< Markus 1 >
1 Farkon bishara game da Yesu Kiristi, Ɗan Allah.
Ukuqala kwevangeli likaJesu Kristu, iNdodana kaNkulunkulu;
2 An rubuta a cikin littafin annabi Ishaya cewa, “Zan aika da ɗan aikena yă sha gabanka, wanda zai shirya hanyarka,”
njengokulotshiweyo kubaprofethiukuthi: Khangela, mina ngiyathuma isithunywa sami phambi kobuso bakho, esizalungisa indlela yakho phambi kwakho.
3 “muryar mai kira a hamada tana cewa, ‘Ku shirya wa Ubangiji hanya, ku miƙe hanyoyi dominsa.’”
Ilizwi lomemezayo enkangala, lithi: Lungisani indlela yeNkosi; qondisani izindledlana zayo.
4 Ta haka Yohanna ya zo, yana baftisma a yankin hamada, yana kuma wa’azin baftismar tuba don gafarar zunubai.
Kweza uJohane ebhabhathiza enkangala, etshumayela ubhabhathizo lokuphenduka kukho ukuthethelelwa kwezono,
5 Dukan ƙauyukan Yahudiya da dukan mutanen Urushalima suka fiffito zuwa wurinsa. Suna furta zunubansu, ya kuwa yi musu baftisma a Kogin Urdun.
njalo kwaphumela kuye ilizwe lonke leJudiya, labo abeJerusalema, basebebhabhathizwa bonke nguye emfuleni iJordani, bevuma izono zabo.
6 Yohanna ya sa tufafin gashin raƙumi, ya kuma yi ɗamara da fata. Abincinsa fāri ne da kuma zumar jeji.
Futhi uJohane wayembethe uboya bekamela, elozwezwe lwesikhumba ekhalweni lwakhe, wayesidla intethe loluju lweganga.
7 Wannan kuwa shi ne saƙonsa, “A bayana, wanda ya fi ni iko yana zuwa, ban kuwa isa in sunkuya in kunce igiyar takalmansa ba.
Watshumayela, esithi: Olamandla kulami uyeza emva kwami, engingafanele ukukhothama ngithukulule umchilo wamanyathela akhe.
8 Ina muku baftisma da ruwa, amma shi zai yi muku baftisma da Ruhu Mai Tsarki.”
Mina isibili ngilibhabhathize ngamanzi; kodwa yena uzalibhabhathiza ngoMoya oNgcwele.
9 A lokacin, Yesu ya zo daga Nazaret na Galili, Yohanna kuwa ya yi masa baftisma a Urdun.
Kwasekusithi ngalezonsuku kwafika uJesu evela eNazaretha yeGalili, wabhabhathizwa nguJohane eJordani.
10 Da Yesu yana fitowa daga ruwan, sai ya ga sama ya buɗe, Ruhu kuma yana saukowa a kansa kamar kurciya.
Wenela ukukhuphuka emanzini, wabona amazulu eqhekezeka, loMoya kungathi lijuba esehlela phezu kwakhe;
11 Sai murya ta fito daga sama ta ce, “Kai ne Ɗana, wanda nake ƙauna, da kai kuma nake fari ciki ƙwarai.”
kwasekusiza ilizwi livela emazulwini, lathi: Wena uyiNdodana yami ethandekayo, engithokoza ngayo.
12 Nan da nan, sai Ruhu ya kai shi cikin hamada,
Njalo uMoya wahle wamqhubela enkangala.
13 ya kuma kasance a hamada kwana arba’in, Shaiɗan yana gwada shi. Yana tare da namomin jeji, mala’iku kuma suka yi masa hidima.
Wayekhona-ke lapho enkangala insuku ezingamatshumi amane elingwa nguSathane, wayelezilo, ingilosi zasezimnceda.
14 Bayan da aka sa Yohanna a kurkuku, sai Yesu ya shigo cikin Galili, yana shelar bisharar Allah.
Kwathi emva kokunikelwa kukaJohane, uJesu wafika eGalili, etshumayela ivangeli lombuso kaNkulunkulu,
15 Yana cewa, “Lokaci ya yi. Mulkin Allah ya yi kusa. Ku tuba, ku gaskata bishara!”
njalo esithi: Isikhathi sigcwalisekile, njalo umbuso kaNkulunkulu ususondele; phendukani, likholwe ivangeli.
