< Markus 10 >

1 Sai Yesu ya tashi daga nan ya tafi yankin Yahudiya, da kuma ƙetaren Urdun. Taron mutane suka sāke zuwa wurinsa, ya kuma koya musu kamar yadda ya saba.
And, from thence, arising, he cometh into the bounds of Judaea and beyond the Jordan, —and there come together again, multitudes unto him, and, as he had been wont, again, was he teaching them.
2 Waɗansu Farisiyawa suka zo suka gwada shi, ta wurin yin masa tambaya cewa, “Daidai ne bisa ga doka, mutum yă saki matarsa?”
And Pharisees coming near were questioning him—whether it is allowed a husband to divorce a wife, testing him.
3 Ya amsa ya ce, “Me Musa ya umarce ku?”
But, he, answering, said unto them—What unto you did, Moses, command?
4 Suka ce, “Musa ya ba da izini mutum yă rubuta takardar saki, yă kuma kore ta.”
And, they, said—Moses permitted, to write, a roll of dismissal, and to divorce.
5 Yesu ya ce, “Saboda taurin kanku ne, Musa ya rubuta muku wannan doka.
But, Jesus, said unto them—In view of your hardness of heart, wrote he for you this commandment;
6 Amma a farkon halitta, Allah ya ‘halicce su miji da mace.’
But, from the beginning of creation, male and female, made he [them];
7 ‘Saboda wannan dalili, mutum zai bar mahaifinsa da mahaifiyarsa, yă manne wa matarsa,
For this cause, shall a man leave behind his father and mother,
8 su biyun kuma za su zama jiki ɗaya.’Saboda haka, su ba mutum biyu ba ne, amma mutum ɗaya.
and, the two, shall become, one flesh; so that, no longer, are they two, but, one flesh.
9 Domin haka, abin da Allah ya haɗa, kada mutum yă raba.”
What then, God, hath yoked together, let, a man, not put asunder.
10 Da suna cikin gida kuma, sai almajiran suka tambayi Yesu game da wannan.
And, [coming] into the house again, the disciples, concerning this, were questioning him;
11 Ya amsa ya ce, “Duk wanda ya saki matarsa, ya auri wata, yana da laifin aikata zina a kan matar da ya saki.
and he saith unto them—Whosoever shall divorce his wife, and marry another, committeth adultery against her;
12 In kuma ta saki mijinta ta auri wani, ta yi zina ke nan.”
And, if, she, divorcing her husband, marry another, she committeth adultery.
13 Mutane suka kawo ƙananan yara wurin Yesu don yă taɓa su, amma almajiran suka kwaɓe su.
And they were bringing unto him children, that he might, touch, them, —the disciples, however, were rebuking them.
14 Da Yesu ya ga haka, sai ya yi fushi, ya ce musu, “Ku bar yara ƙanana su zo wurina, kada ku hana su, gama mulkin Allah na irin waɗannan ne.
But Jesus, seeing it, was greatly displeased, and said unto them—Suffer the children to come unto me, —do not hinder them; for, of such, is the kingdom of God.
15 Gaskiya nake gaya muku, duk wanda bai karɓi mulkin Allah kamar ƙaramin yaro ba, ba zai taɓa shiga mulkin ba.”
Verily, I say unto you—Whosoever shall not welcome the kingdom of God, as a child, in nowise shall enter thereinto.
16 Sai ya ɗauki yaran a hannuwansa, ya ɗibiya musu hannuwansa, ya kuma albarkace su.
And, folding them in his arms, he was blessing them, having laid his hands upon them.
17 Da Yesu ya kama hanya, sai wani mutum ya ruga da gudu ya zo wajensa, ya durƙusa a gabansa ya ce, “Malam nagari, me zan yi domin in gāji rai madawwami?” (aiōnios g166)
And, as he was going forth into a road, one, running, and kneeling before him, was questioning him—Good Teacher! what shall I do that, life age—abiding, I may inherit? (aiōnios g166)
18 Yesu ya amsa ya ce, “Don me kake ce da ni mai nagarta? Ai, ba wani nagari, sai Allah kaɗai.
And, Jesus, said unto him—Why callest thou me, good? None, is good, save one—God.
19 Ka san dokokin da suka ce, ‘Kada ka yi kisankai, kada ka yi zina, kada ka yi sata, kada ka ba da shaida ta ƙarya, kada ka cuci wani, ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka.’”
The commandments, thou knowest, —Do not commit murder, Do not commit adultery, Do not steal; Do not bear false witness, Do not defraud, Honour thy father and mother.
20 Mutumin ya ce, “Malam, ai, tun ina yaro na kiyaye duk waɗannan.”
And, he, said unto him—Teacher! all these things, have I kept, from my youth.
