< Markus 10 >

1 Sai Yesu ya tashi daga nan ya tafi yankin Yahudiya, da kuma ƙetaren Urdun. Taron mutane suka sāke zuwa wurinsa, ya kuma koya musu kamar yadda ya saba.
Ježíš opustil Kafarnaum a prošel Zajordáním do Judska. I zde ho obklopilo množství lidí a on je začal učit jako obvykle.
2 Waɗansu Farisiyawa suka zo suka gwada shi, ta wurin yin masa tambaya cewa, “Daidai ne bisa ga doka, mutum yă saki matarsa?”
Přišli však za ním farizejové a pokoušeli se ho nachytat: zeptali se ho, zda je dovolen rozvod.
3 Ya amsa ya ce, “Me Musa ya umarce ku?”
Místo odpovědi jim dal otázku: „Co řekl o rozvodu Mojžíš?“
4 Suka ce, “Musa ya ba da izini mutum yă rubuta takardar saki, yă kuma kore ta.”
„K tomu, aby manželství bylo zrušeno, podle Mojžíše stačí, když muž napíše ženě rozlukový list.“
5 Yesu ya ce, “Saboda taurin kanku ne, Musa ya rubuta muku wannan doka.
„To byl jen Mojžíšův ústupek tvrdosti lidského srdce, “řekl na to Ježíš. „Bůh si to tak nikdy nepřál.
6 Amma a farkon halitta, Allah ya ‘halicce su miji da mace.’
Hned na počátku stvořil člověka jako nerozlučnou dvojici, muže a ženu.
7 ‘Saboda wannan dalili, mutum zai bar mahaifinsa da mahaifiyarsa, yă manne wa matarsa,
Proto muž opustí své rodiče a připojí se ke své manželce;
8 su biyun kuma za su zama jiki ɗaya.’Saboda haka, su ba mutum biyu ba ne, amma mutum ɗaya.
v tom spojení již nežijí jako dva jedinci, ale stávají se jednou bytostí.
9 Domin haka, abin da Allah ya haɗa, kada mutum yă raba.”
A proto člověk nemá právo rozdělit, co Bůh spojil.“
10 Da suna cikin gida kuma, sai almajiran suka tambayi Yesu game da wannan.
Později se učedníci znovu k té otázce vrátili.
11 Ya amsa ya ce, “Duk wanda ya saki matarsa, ya auri wata, yana da laifin aikata zina a kan matar da ya saki.
Vyložil jim to: „Kdo se rozvede se svou ženou a ožení se s jinou, hřeší stejně, jako by měl ženy dvě.
12 In kuma ta saki mijinta ta auri wani, ta yi zina ke nan.”
A právě tak rozvede-li se žena se svým mužem a vdá se za jiného, dopouští se cizoložství.“
13 Mutane suka kawo ƙananan yara wurin Yesu don yă taɓa su, amma almajiran suka kwaɓe su.
Lidé nosili k Ježíšovi děti, aby jim žehnal. Učedníci jim domlouvali, aby ho neobtěžovali.
14 Da Yesu ya ga haka, sai ya yi fushi, ya ce musu, “Ku bar yara ƙanana su zo wurina, kada ku hana su, gama mulkin Allah na irin waɗannan ne.
Když to Ježíš slyšel, zlobil se: „Neodhánějte ty děti a nebraňte jim, když chtějí ke mně. I jim přece patří Boží království.
15 Gaskiya nake gaya muku, duk wanda bai karɓi mulkin Allah kamar ƙaramin yaro ba, ba zai taɓa shiga mulkin ba.”
A říkám vám, že kdo nepřijde k Bohu s dětskou prostotou, nestane se občanem toho království.“
16 Sai ya ɗauki yaran a hannuwansa, ya ɗibiya musu hannuwansa, ya kuma albarkace su.
Bral děti do náruče, hladil je a žehnal jim.
17 Da Yesu ya kama hanya, sai wani mutum ya ruga da gudu ya zo wajensa, ya durƙusa a gabansa ya ce, “Malam nagari, me zan yi domin in gāji rai madawwami?” (aiōnios g166)
Když se zase vydali na cestu, dohonil je nějaký muž a padl před Ježíšem na kolena: „Dobrý učiteli, co mám dělat, abych získal věčný život?“ (aiōnios g166)
18 Yesu ya amsa ya ce, “Don me kake ce da ni mai nagarta? Ai, ba wani nagari, sai Allah kaɗai.
„Proč mi říkáš dobrý? Vždyť dobrý je jen Bůh, “odvětil Ježíš.
19 Ka san dokokin da suka ce, ‘Kada ka yi kisankai, kada ka yi zina, kada ka yi sata, kada ka ba da shaida ta ƙarya, kada ka cuci wani, ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka.’”
