< Markus 10 >

1 Sai Yesu ya tashi daga nan ya tafi yankin Yahudiya, da kuma ƙetaren Urdun. Taron mutane suka sāke zuwa wurinsa, ya kuma koya musu kamar yadda ya saba.
Jésus, étant parti de là, passa sur le territoire de la Judée, au-delà du Jourdain. La foule se rassembla encore auprès de lui, et, selon sa coutume, il se mit à l'instruire.
2 Waɗansu Farisiyawa suka zo suka gwada shi, ta wurin yin masa tambaya cewa, “Daidai ne bisa ga doka, mutum yă saki matarsa?”
Alors les pharisiens s'approchèrent et lui demandèrent, pour le mettre à l'épreuve: Est-il permis à un homme de répudier sa femme?
3 Ya amsa ya ce, “Me Musa ya umarce ku?”
Il leur répondit: Qu'est-ce que Moïse vous a commandé?
4 Suka ce, “Musa ya ba da izini mutum yă rubuta takardar saki, yă kuma kore ta.”
Ils lui dirent: Moïse a permis d'écrire une lettre de divorce et de répudier sa femme.
5 Yesu ya ce, “Saboda taurin kanku ne, Musa ya rubuta muku wannan doka.
Jésus leur répondit: C'est à cause de la dureté de votre coeur qu'il vous a donné ce commandement.
6 Amma a farkon halitta, Allah ya ‘halicce su miji da mace.’
Mais au commencement de la création. Dieu fit un homme et une femme,
7 ‘Saboda wannan dalili, mutum zai bar mahaifinsa da mahaifiyarsa, yă manne wa matarsa,
«C'est pourquoi, l'homme quittera son père et sa mère et s'attachera à sa femme;
8 su biyun kuma za su zama jiki ɗaya.’Saboda haka, su ba mutum biyu ba ne, amma mutum ɗaya.
et les deux ne feront qu'une seule chair.» Ainsi ils ne sont plus deux, mais une seule chair.
9 Domin haka, abin da Allah ya haɗa, kada mutum yă raba.”
Que l'homme ne sépare donc pas ce que Dieu a uni.
10 Da suna cikin gida kuma, sai almajiran suka tambayi Yesu game da wannan.
Lorsqu'ils furent dans la maison, les disciples l'interrogèrent encore sur ce sujet;
11 Ya amsa ya ce, “Duk wanda ya saki matarsa, ya auri wata, yana da laifin aikata zina a kan matar da ya saki.
et il leur dit: Quiconque répudie sa femme pour en épouser une autre commet un adultère envers elle;
12 In kuma ta saki mijinta ta auri wani, ta yi zina ke nan.”
et si une femme qui a quitté son mari en épouse un autre, elle commet un adultère.
13 Mutane suka kawo ƙananan yara wurin Yesu don yă taɓa su, amma almajiran suka kwaɓe su.
On lui présenta des petits enfants, afin qu'il les touchât; mais les disciples reprenaient ceux qui les présentaient.
14 Da Yesu ya ga haka, sai ya yi fushi, ya ce musu, “Ku bar yara ƙanana su zo wurina, kada ku hana su, gama mulkin Allah na irin waɗannan ne.
Jésus, voyant cela, en fut indigné, et il leur dit: Laissez venir à moi les petits enfants, et ne les en empêchez point; car le royaume de Dieu est pour ceux qui leur ressemblent.
15 Gaskiya nake gaya muku, duk wanda bai karɓi mulkin Allah kamar ƙaramin yaro ba, ba zai taɓa shiga mulkin ba.”
En vérité, je vous le déclare, quiconque ne recevra pas le royaume de Dieu comme un petit enfant, n'y entrera point.
16 Sai ya ɗauki yaran a hannuwansa, ya ɗibiya musu hannuwansa, ya kuma albarkace su.
Et, les ayant pria entre ses bras, il leur imposa les mains et les bénit.