21 Yesu ya kalle shi da ƙauna ya ce, “Abu ɗaya ka rasa, ka tafi ka sayar da duk abin da kake da shi, ka ba wa matalauta, za ka kuwa sami dukiya a sama. Sa’an nan ka zo ka bi ni.”
And, Jesus, looking at him, loved him, and said unto him—One thing, unto thee, is wanting; —Withdraw! whatsoever thou hast, sell, and give unto [the] destitute, —and thou shalt have treasure in heaven; and come! be following me.
22 Da jin wannan, sai mutumin ya ɓata fuskarsa, ya tafi da baƙin ciki, gama yana da arziki sosai.
And, he, becoming gloomy because of the word, departed sorrowing, for he was holding, many possessions.
23 Yesu ya dudduba, sai ya ce wa almajiransa, “Yana da wuya fa masu arziki su shiga mulkin Allah!”
And, looking around, Jesus saith unto his disciples—With what difficulty, shall, they who have money, enter, into the kingdom of God!
24 Almajiransa suka yi mamakin kalmominsa. Amma Yesu ya sāke ce musu, “’Ya’yana, yana da wuya fa a shiga mulkin Allah!
And, the disciples, were in amazement, because of the words. But, Jesus, again answering, saith unto them—Children! how difficult, it is, to enter, into the kingdom of God!
25 Ya fi sauƙi raƙumi yă shiga ta kafar allura, da mai arziki yă shiga mulkin Allah.”
It is, easier, for a camel, through the eye of a needle, to pass, than for, a rich man, into the kingdom of God, to enter.
26 Almajiran suka yi mamaki ƙwarai, suka ce wa juna, “To, wa zai sami ceto ke nan?”
And, they, were being exceedingly struck with astonishment, saying unto him—Who, then, can, be saved?
27 Yesu ya kalle su ya ce, “Ga mutum kam, wannan ba mai yiwuwa ba ne, amma ga Allah, wannan mai yiwuwa ne; dukan abubuwa masu yiwuwa ne ga Allah.”
Looking at them, Jesus saith—With men, impossible, but not, with God; for, all things, are possible, with God
28 Bitrus ya ce, “Mun bar kome domin mu bi ka!”
Peter began to be saying unto him—Lo! we, have left all, and followed thee!
29 Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, babu wanda zai bar gida, ko’yan’uwa maza da mata, ko mahaifiya, ko mahaifi, ko’ya’ya, ko gonaki saboda ni, da kuma bishara,
Jesus said—Verily, I say unto you—There is, no one, who hath left house, or brethren, or sisters, or mother, or father, or children, or lands, for the sake of me, and [for the sake of] the glad-message,
30 sa’an nan yă kāsa samun ninkinsu ɗari a zamanin yanzu (na gidaje, da’yan’uwa mata, da’yan’uwa maza, da uwaye, da’ya’ya, da gonaki amma tare da tsanani) a lahira kuma yă sami rai madawwami. (aiōn g165, aiōnios g166)
who shall not receive a hundredfold, now, in this season, houses, and brethren, and sisters, and mothers, and children, and lands, —with persecutions, and, in the age that is coming, life age-abiding. (aiōn g165, aiōnios g166)
31 Amma da yawa da suke na farko, za su zama na ƙarshe, na ƙarshe kuma, za su zama na farko.”
But, many, shall be—first-last, and [the] Last-first.
32 Suna haurawa a hanyarsu zuwa Urushalima ke nan, Yesu yana a gaba, almajiran suna bin sa suna mamaki, waɗanda suke bi kuma suna ji tsoro. Ya sāke kai Sha Biyun nan gefe, ya gaya musu abin da zai faru da shi.
Now they were in the way, going up unto Jerusalem, and Jesus was going on before them, —and they were in amazement; and, they who followed, were in fear. And, taking unto himself, again, the twelve, he began to be saying unto them, as to the things about to befall him—
33 Ya ce, “Za mu haura zuwa Urushalima, za a bashe Ɗan Mutum, ga manyan firistoci da malaman dokoki. Za su yi masa hukuncin kisa, a kuma ba da shi ga Al’ummai,
Lo! we are going up unto Jerusalem; and, the Son of Man, will be delivered up, unto the Chief-priests and the Scribes, —and they will condemn him to death, and deliver him up unto the nations;
34 waɗanda za su yi masa ba’a, su tofa masa miyau, su yi masa bulala, su kuma kashe shi. Bayan kwana uku kuma yă tashi.”
And they will mock him, and spit upon him, and scourge him, and, slay; —and, after three days, will he, arise.
35 Sai Yaƙub da Yohanna,’ya’yan Zebedi maza suka zo wurinsa suka ce, “Malam, muna so ka yi mana duk abin da muka roƙa.”
And there come near unto him, James and John, the [two] sons of Zebedee, —saying unto him—Teacher! we desire, that, whatsoever we shall ask thee, thou wilt do for us.
