< Markus 10 >
1 Sai Yesu ya tashi daga nan ya tafi yankin Yahudiya, da kuma ƙetaren Urdun. Taron mutane suka sāke zuwa wurinsa, ya kuma koya musu kamar yadda ya saba.
He arose from there and came into the borders of Judea and beyond the Jordan. Crowds came together to him again. As he usually did, he was again teaching them.
2 Waɗansu Farisiyawa suka zo suka gwada shi, ta wurin yin masa tambaya cewa, “Daidai ne bisa ga doka, mutum yă saki matarsa?”
Pharisees came to him testing him, and asked him, "Is it lawful for a man to divorce his wife?"
3 Ya amsa ya ce, “Me Musa ya umarce ku?”
He answered, "What did Moses command you?"
4 Suka ce, “Musa ya ba da izini mutum yă rubuta takardar saki, yă kuma kore ta.”
They said, "Moses allowed a certificate of divorce to be written, and to divorce her."
5 Yesu ya ce, “Saboda taurin kanku ne, Musa ya rubuta muku wannan doka.
But Jesus said to them, "Because of your hardness of heart, he wrote you this commandment.
6 Amma a farkon halitta, Allah ya ‘halicce su miji da mace.’
But from the beginning of the creation, he made them male and female.
7 ‘Saboda wannan dalili, mutum zai bar mahaifinsa da mahaifiyarsa, yă manne wa matarsa,
For this cause a man will leave his father and mother, and will join to his wife,
8 su biyun kuma za su zama jiki ɗaya.’Saboda haka, su ba mutum biyu ba ne, amma mutum ɗaya.
and the two will become one flesh, so that they are no longer two, but one flesh.
9 Domin haka, abin da Allah ya haɗa, kada mutum yă raba.”
What therefore God has joined together, let no one separate."
10 Da suna cikin gida kuma, sai almajiran suka tambayi Yesu game da wannan.
In the house, the disciples asked him again about the same matter.
11 Ya amsa ya ce, “Duk wanda ya saki matarsa, ya auri wata, yana da laifin aikata zina a kan matar da ya saki.
He said to them, "Whoever divorces his wife, and marries another, commits adultery against her.
12 In kuma ta saki mijinta ta auri wani, ta yi zina ke nan.”
If she herself divorces her husband, and marries another, she commits adultery."
13 Mutane suka kawo ƙananan yara wurin Yesu don yă taɓa su, amma almajiran suka kwaɓe su.
They were bringing to him little children, that he should touch them, but the disciples rebuked them.
14 Da Yesu ya ga haka, sai ya yi fushi, ya ce musu, “Ku bar yara ƙanana su zo wurina, kada ku hana su, gama mulkin Allah na irin waɗannan ne.
But when Jesus saw it, he was moved with indignation, and said to them, "Allow the little children to come to me. Do not forbid them, for the kingdom of God belongs to such as these.
15 Gaskiya nake gaya muku, duk wanda bai karɓi mulkin Allah kamar ƙaramin yaro ba, ba zai taɓa shiga mulkin ba.”
Truly I tell you, whoever will not receive the kingdom of God like a little child, he will in no way enter into it."
16 Sai ya ɗauki yaran a hannuwansa, ya ɗibiya musu hannuwansa, ya kuma albarkace su.
And he took them in his arms, laying his hands on them, and blessed them.
17 Da Yesu ya kama hanya, sai wani mutum ya ruga da gudu ya zo wajensa, ya durƙusa a gabansa ya ce, “Malam nagari, me zan yi domin in gāji rai madawwami?” (aiōnios )
As he was going out into the way, one ran to him, knelt before him, and asked him, "Good Teacher, what must I do that I may inherit everlasting life?" (aiōnios )
18 Yesu ya amsa ya ce, “Don me kake ce da ni mai nagarta? Ai, ba wani nagari, sai Allah kaɗai.
Jesus said to him, "Why do you call me good? No one is good except one—God.
19 Ka san dokokin da suka ce, ‘Kada ka yi kisankai, kada ka yi zina, kada ka yi sata, kada ka ba da shaida ta ƙarya, kada ka cuci wani, ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka.’”
You know the commandments: 'Do not commit adultery,' 'Do not murder,' 'Do not steal,' 'Do not give false testimony,' 'Do not defraud,' 'Honor your father and mother.'"
20 Mutumin ya ce, “Malam, ai, tun ina yaro na kiyaye duk waɗannan.”
And he said to him, "Teacher, I have kept all these things from my youth."