„A k tvé otázce – přikázání přece znáš: nebudeš zabíjet, cizoložit, krást, lhát, podvádět, budeš si vážit svých rodičů.“
20 Mutumin ya ce, “Malam, ai, tun ina yaro na kiyaye duk waɗannan.”
„Mistře, všechno jsem dodržoval od mládí.“
21 Yesu ya kalle shi da ƙauna ya ce, “Abu ɗaya ka rasa, ka tafi ka sayar da duk abin da kake da shi, ka ba wa matalauta, za ka kuwa sami dukiya a sama. Sa’an nan ka zo ka bi ni.”
Ježíš ho objal pohledem: „A přece ti něco schází. Jdi a prodej všechno, co máš, peníze rozdej chudým a získáš tak poklad v nebi. Potom se vrať a staň se mým následovníkem.“
22 Da jin wannan, sai mutumin ya ɓata fuskarsa, ya tafi da baƙin ciki, gama yana da arziki sosai.
Když to ten člověk vyslechl, zesmutněl a odešel s těžkým srdcem. Byl totiž velmi bohatý.
23 Yesu ya dudduba, sai ya ce wa almajiransa, “Yana da wuya fa masu arziki su shiga mulkin Allah!”
Ježíš ho mlčky sledoval očima a pak se otočil k učedníkům: „Jak těžké je pro boháče vejít do Božího království!“
24 Almajiransa suka yi mamakin kalmominsa. Amma Yesu ya sāke ce musu, “’Ya’yana, yana da wuya fa a shiga mulkin Allah!
To je zarazilo. Není snad majetek důkazem Boží přízně? „Přátelé, do Božího království se těžko dostanou ti, pro které jsou peníze a majetek smyslem života.
25 Ya fi sauƙi raƙumi yă shiga ta kafar allura, da mai arziki yă shiga mulkin Allah.”
Snáze projde velbloud tou uzoučkou brankou, které říkáte jehelné ucho, než bohatý vejde do Božího království.“
26 Almajiran suka yi mamaki ƙwarai, suka ce wa juna, “To, wa zai sami ceto ke nan?”
To jim dodalo. „Má vůbec někdo naději, že se tam dostane?“říkali si mezi sebou.
27 Yesu ya kalle su ya ce, “Ga mutum kam, wannan ba mai yiwuwa ba ne, amma ga Allah, wannan mai yiwuwa ne; dukan abubuwa masu yiwuwa ne ga Allah.”
Podíval se na ně. „Člověk na to nestačí, ale Bůh je všemocný.“
28 Bitrus ya ce, “Mun bar kome domin mu bi ka!”
Tu promluvil Petr: „Ale my jsme se všeho vzdali a šli za tebou.“
29 Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, babu wanda zai bar gida, ko’yan’uwa maza da mata, ko mahaifiya, ko mahaifi, ko’ya’ya, ko gonaki saboda ni, da kuma bishara,
„Ujišťuji vás, “odpověděl Ježíš, „že každému, kdo se z lásky ke mně a pro šíření evangelia něčeho vzdá – ať už domova, života se sourozenci, rodiči, manželkou a dětmi, nebo majetku,
30 sa’an nan yă kāsa samun ninkinsu ɗari a zamanin yanzu (na gidaje, da’yan’uwa mata, da’yan’uwa maza, da uwaye, da’ya’ya, da gonaki amma tare da tsanani) a lahira kuma yă sami rai madawwami. (aiōn g165, aiōnios g166)
se to vrátí stonásobně už zde na zemi (i když neujde pronásledování) a v budoucnosti ho čeká věčný život. (aiōn g165, aiōnios g166)
31 Amma da yawa da suke na farko, za su zama na ƙarshe, na ƙarshe kuma, za su zama na farko.”
Mnozí, kteří u lidí něco znamenají, budou poslední, a těm nejpohrdanějším se tam dostane čestných míst.“
32 Suna haurawa a hanyarsu zuwa Urushalima ke nan, Yesu yana a gaba, almajiran suna bin sa suna mamaki, waɗanda suke bi kuma suna ji tsoro. Ya sāke kai Sha Biyun nan gefe, ya gaya musu abin da zai faru da shi.
Když potom byli na cestě do Jeruzaléma, Ježíš šel vpředu a ostatní se drželi za ním. Co jim Ježíš řekl, to je znepokojilo a naplnilo obavami. Zavolal k sobě svých dvanáct učedníků a znovu je připravoval na to, co ho čeká:
33 Ya ce, “Za mu haura zuwa Urushalima, za a bashe Ɗan Mutum, ga manyan firistoci da malaman dokoki. Za su yi masa hukuncin kisa, a kuma ba da shi ga Al’ummai,
„Musíme do Jeruzaléma a tam Syn člověka padne do rukou velekněží a učitelů zákona a ti ho odsoudí a vydají pohanům.
34 waɗanda za su yi masa ba’a, su tofa masa miyau, su yi masa bulala, su kuma kashe shi. Bayan kwana uku kuma yă tashi.”