36 Ya tambaye su ya ce, “Me kuke so in yi muku?”
But, he, said unto them—What desire ye, I should do for you?
37 Suka amsa suka ce, “Ka bar ɗayanmu yă zauna a damarka, ɗayan kuma a hagunka, a cikin ɗaukakarka.”
And, they, said unto him—Grant us, that, one on thy right hand, and one on thy left, we may sit, in thy glory.
38 Yesu ya ce, “Ba ku san abin da kuke roƙo ba. Za ku iya shan kwaf da zan sha, ko a yi muku baftisma da baftismar da aka yi mini?”
But, Jesus, said unto them—Ye know not what ye are asking: Are ye able to drink the cup that, I, am to drink? or to be immersed, with the immersion wherewith, I, am to be immersed?
39 Suka ce, “Za mu iya.” Yesu ya ce musu, “Za ku sha kwaf da zan sha, a kuma yi muku baftisma da aka yi mini,
And, they, said unto him—We are able. And, Jesus, said unto them—The cup which, I, am to drink, ye shall drink, and, with the immersion wherewith, I, am to be immersed, shall ye be immersed;
40 amma zama a damana ko haguna, ba ni nake ba da izinin ba. Waɗannan wurare na waɗanda aka riga aka shirya musu ne.”
But, to sit on my right hand and on my left, is not mine to give, except unto them for whom it hath been prepared.
41 Da sauran goman suka ji wannan, sai suka yi fushi da Yaƙub da Yohanna.
And the ten, hearing, began to be sorely displeased, concerning James and John.
42 Yesu ya kira su ya ce musu, “Kun sani waɗanda aka san su da mulkin al’ummai sukan nuna musu iko, hakimansu ma sukan gasa musu iko.
And Jesus, calling them near, saith unto them—Ye know that, they who think to rule the nations, lord it over them, and, their great ones, wield authority over them;
43 Ba haka ya kamata yă zama da ku ba. A maimakon, duk wanda yake so yă zama babba a cikinku, dole yă zama bawanku.
But, not so, it is, among you. But, whosoever desireth to become, great, among you, shall be, your minister,
44 Duk wanda kuma yake so yă zama na farko, dole yă zama bawan kowa.
And, whosoever desireth, among you, to be, first, shall be, servant of all;
45 Gama ko Ɗan Mutum ma, bai zo domin a bauta masa ba, amma don yă yi bauta, yă kuma ba da ransa fansa saboda mutane da yawa.”
For, even the Son of Man, came not to be ministered unto, but minister, —and to give his life, a ransom instead of many.
46 Sai suka iso Yeriko. Sa’ad da Yesu da almajiransa tare da taro mai yawa suke barin birnin, wani makaho da ake kira Bartimawus kuwa (wato, “ɗan Timawus”), yana zaune a gefen hanya yana bara.
And they come into Jericho. And, as he was journeying forth from Jericho, and his disciples, and a considerable multitude, the son of Timaeus, blind Bar-Timaeus, a beggar, was sitting beside the road.
47 Da ya ji cewa Yesu Banazare ne, sai ya ɗaga murya, yana cewa, “Yesu Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai!”
And, hearing that it was, Jesus the Nazarene, he began to be crying aloud, and saying—O Son of David! Jesus! have mercy on me.
48 Mutane da yawa suka kwaɓe shi, suka ce yă yi shiru, amma ya ƙara ɗaga murya yana cewa, “Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai!”
And many were rebuking him, that he might hold his peace; but, he, so much the more, was crying aloud, O Son of David, have mercy on me.
49 Yesu ya tsaya ya ce, “Ku kira shi.” Sai suka kira makahon suka ce, “Ka yi farin ciki! Tashi tsaye! Yana kiranka.”
And, coming to a stand, Jesus said—Call him! And they call the blind man, saying unto him—Take courage! rise! he calleth thee!
50 Ya jefar da mayafinsa waje ɗaya, ya yi wuf, ya zo wurin Yesu.
And, he, throwing off his mantle—springing to his feet, came unto Jesus.
51 Yesu ya tambaye shi ya ce, “Me kake so in yi maka?” Makahon ya ce, “Rabbi, ina so in sami ganin gari.”
And, answering him, Jesus said—What desirest thou, I should do for thee? And, the blind man, said unto him—Rabboni! that may recover sight.
52 Yesu ya ce, “Je ka, bangaskiyarka ta warkar da kai.” Nan da nan, ya sami ganin gari, ya kuma bi Yesu suka tafi.
And, Jesus, said unto him—Go thy way! thy faith, hath saved thee. And, straightway, he recovered sight, and was following him in the road.

< Markus 10 >