21 Yesu ya kalle shi da ƙauna ya ce, “Abu ɗaya ka rasa, ka tafi ka sayar da duk abin da kake da shi, ka ba wa matalauta, za ka kuwa sami dukiya a sama. Sa’an nan ka zo ka bi ni.”
Jesus looking at him loved him, and said to him, "One thing you lack. Go, sell whatever you have, and give to the poor, and you will have treasure in heaven; and come, follow me, taking up the cross."
22 Da jin wannan, sai mutumin ya ɓata fuskarsa, ya tafi da baƙin ciki, gama yana da arziki sosai.
But his face fell at that saying, and he went away sorrowful, for he was one who had great possessions.
23 Yesu ya dudduba, sai ya ce wa almajiransa, “Yana da wuya fa masu arziki su shiga mulkin Allah!”
Jesus looked around, and said to his disciples, "How difficult it is for those who have riches to enter into the kingdom of God."
24 Almajiransa suka yi mamakin kalmominsa. Amma Yesu ya sāke ce musu, “’Ya’yana, yana da wuya fa a shiga mulkin Allah!
The disciples were amazed at his words. But Jesus answered again and said to them, "Children, how hard it is for those who trust in riches to enter the kingdom of God.
25 Ya fi sauƙi raƙumi yă shiga ta kafar allura, da mai arziki yă shiga mulkin Allah.”
It is easier for a camel to go through a needle's eye than for a rich person to enter into the kingdom of God."
26 Almajiran suka yi mamaki ƙwarai, suka ce wa juna, “To, wa zai sami ceto ke nan?”
They were exceedingly astonished, saying to him, "Then who can be saved?"
27 Yesu ya kalle su ya ce, “Ga mutum kam, wannan ba mai yiwuwa ba ne, amma ga Allah, wannan mai yiwuwa ne; dukan abubuwa masu yiwuwa ne ga Allah.”
Jesus, looking at them, said, "With humans it is impossible, but not with God, for all things are possible with God."
28 Bitrus ya ce, “Mun bar kome domin mu bi ka!”
Peter began to tell him, "Look, we have left everything, and have followed you."
29 Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, babu wanda zai bar gida, ko’yan’uwa maza da mata, ko mahaifiya, ko mahaifi, ko’ya’ya, ko gonaki saboda ni, da kuma bishara,
Jesus said, "Truly I tell you, there is no one who has left house, or brothers, or sisters, or mother, or father, or children, or land, for my sake, and for the sake of the Good News,
30 sa’an nan yă kāsa samun ninkinsu ɗari a zamanin yanzu (na gidaje, da’yan’uwa mata, da’yan’uwa maza, da uwaye, da’ya’ya, da gonaki amma tare da tsanani) a lahira kuma yă sami rai madawwami. (aiōn , aiōnios )
but he will receive one hundred times more now in this time, houses, brothers, sisters, mothers, children, and land, with persecutions; and in the age to come, everlasting life. (aiōn , aiōnios )
31 Amma da yawa da suke na farko, za su zama na ƙarshe, na ƙarshe kuma, za su zama na farko.”
But many who are first will be last; and the last first."
32 Suna haurawa a hanyarsu zuwa Urushalima ke nan, Yesu yana a gaba, almajiran suna bin sa suna mamaki, waɗanda suke bi kuma suna ji tsoro. Ya sāke kai Sha Biyun nan gefe, ya gaya musu abin da zai faru da shi.
They were on the way, going up to Jerusalem; and Jesus was going in front of them, and they were amazed; and those who followed were afraid. He again took the twelve, and began to tell them the things that were going to happen to him.
33 Ya ce, “Za mu haura zuwa Urushalima, za a bashe Ɗan Mutum, ga manyan firistoci da malaman dokoki. Za su yi masa hukuncin kisa, a kuma ba da shi ga Al’ummai,
"Look, we are going up to Jerusalem. The Son of Man will be delivered to the chief priests and the scribes. They will condemn him to death, and will deliver him to foreigners.
34 waɗanda za su yi masa ba’a, su tofa masa miyau, su yi masa bulala, su kuma kashe shi. Bayan kwana uku kuma yă tashi.”
They will mock him, spit on him, scourge him, and kill him. After three days he will rise again."