17 Da Yesu ya kama hanya, sai wani mutum ya ruga da gudu ya zo wajensa, ya durƙusa a gabansa ya ce, “Malam nagari, me zan yi domin in gāji rai madawwami?” (aiōnios g166)
Comme il sortait pour se mettre en route, un homme accourut; et, se jetant à genoux devant lui, il lui demanda: Mon bon Maître, que dois-je faire pour hériter la vie éternelle? (aiōnios g166)
18 Yesu ya amsa ya ce, “Don me kake ce da ni mai nagarta? Ai, ba wani nagari, sai Allah kaɗai.
Jésus lui répondit: Pourquoi m'appelles-tu bon? Un seul est bon, c'est Dieu.
19 Ka san dokokin da suka ce, ‘Kada ka yi kisankai, kada ka yi zina, kada ka yi sata, kada ka ba da shaida ta ƙarya, kada ka cuci wani, ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka.’”
Tu connais les commandements: «Ne commets point d'adultère; ne tue pas; ne dérobe point; ne dis pas de faux témoignage; ne fais tort à personne; honore ton père et ta mère.»
20 Mutumin ya ce, “Malam, ai, tun ina yaro na kiyaye duk waɗannan.”
L'homme répondit: Maître, j'ai observé toutes ces choses dès ma jeunesse.
21 Yesu ya kalle shi da ƙauna ya ce, “Abu ɗaya ka rasa, ka tafi ka sayar da duk abin da kake da shi, ka ba wa matalauta, za ka kuwa sami dukiya a sama. Sa’an nan ka zo ka bi ni.”
Jésus, l'ayant regardé, l'aima, et il lui dit: Il te manque une chose. Va, vends tout ce que tu as, donne-le aux pauvres, et tu auras un trésor dans le ciel; puis, viens et suis-moi.
22 Da jin wannan, sai mutumin ya ɓata fuskarsa, ya tafi da baƙin ciki, gama yana da arziki sosai.
Mais cet homme fut affligé de cette parole, et il s'en alla tout triste; car il avait de grands biens.
23 Yesu ya dudduba, sai ya ce wa almajiransa, “Yana da wuya fa masu arziki su shiga mulkin Allah!”
Alors Jésus, regardant autour de lui, dit à ses disciples: Qu'il est difficile à ceux qui ont des richesses d'entrer dans le royaume de Dieu!
24 Almajiransa suka yi mamakin kalmominsa. Amma Yesu ya sāke ce musu, “’Ya’yana, yana da wuya fa a shiga mulkin Allah!
Ses disciples furent étonnés de ces paroles. Mais Jésus, reprenant, leur dit: Mes enfants, qu'il est difficile à ceux qui se confient dans les richesses d'entrer dans le royaume de Dieu!
25 Ya fi sauƙi raƙumi yă shiga ta kafar allura, da mai arziki yă shiga mulkin Allah.”
Il est plus facile à un chameau de passer par le trou de l'aiguille, qu'il ne l'est à un riche d'entrer dans le royaume de Dieu.
26 Almajiran suka yi mamaki ƙwarai, suka ce wa juna, “To, wa zai sami ceto ke nan?”
Ils furent encore plus étonnés, et ils se disaient l'un à l'autre: Et qui peut donc être sauvé?
27 Yesu ya kalle su ya ce, “Ga mutum kam, wannan ba mai yiwuwa ba ne, amma ga Allah, wannan mai yiwuwa ne; dukan abubuwa masu yiwuwa ne ga Allah.”
Jésus, les regardant, leur dit: Cela est impossible aux hommes, mais non pas à Dieu; car toutes choses sont possibles à Dieu.
28 Bitrus ya ce, “Mun bar kome domin mu bi ka!”
Pierre se mit à lui dire: Voici que nous avons tout quitté, et nous t'avons suivi!
