< Markus 10 >

1 Sai Yesu ya tashi daga nan ya tafi yankin Yahudiya, da kuma ƙetaren Urdun. Taron mutane suka sāke zuwa wurinsa, ya kuma koya musu kamar yadda ya saba.
耶穌從那裏起身,來到猶太境界,約旦河的對岸,群眾又聚集到他那裏,他又照常教訓他們。
2 Waɗansu Farisiyawa suka zo suka gwada shi, ta wurin yin masa tambaya cewa, “Daidai ne bisa ga doka, mutum yă saki matarsa?”
有些法利賽人前來問耶穌:許不許丈夫休妻﹖意思是要試探他。
3 Ya amsa ya ce, “Me Musa ya umarce ku?”
耶穌回答他們說:「梅瑟吩咐了你們什麼﹖」
4 Suka ce, “Musa ya ba da izini mutum yă rubuta takardar saki, yă kuma kore ta.”
他們說:「梅瑟准許了寫休書休妻。」
5 Yesu ya ce, “Saboda taurin kanku ne, Musa ya rubuta muku wannan doka.
耶穌對他們說:「這是為了你們的心硬,他才給你們寫下了這條法令。
6 Amma a farkon halitta, Allah ya ‘halicce su miji da mace.’
但是,從創造之初,天主造了他們一男一女。
7 ‘Saboda wannan dalili, mutum zai bar mahaifinsa da mahaifiyarsa, yă manne wa matarsa,
為此,人要離開他的父母,依附自己的妻子,
8 su biyun kuma za su zama jiki ɗaya.’Saboda haka, su ba mutum biyu ba ne, amma mutum ɗaya.
二人成為一體,以致他們不再是兩個,而是一體了。
9 Domin haka, abin da Allah ya haɗa, kada mutum yă raba.”
所以,天主所結合的人不可拆散。」
10 Da suna cikin gida kuma, sai almajiran suka tambayi Yesu game da wannan.
回到家裏,門徒又問他這事,
11 Ya amsa ya ce, “Duk wanda ya saki matarsa, ya auri wata, yana da laifin aikata zina a kan matar da ya saki.
耶穌對他們說:「誰若休自己的妻子而另娶,就是犯姦淫,辜負妻子;
12 In kuma ta saki mijinta ta auri wani, ta yi zina ke nan.”
若妻子離棄自己的丈夫而另嫁,也是犯姦淫。」
13 Mutane suka kawo ƙananan yara wurin Yesu don yă taɓa su, amma almajiran suka kwaɓe su.
有人給耶穌領來小孩子,要他撫摸他們;門徒卻斥責他們。
14 Da Yesu ya ga haka, sai ya yi fushi, ya ce musu, “Ku bar yara ƙanana su zo wurina, kada ku hana su, gama mulkin Allah na irin waɗannan ne.
耶穌見了,就生了氣,對他們說:「讓小孩子到我跟前來,不要阻止他們! 因為天主的國正屬於這樣的人。
15 Gaskiya nake gaya muku, duk wanda bai karɓi mulkin Allah kamar ƙaramin yaro ba, ba zai taɓa shiga mulkin ba.”
我實在告訴你們:誰若不像小孩子一接受天主的國,決不能進去。」
16 Sai ya ɗauki yaran a hannuwansa, ya ɗibiya musu hannuwansa, ya kuma albarkace su.
耶穌遂抱起他們來,給他們覆手,祝福了他們。
17 Da Yesu ya kama hanya, sai wani mutum ya ruga da gudu ya zo wajensa, ya durƙusa a gabansa ya ce, “Malam nagari, me zan yi domin in gāji rai madawwami?” (aiōnios g166)
正在耶穌出來行路時,跑來了一個人,跪在他面,前問他說:「善師,為承受永生,我該做什麼﹖」 (aiōnios g166)
18 Yesu ya amsa ya ce, “Don me kake ce da ni mai nagarta? Ai, ba wani nagari, sai Allah kaɗai.
耶穌對他說:「你為什麼稱我善﹖除了天主一個外,沒有誰是善的。
19 Ka san dokokin da suka ce, ‘Kada ka yi kisankai, kada ka yi zina, kada ka yi sata, kada ka ba da shaida ta ƙarya, kada ka cuci wani, ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka.’”
誡命你都知道:不可殺人,不可姦淫,不可偷盜,不可做假見證,不可欺詐,應孝敬你的父母。」
20 Mutumin ya ce, “Malam, ai, tun ina yaro na kiyaye duk waɗannan.”
他回答耶穌說:「傅! 這一切我從小就遵守了。」
21 Yesu ya kalle shi da ƙauna ya ce, “Abu ɗaya ka rasa, ka tafi ka sayar da duk abin da kake da shi, ka ba wa matalauta, za ka kuwa sami dukiya a sama. Sa’an nan ka zo ka bi ni.”
