “ɗan Timawus”), yana zaune a gefen hanya yana bara.
Ils vinrent ensuite à Jéricho; et comme il partait de Jéricho avec ses disciples et avec une grande multitude, le fils de Timée, Bartimée l’aveugle, qui était assis sur le bord du chemin, demandant l’aumône,
47 Da ya ji cewa Yesu Banazare ne, sai ya ɗaga murya, yana cewa, “Yesu Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai!”
Ayant entendu que c’était Jésus de Nazareth, se mit à crier, disant: Jésus, fils de David, ayez pitié de moi!
48 Mutane da yawa suka kwaɓe shi, suka ce yă yi shiru, amma ya ƙara ɗaga murya yana cewa, “Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai!”
Nombre de personnes le menaçaient pour le faire taire; mais lui criait beaucoup plus encore: Fils de David, ayez pitié de moi!
49 Yesu ya tsaya ya ce, “Ku kira shi.” Sai suka kira makahon suka ce, “Ka yi farin ciki! Tashi tsaye! Yana kiranka.”
Alors Jésus, s’arrêtant, ordonna qu’on l’appelât. On appela donc l’aveugle en lui disant: Aie confiance, lève-toi, il t’appelle.
50 Ya jefar da mayafinsa waje ɗaya, ya yi wuf, ya zo wurin Yesu.
Celui-ci, jetant son manteau, s’élança et vint à Jésus.
51 Yesu ya tambaye shi ya ce, “Me kake so in yi maka?” Makahon ya ce, “Rabbi, ina so in sami ganin gari.”
Et Jésus lui demanda: Que veux-tu que je te fasse? L’aveugle lui répondit: Maître, que je voie.
52 Yesu ya ce, “Je ka, bangaskiyarka ta warkar da kai.” Nan da nan, ya sami ganin gari, ya kuma bi Yesu suka tafi.
Va, lui dit Jésus, ta foi t’a guéri. Et aussitôt il vit, et il le suivait dans le chemin.

< Markus 10 >