29 Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, babu wanda zai bar gida, ko’yan’uwa maza da mata, ko mahaifiya, ko mahaifi, ko’ya’ya, ko gonaki saboda ni, da kuma bishara,
Jésus répondit: En vérité, je vous le déclare, de tous ceux qui ont quitté maison, ou frères, ou soeurs, ou père, ou mère, ou enfants, ou champs, à cause de moi et de l'Évangile,
30 sa’an nan yă kāsa samun ninkinsu ɗari a zamanin yanzu (na gidaje, da’yan’uwa mata, da’yan’uwa maza, da uwaye, da’ya’ya, da gonaki amma tare da tsanani) a lahira kuma yă sami rai madawwami. (aiōn g165, aiōnios g166)
il n'y en a pas un qui ne reçoive maintenant, dès le temps présent, cent fois davantage, des maisons, des frères, des soeurs, des mères, des enfants, et des champs, — avec des persécutions, — et, dans le siècle à venir, la vie éternelle. (aiōn g165, aiōnios g166)
31 Amma da yawa da suke na farko, za su zama na ƙarshe, na ƙarshe kuma, za su zama na farko.”
Mais plusieurs des premiers seront les derniers, et plusieurs des derniers seront les premiers.
32 Suna haurawa a hanyarsu zuwa Urushalima ke nan, Yesu yana a gaba, almajiran suna bin sa suna mamaki, waɗanda suke bi kuma suna ji tsoro. Ya sāke kai Sha Biyun nan gefe, ya gaya musu abin da zai faru da shi.
Ils étaient en chemin pour monter à Jérusalem, et Jésus marchait en avant; les disciples étaient saisis d'effroi, et la crainte s'était emparée de ceux qui le suivaient. Prenant encore avec lui les Douze, il se mit à leur dire ce qui devait lui arriver:
33 Ya ce, “Za mu haura zuwa Urushalima, za a bashe Ɗan Mutum, ga manyan firistoci da malaman dokoki. Za su yi masa hukuncin kisa, a kuma ba da shi ga Al’ummai,
Voici que nous montons à Jérusalem, et le Fils de l'homme sera livré aux principaux sacrificateurs et aux scribes; ils le condamneront à mort et le livreront aux Païens.
34 waɗanda za su yi masa ba’a, su tofa masa miyau, su yi masa bulala, su kuma kashe shi. Bayan kwana uku kuma yă tashi.”
On se moquera de lui, on crachera sur lui, on le battra de verges, et on le fera mourir; et trois jours après, il ressuscitera.
35 Sai Yaƙub da Yohanna,’ya’yan Zebedi maza suka zo wurinsa suka ce, “Malam, muna so ka yi mana duk abin da muka roƙa.”
Alors Jacques et Jean, les fils de Zébédée, s'approchèrent de Jésus et lui dirent: Maître, nous voudrions que tu fisses pour nous ce que nous te demanderons.
36 Ya tambaye su ya ce, “Me kuke so in yi muku?”
Il leur répliqua: Que voulez-vous que je fasse pour vous?
37 Suka amsa suka ce, “Ka bar ɗayanmu yă zauna a damarka, ɗayan kuma a hagunka, a cikin ɗaukakarka.”
Ils lui répondirent: Accorde-nous d'être assis dans ta gloire, l'un à ta droite, l'autre à ta gauche.
38 Yesu ya ce, “Ba ku san abin da kuke roƙo ba. Za ku iya shan kwaf da zan sha, ko a yi muku baftisma da baftismar da aka yi mini?”
Mais Jésus leur dit: Vous ne savez ce que vous demandez. Pouvez-vous boire la coupe que je bois, et être baptisés du baptême dont je suis baptisé?