16 Yayinda Yesu yake tafiya a gaɓar Tekun Galili, sai ya ga Siman da ɗan’uwansa Andarawus, suna jefa abin kamun kifi a cikin tafkin, domin su masunta ne.
Kwathi ehambahamba elwandle lweGalili wabona uSimoni loAndreya umfowabo, bephosela imbule olwandle; ngoba babengabagoli benhlanzi.
17 Yesu ya ce, “Ku zo, ku bi ni, ni kuwa zan mai da ku masuntan mutane.”
UJesu wasesithi kubo: Ngilandelani, ngizalenza libe ngabagoli babantu.
18 Nan da nan, suka bar abin kamun kifinsu, suka bi shi.
Njalo bahle batshiya amambule abo, bamlandela.
19 Da ya yi gaba kaɗan, sai ya ga Yaƙub ɗan Zebedi, da ɗan’uwansa Yohanna a cikin jirgin ruwa, suna gyaran abin kamun kifinsu.
Eseqhubeke ibangana esuka lapho, wabona uJakobe okaZebediya, loJohane umfowabo, labo babesemkhunjini belungisa amambule abo.
20 Ba da ɓata lokaci ba, ya kira su, sai suka bar mahaifinsu Zebedi a cikin jirgin ruwan, tare da’yan haya, suka kuwa bi shi.
Njalo wahle wababiza; basebetshiya uyise uZebediya emkhunjini leziqhatshwa, basuka bamlandela.
21 Suka tafi Kafarnahum. Da ranar Asabbaci ta kewayo, sai Yesu ya shiga majami’a ya fara koyarwa.
Basebengena eKapenawume; kwathi ngesabatha wahle wangena esinagogeni, wafundisa.
22 Mutane suka yi mamakin koyarwarsa, domin ya koyar da su kamar wanda yake da iko, ba kamar malaman dokoki ba.
Basebebabaza ngemfundiso yakhe; ngoba wabafundisa njengolamandla, njalo kungenjengababhali.
23 Nan take, sai wani mutum mai mugun ruhu a majami’arsu, ya ɗaga murya ya ce,
Futhi kwakukhona esinagogeni labo umuntu owayelomoya ongcolileyo, wasememeza,
24 “Ina ruwanka da mu, Yesu Banazare? Ka zo ne don ka hallaka mu? Na san wane ne kai, Mai Tsarki nan na Allah!”
wathi: Yekela, silani lawe, Jesu weNazaretha? Uze ukusibhubhisa yini? Ngiyakwazi wena ukuthi ungubani: ONgcwele kaNkulunkulu.
25 Yesu ya tsawata masa ya ce, “Yi shiru! Fita daga cikinsa!”
UJesu wasemkhuza, wathi: Thula, uphume kuye.
26 Sai mugun ruhun ya jijjiga mutumin da ƙarfi, ya fita daga jikinsa da ihu.
Futhi umoya ongcolileyo emhlukuluza ekhala ngelizwi elikhulu, waphuma kuye.
27 Dukan mutane suka yi mamaki, suna tambayar juna suna cewa, “Mene ne haka? Tabɗi! Yau ga sabuwar koyarwa kuma da iko! Yana ma ba wa mugayen ruhohi umarni, suna kuma yin masa biyayya.”
Basebemangala bonke, baze babuzana, bathi: Kuyini lokhu? Yimfundiso bani entsha le, ukuthi ngamandla uyalaya labomoya abangcolileyo, futhi bamlalele.
28 Labari game da shi ya bazu nan da nan ko’ina a dukan yankin Galili.
Njalo yahle yaphuma indumela yakhe esigabeni sonke seGalili esizingelezeleyo.
29 Da suka bar majami’ar, sai suka tafi gidan su Siman da Andarawus, tare da Yaƙub da Yohanna.
Njalo bahle baphuma esinagogeni, bangena endlini kaSimoni loAndreya, kanye loJakobe loJohane.