35 Sai Yaƙub da Yohanna,’ya’yan Zebedi maza suka zo wurinsa suka ce, “Malam, muna so ka yi mana duk abin da muka roƙa.”
James and John, the sons of Zebedee, came near to him, and said to him, "Teacher, we want you to do for us whatever we will ask."
36 Ya tambaye su ya ce, “Me kuke so in yi muku?”
He said to them, "What do you want me to do for you?"
37 Suka amsa suka ce, “Ka bar ɗayanmu yă zauna a damarka, ɗayan kuma a hagunka, a cikin ɗaukakarka.”
They said to him, "Grant to us that we may sit, one at your right hand, and one at your left hand, in your glory."
38 Yesu ya ce, “Ba ku san abin da kuke roƙo ba. Za ku iya shan kwaf da zan sha, ko a yi muku baftisma da baftismar da aka yi mini?”
But Jesus said to them, "You do not know what you are asking. Are you able to drink the cup that I drink, or to be baptized with the baptism that I am baptized with?"
39 Suka ce, “Za mu iya.” Yesu ya ce musu, “Za ku sha kwaf da zan sha, a kuma yi muku baftisma da aka yi mini,
And they said to him, "We are able." And Jesus said to them, "You will drink the cup I drink, and you will be baptized with the baptism that I am baptized with;
40 amma zama a damana ko haguna, ba ni nake ba da izinin ba. Waɗannan wurare na waɗanda aka riga aka shirya musu ne.”
but to sit at my right hand and at my left hand is not mine to give, but for whom it has been prepared."
41 Da sauran goman suka ji wannan, sai suka yi fushi da Yaƙub da Yohanna.
When the ten heard it, they began to be indignant towards James and John.
42 Yesu ya kira su ya ce musu, “Kun sani waɗanda aka san su da mulkin al’ummai sukan nuna musu iko, hakimansu ma sukan gasa musu iko.
Jesus summoned them, and said to them, "You know that they who are recognized as rulers over the nations lord it over them, and their great ones exercise authority over them.
43 Ba haka ya kamata yă zama da ku ba. A maimakon, duk wanda yake so yă zama babba a cikinku, dole yă zama bawanku.
But it will not be so among you, but whoever wants to become great among you must be your servant.
44 Duk wanda kuma yake so yă zama na farko, dole yă zama bawan kowa.
And whoever wants to be first among you must be slave of all.
45 Gama ko Ɗan Mutum ma, bai zo domin a bauta masa ba, amma don yă yi bauta, yă kuma ba da ransa fansa saboda mutane da yawa.”
For the Son of Man also did not come to be served, but to serve, and to give his life as a ransom for many."
46 Sai suka iso Yeriko. Sa’ad da Yesu da almajiransa tare da taro mai yawa suke barin birnin, wani makaho da ake kira Bartimawus kuwa (wato, “ɗan Timawus”), yana zaune a gefen hanya yana bara.
They came to Jericho. As he went out from Jericho, with his disciples and a large crowd, Bartimaeus, the son of Timaeus, a blind beggar, was sitting by the road.
47 Da ya ji cewa Yesu Banazare ne, sai ya ɗaga murya, yana cewa, “Yesu Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai!”
When he heard that it was Jesus the Nazarene, he began to cry out, and say, "Jesus, Son of David, have mercy on me."
48 Mutane da yawa suka kwaɓe shi, suka ce yă yi shiru, amma ya ƙara ɗaga murya yana cewa, “Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai!”
Many rebuked him, that he should be quiet, but he shouted all the louder, "Son of David, have mercy on me."
49 Yesu ya tsaya ya ce, “Ku kira shi.” Sai suka kira makahon suka ce, “Ka yi farin ciki! Tashi tsaye! Yana kiranka.”
Jesus stood still, and said, "Call him." They called the blind man, saying to him, "Cheer up. Get up. He is calling you."
50 Ya jefar da mayafinsa waje ɗaya, ya yi wuf, ya zo wurin Yesu.
He, casting away his coat, jumped up, and came to Jesus.
51 Yesu ya tambaye shi ya ce, “Me kake so in yi maka?” Makahon ya ce, “Rabbi, ina so in sami ganin gari.”
Jesus asked him, "What do you want me to do for you?" The blind man said to him, "Rabboni, that I may see again."
52 Yesu ya ce, “Je ka, bangaskiyarka ta warkar da kai.” Nan da nan, ya sami ganin gari, ya kuma bi Yesu suka tafi.
Jesus said to him, "Go your way. Your faith has made you well." And immediately he received his sight, and followed him on the road.