耶穌定睛看他,就喜愛他,對他說:「你還缺少一樣:你去,變賣你所有的一切,施捨給窮人,你必有寶藏在天上;然後來,背著十字架,跟隨我!」
22 Da jin wannan, sai mutumin ya ɓata fuskarsa, ya tafi da baƙin ciki, gama yana da arziki sosai.
因了這話,那人就面帶愁容,憂鬱地走了,因為他有許多產業。
23 Yesu ya dudduba, sai ya ce wa almajiransa, “Yana da wuya fa masu arziki su shiga mulkin Allah!”
耶穌周圍一看,就對自己的門徒說:「那些有錢的人,進天主的國是多麼難啊!」
24 Almajiransa suka yi mamakin kalmominsa. Amma Yesu ya sāke ce musu, “’Ya’yana, yana da wuya fa a shiga mulkin Allah!
門徒就都驚奇他這句話。耶穌又對他們說:「孩子們! 仗恃錢財的人,進天主的國是多麼難啊!
25 Ya fi sauƙi raƙumi yă shiga ta kafar allura, da mai arziki yă shiga mulkin Allah.”
駱駝穿過針孔, 比富有的人進天主的國還容易。」
26 Almajiran suka yi mamaki ƙwarai, suka ce wa juna, “To, wa zai sami ceto ke nan?”
他們就更加驚奇,彼此說:「這樣,誰還能得救﹖」
27 Yesu ya kalle su ya ce, “Ga mutum kam, wannan ba mai yiwuwa ba ne, amma ga Allah, wannan mai yiwuwa ne; dukan abubuwa masu yiwuwa ne ga Allah.”
耶穌注視他們說:「在人不可能,在天主卻不然,因為在天主,一切都是可能的。」
28 Bitrus ya ce, “Mun bar kome domin mu bi ka!”
伯多祿開口對他說:「看,我們捨棄了一切,而跟隨了你。」
29 Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, babu wanda zai bar gida, ko’yan’uwa maza da mata, ko mahaifiya, ko mahaifi, ko’ya’ya, ko gonaki saboda ni, da kuma bishara,
耶穌回答說:「我實在告訴你們:人為了我,為了福音,而捨棄了房屋、或兄弟、或姊妹、或母親、或父親、或兒女、或田地,
30 sa’an nan yă kāsa samun ninkinsu ɗari a zamanin yanzu (na gidaje, da’yan’uwa mata, da’yan’uwa maza, da uwaye, da’ya’ya, da gonaki amma tare da tsanani) a lahira kuma yă sami rai madawwami. (aiōn g165, aiōnios g166)
沒有不在今時就百倍的房屋、兄弟、姊妹、母親、兒女、田地──連迫害也在內,並在來世獲得永生的。 (aiōn g165, aiōnios g166)
31 Amma da yawa da suke na farko, za su zama na ƙarshe, na ƙarshe kuma, za su zama na farko.”
但有許多在先的,要成為在後的;在後的,要成為在先的。」
32 Suna haurawa a hanyarsu zuwa Urushalima ke nan, Yesu yana a gaba, almajiran suna bin sa suna mamaki, waɗanda suke bi kuma suna ji tsoro. Ya sāke kai Sha Biyun nan gefe, ya gaya musu abin da zai faru da shi.
那時,他們在路上,要上耶路撒冷去,耶穌在門徒前頭走,他們都驚奇,跟隨的人也都害。耶穌又把那十二人帶到一邊,開始告訴他們那將要臨到他身上的事:「
33 Ya ce, “Za mu haura zuwa Urushalima, za a bashe Ɗan Mutum, ga manyan firistoci da malaman dokoki. Za su yi masa hukuncin kisa, a kuma ba da shi ga Al’ummai,
看,我們上耶路撒冷去,人子要被交於司祭長和經師;他們要定他的死罪,把他交給外邦人;
34 waɗanda za su yi masa ba’a, su tofa masa miyau, su yi masa bulala, su kuma kashe shi. Bayan kwana uku kuma yă tashi.”