30 Surukar Siman tana kwance da zazzaɓi, sai suka gaya wa Yesu game da ita.
Futhi uninazala kaSimoni wayelele eloqhuqho, njalo bahle bamtshela ngaye;
31 Sai ya je wajenta, ya kama hannunta, ya ɗaga ta. Zazzaɓin kuwa ya sāke ta, ta kuma yi musu hidima.
wasesondela, wabamba isandla sakhe wamvusa; futhi uqhuqho lwahle lwamyekela, wabasebenzela.
32 A wannan yamma, bayan fāɗuwar rana, mutane suka kawo wa Yesu dukan marasa lafiya, da masu aljanu.
Kwathi sekuhlwile, ilanga selitshona, baletha kuye bonke abagulayo lababengenwe ngamadimoni;
33 Duk garin ya taru a ƙofar gidan.
njalo umuzi wonke wawubuthene emnyango.
34 Yesu kuwa ya warkar da marasa lafiya da yawa da suke da cututtuka iri-iri. Ya kuma fitar da aljanu da yawa, amma bai yarda aljanun suka yi magana ba, don sun san wane ne shi.
Wasesilisa abanengi ababegula izifo ezitshiyeneyo, wakhupha amadimoni amanengi, kodwa kavumelanga amadimoni ukuthi akhulume, ngoba ayemazi.
35 Da sassafe, tun da sauran duhu, Yesu ya tashi, ya bar gida, ya tafi wani wurin da ba kowa, a can ya yi addu’a.
Njalo ekuseni kusesemnyama kakhulu wavuka waphuma, waya endaweni eyinkangala, wakhuleka khona.
36 Siman da abokansa suka fita nemansa.
USimoni lababelaye basebemdingisisa;
37 Da suka same shi, sai suka ce, “Kowa yana nemanka!”
sebemtholile bathi kuye: Bonke bayakudinga.
38 Yesu ya amsa ya ce, “Mu je wani wuri dabam, zuwa ƙauyukan da suke kusa, don in yi wa’azi a can ma. Wannan shi ne dalilin zuwana.”
Wasesithi kubo: Asiye emizini eseduze, ukuze ngitshumayele lakhona; ngoba ngiphumele lokhu.
39 Sai ya tafi ko’ina a Galili, yana wa’azi a majami’unsu, yana kuma fitar da aljanu.
Wasetshumayela emasinagogeni abo kulo lonke eleGalili, ekhupha amadimoni.
40 Wani mutum mai kuturta ya zo wurinsa, ya durƙusa ya roƙe shi ya ce, “In kana so, za ka iya tsabtacce ni.”
Kwasekufika kuye umlephero, emncenga eguqa ngamadolo phambi kwakhe, esithi kuye: Aluba uthanda, ungangihlambulula.
41 Cike da tausayi, sai Yesu ya miƙa hannunsa ya taɓa mutumin ya ce, “Na yarda, ka tsabtacce!”
UJesu wasesiba lesihelo, welula isandla, wamthinta, wathi kuye: Ngiyathanda, hlambuluka;
42 Nan da nan, sai kuturtar ta rabu da shi, ya kuma warke.
esekhulumile bahle basuka ubulephero kuye, wahlanjululwa.
43 Yesu ya sallame shi nan take, da gargaɗi mai ƙarfi cewa,
Wasemlayisisa, wahle wamyekela wahamba,
44 “Ka lura kada ka gaya wa kowa wannan. Amma ka tafi ka nuna kanka ga firist, ka kuma miƙa hadayun da Musa ya umarta saboda tsarkakewarka, don yă zama shaida gare su.”
esithi kuye: Khangela ungatsheli muntu ulutho; kodwa hamba, uziveze kumpristi, unikele ngokuhlanjululwa kwakho lokho uMozisi akulayayo, kube yibufakazi kubo.
45 A maimakon haka, sai ya fita, ya fara magana a sake, yana baza labarin. Saboda haka, Yesu bai ƙara iya shiga cikin gari a fili ba, sai dai ya kasance a wuraren da ba kowa. Duk da haka, mutane suka yi ta zuwa wurinsa daga ko’ina.
Kodwa yena esephumile waqala ukumemezela kakhulu walwandisa udaba, kwaze kwathi wayengaselakho ukungena emzini obala, kodwa wayengaphandle ezindaweni ezizinkangala; beza kuye bevela enhlangothini zonke.