Budou se mu veřejně vysmívat, plivat na něj, zbičují a zabijí ho. Ale třetí den vstane z mrtvých.“
35 Sai Yaƙub da Yohanna,’ya’yan Zebedi maza suka zo wurinsa suka ce, “Malam, muna so ka yi mana duk abin da muka roƙa.”
Přihlásili se Zebedeovi synové Jakub a Jan: „Mistře, chtěli bychom tě o něco poprosit.“
36 Ya tambaye su ya ce, “Me kuke so in yi muku?”
„Co si ode mne přejete?“vzhlédl Ježíš.
37 Suka amsa suka ce, “Ka bar ɗayanmu yă zauna a damarka, ɗayan kuma a hagunka, a cikin ɗaukakarka.”
„Až usedneš na trůn, chtěli bychom ti sedět nejblíže se všech, každý z jedné strany vedle tebe.“
38 Yesu ya ce, “Ba ku san abin da kuke roƙo ba. Za ku iya shan kwaf da zan sha, ko a yi muku baftisma da baftismar da aka yi mini?”
„Nevíte, oč prosíte. Můžete pít z kalicha hořkosti, ze kterého musím pít já, a projít křtem utrpení, který mě čeká?“
39 Suka ce, “Za mu iya.” Yesu ya ce musu, “Za ku sha kwaf da zan sha, a kuma yi muku baftisma da aka yi mini,
„Ale jistě, “přisvědčili. „Dobře, budete pít z mého kalicha a budete pokřtěni stejným křtem.
40 amma zama a damana ko haguna, ba ni nake ba da izinin ba. Waɗannan wurare na waɗanda aka riga aka shirya musu ne.”
Ale není mou věcí určovat vám pořadí v Božím království. To už je stanoveno.“
41 Da sauran goman suka ji wannan, sai suka yi fushi da Yaƙub da Yohanna.
Ostatních deset se zlobilo na Jakuba a Jana.
42 Yesu ya kira su ya ce musu, “Kun sani waɗanda aka san su da mulkin al’ummai sukan nuna musu iko, hakimansu ma sukan gasa musu iko.
Ale Ježíš je svolal dohromady a řekl jim: „Víte, že vládcové mají moc nad národy, a kdo vládne, obvykle druhé utlačuje.
43 Ba haka ya kamata yă zama da ku ba. A maimakon, duk wanda yake so yă zama babba a cikinku, dole yă zama bawanku.
Ale mezi vámi to tak být nemá. Naopak, kdo z vás chce být velký, ať všem pokorně slouží.
44 Duk wanda kuma yake so yă zama na farko, dole yă zama bawan kowa.
A kdo z vás chce být na předním místě, ať je pomocníkem všech.
45 Gama ko Ɗan Mutum ma, bai zo domin a bauta masa ba, amma don yă yi bauta, yă kuma ba da ransa fansa saboda mutane da yawa.”
Vždyť já – Syn člověka – jsem nepřišel na svět proto, aby mi ostatní sloužili, ale abych já sloužil jim a abych položil život pro záchranu mnoha lidí.“
46 Sai suka iso Yeriko. Sa’ad da Yesu da almajiransa tare da taro mai yawa suke barin birnin, wani makaho da ake kira Bartimawus kuwa (wato, “ɗan Timawus”), yana zaune a gefen hanya yana bara.
Procházeli také Jerichem, kde se k nim přidal velký zástup. U cesty seděl slepý žebrák Bartimeus – Timeův syn.
47 Da ya ji cewa Yesu Banazare ne, sai ya ɗaga murya, yana cewa, “Yesu Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai!”
Když uslyšel, že to jde Ježíš Nazaretský, křičel: „Ježíši z rodu krále Davida, slituj se nade mnou!“
48 Mutane da yawa suka kwaɓe shi, suka ce yă yi shiru, amma ya ƙara ɗaga murya yana cewa, “Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai!”
Lidé mu domlouvali, aby mlčel. Ale on volal tím hlasitěji: „Synu Davidův, slituj se nade mnou!“
49 Yesu ya tsaya ya ce, “Ku kira shi.” Sai suka kira makahon suka ce, “Ka yi farin ciki! Tashi tsaye! Yana kiranka.”
Ježíš ho uslyšel, zastavil se a přikázal, aby slepce zavolali. Vrátili se tedy k Bartimeovi se vzkazem: „Máš štěstí, Ježíš tě volá – vstaň!“
50 Ya jefar da mayafinsa waje ɗaya, ya yi wuf, ya zo wurin Yesu.
Slepec odhodil svůj starý kabát, vyskočil a klopýtal k Ježíšovi.
51 Yesu ya tambaye shi ya ce, “Me kake so in yi maka?” Makahon ya ce, “Rabbi, ina so in sami ganin gari.”
„Co pro tebe mohu udělat?“dotkl se ho Ježíš. „Mistře, chci vidět!“
52 Yesu ya ce, “Je ka, bangaskiyarka ta warkar da kai.” Nan da nan, ya sami ganin gari, ya kuma bi Yesu suka tafi.
„Staň se, tvá víra tě zachránila.“V té chvíli se slepci vrátil zrak a on se vydal také za Ježíšem.

< Markus 10 >