這些人要戲弄他,唾污他,鞭打,他殺害他;但三天以後,他必要復活。」
35 Sai Yaƙub da Yohanna,’ya’yan Zebedi maza suka zo wurinsa suka ce, “Malam, muna so ka yi mana duk abin da muka roƙa.”
載伯德的兒子雅各伯和若望走到耶穌跟前,對他說:「師傅! 我們願你允許我們的要求!」
36 Ya tambaye su ya ce, “Me kuke so in yi muku?”
耶穌對他們說:「你們願意我給你們做什麼﹖」
37 Suka amsa suka ce, “Ka bar ɗayanmu yă zauna a damarka, ɗayan kuma a hagunka, a cikin ɗaukakarka.”
他們回答說:「賜我們在你的光榮中,一個坐在你右邊, 一個坐在你左邊。」
38 Yesu ya ce, “Ba ku san abin da kuke roƙo ba. Za ku iya shan kwaf da zan sha, ko a yi muku baftisma da baftismar da aka yi mini?”
耶穌對他們說:「你們知不知道你們所求的是什麼;你們能飲我的爵嗎﹖或者,你們能受我受的的洗嗎﹖」
39 Suka ce, “Za mu iya.” Yesu ya ce musu, “Za ku sha kwaf da zan sha, a kuma yi muku baftisma da aka yi mini,
他們對他說:「我們能。」耶穌就對他們說:「我飲的爵,你們必要飲;我受的洗你們必要受;
40 amma zama a damana ko haguna, ba ni nake ba da izinin ba. Waɗannan wurare na waɗanda aka riga aka shirya musu ne.”
但坐在我右邊或左邊,不是我可以給的,而是給誰預備了,就給誰。」
41 Da sauran goman suka ji wannan, sai suka yi fushi da Yaƙub da Yohanna.
那十個聽了,就開始惱怒雅各伯和若望。
42 Yesu ya kira su ya ce musu, “Kun sani waɗanda aka san su da mulkin al’ummai sukan nuna musu iko, hakimansu ma sukan gasa musu iko.
耶穌叫門徒過來,對他們說:「你們知道:在外邦人中,有尊為首領的,主宰他們,有大臣管轄他們;
43 Ba haka ya kamata yă zama da ku ba. A maimakon, duk wanda yake so yă zama babba a cikinku, dole yă zama bawanku.
但你們中間卻不可這樣:誰若願意在你們中間成為大的,就當作你們的僕役;
44 Duk wanda kuma yake so yă zama na farko, dole yă zama bawan kowa.
誰若願意在你們中間為首,就當作眾人的奴僕;
45 Gama ko Ɗan Mutum ma, bai zo domin a bauta masa ba, amma don yă yi bauta, yă kuma ba da ransa fansa saboda mutane da yawa.”
因為人子,不是來受服事,而是來服事人,並交出自己的性命,為大眾作贖價。」
46 Sai suka iso Yeriko. Sa’ad da Yesu da almajiransa tare da taro mai yawa suke barin birnin, wani makaho da ake kira Bartimawus kuwa (wato, “ɗan Timawus”), yana zaune a gefen hanya yana bara.
他們來到耶里哥。耶穌和他的門徒及一大群人,從耶里哥出來的時候,有一個瞎眼的乞丐,即提買的兒子巴爾提買坐在路旁。
47 Da ya ji cewa Yesu Banazare ne, sai ya ɗaga murya, yana cewa, “Yesu Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai!”
他一聽說是納匝肋人耶穌,就喊叫說:「耶穌,達味之子,可憐我罷!」
48 Mutane da yawa suka kwaɓe shi, suka ce yă yi shiru, amma ya ƙara ɗaga murya yana cewa, “Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai!”
有許多人就斥責他,叫他要作聲;但他越發喊叫說:「達味之子,可憐我罷!」
49 Yesu ya tsaya ya ce, “Ku kira shi.” Sai suka kira makahon suka ce, “Ka yi farin ciki! Tashi tsaye! Yana kiranka.”
耶穌就站住說:「叫他過來!」人就叫那瞎子,給他說:「放心! 起來! 他叫你呢!」
50 Ya jefar da mayafinsa waje ɗaya, ya yi wuf, ya zo wurin Yesu.
瞎子就扔下自己的外衣,跳起來,走到耶穌跟前。
51 Yesu ya tambaye shi ya ce, “Me kake so in yi maka?” Makahon ya ce, “Rabbi, ina so in sami ganin gari.”
耶穌對他說:「你願意我給你做什麼﹖」瞎子說:「師傅! 叫我看見!」
52 Yesu ya ce, “Je ka, bangaskiyarka ta warkar da kai.” Nan da nan, ya sami ganin gari, ya kuma bi Yesu suka tafi.
耶穌對他說:「去罷! 你的信德救了你。」瞎子立刻看了,就在路上跟著耶穌去了。

< Markus 10 >