39 Suka ce, “Za mu iya.” Yesu ya ce musu, “Za ku sha kwaf da zan sha, a kuma yi muku baftisma da aka yi mini,
Ils lui répondirent: Nous le pouvons. Jésus leur dit: Vous boirez la coupe que je bois, et vous serez baptisés du baptême dont je suis baptisé;
40 amma zama a damana ko haguna, ba ni nake ba da izinin ba. Waɗannan wurare na waɗanda aka riga aka shirya musu ne.”
mais, quant à être assis à ma droite ou à ma gauche, il ne m'appartient pas de l'accorder: c'est pour ceux à qui cela est réservé.
41 Da sauran goman suka ji wannan, sai suka yi fushi da Yaƙub da Yohanna.
Les dix autres, qui avaient entendu cette demande, furent indignés contre Jacques et Jean.
42 Yesu ya kira su ya ce musu, “Kun sani waɗanda aka san su da mulkin al’ummai sukan nuna musu iko, hakimansu ma sukan gasa musu iko.
Mais Jésus, les ayant appelés, leur dit: Vous savez que ceux qui sont regardés comme les chefs des nations les asservissent, et que les grands les tiennent sous leur puissance.
43 Ba haka ya kamata yă zama da ku ba. A maimakon, duk wanda yake so yă zama babba a cikinku, dole yă zama bawanku.
Il n'en est pas ainsi parmi vous; au contraire, celui qui voudra être grand parmi vous, sera. votre serviteur;
44 Duk wanda kuma yake so yă zama na farko, dole yă zama bawan kowa.
et celui d'entre vous qui voudra être le premier, sera l'esclave de tous.
45 Gama ko Ɗan Mutum ma, bai zo domin a bauta masa ba, amma don yă yi bauta, yă kuma ba da ransa fansa saboda mutane da yawa.”
Car le Fils de l'homme est venu, non pour être servi, mais pour servir, et donner sa vie pour la rançon de plusieurs.
46 Sai suka iso Yeriko. Sa’ad da Yesu da almajiransa tare da taro mai yawa suke barin birnin, wani makaho da ake kira Bartimawus kuwa (wato, “ɗan Timawus”), yana zaune a gefen hanya yana bara.
Ensuite ils arrivèrent à Jérico. Comme Jésus en repartait avec ses disciples et une assez grande foule, un mendiant aveugle, Bartimée, le fils de Timée, était assis au bord du chemin.
47 Da ya ji cewa Yesu Banazare ne, sai ya ɗaga murya, yana cewa, “Yesu Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai!”
Ayant entendu dire que c'était Jésus de Nazareth, il se mit à crier et à dire: Fils de David, Jésus, aie pitié de moi!
48 Mutane da yawa suka kwaɓe shi, suka ce yă yi shiru, amma ya ƙara ɗaga murya yana cewa, “Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai!”
Plusieurs le reprenaient, pour le faire taire; mais il criait encore plus fort: Fils de David, aie pitié de moi!
49 Yesu ya tsaya ya ce, “Ku kira shi.” Sai suka kira makahon suka ce, “Ka yi farin ciki! Tashi tsaye! Yana kiranka.”
Jésus, s'étant arrêté, dit: Appelez-le. Ils appelèrent l'aveugle, en lui disant: Prends courage, lève-toi, il t'appelle.
50 Ya jefar da mayafinsa waje ɗaya, ya yi wuf, ya zo wurin Yesu.
Et jetant son manteau, il s'élança et vint vers Jésus.
51 Yesu ya tambaye shi ya ce, “Me kake so in yi maka?” Makahon ya ce, “Rabbi, ina so in sami ganin gari.”
Alors Jésus, prenant la parole, lui dit: Que veux-tu que je te fasse? L'aveugle lui répondit: Maître, que je recouvre la vue!
52 Yesu ya ce, “Je ka, bangaskiyarka ta warkar da kai.” Nan da nan, ya sami ganin gari, ya kuma bi Yesu suka tafi.
Jésus lui dit: Va, ta foi t'a guéri. Aussitôt l'aveugle recouvra la vue; et il suivait Jésus dans le chemin.

< Markus 10 >